Showing 1 words to 3000 words out of 34150 words

Chapter 1 - KYAUTAR ZUCIYA Book Complete By Bilkisu H. Muhd.txt

14 Jan 2025

1986

*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*



*NA*




*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_










*Free page 1*








*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*




*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*


*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*




_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*


```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```




*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*




*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*






ABUJA






*T* sarin unguwar tamkar a Turai, unguwa ce wadda ƙaramin mai kuɗi ba zai taɓa iya mallakar muhalli a cikinta ba, shahararrun masu kuɗi waɗanda su ka ci su ka tada kai irin manyan ‘yan siyasa, ƙusoshin gwamnati, ministoci, ‘yan majalissu, sanatoci. Su ne su ka yi sansani a cikin wannan unguwar. Cikin unguwar da kewayenta ba za ka taɓa ganin ƙasa ba, ƙamshin unguwar kaɗai ma ya fita daban. Manyan gidaje masu ɗauke da wasu irin manyan get, su suka fi yawa a nan. Kai kan ka kana dosar unguwar za ka san ka zo unguwar masu gidan rana, ta yadda tun daga nesa za ka hangi sojoji suna ta faman safa da marwa ɗauke da bindigoginsu, kamar masu shirin fita yaƙi. Ko kaɗan babu mabuƙaci a cikin wannan unguwa, za ka gane hakan ne ta yadda za ka dinga ganin kaji a abin shara waɗanda su ka yi funfuna. Shiru-shirun unguwar ya fi komai daɗaɗa wa ‘yan cikinta. Idan kai kaɗai ne a gidanka sai ka mutu har ka ruɓe babu wanda zai sani.
Akasari ‘yan cikin unguwar kansu kawai suka sani, babu wanda ya damu da shiga harkar wani. Ba kowane maƙoci ne ya taɓa ganin maƙocinsa ba, saboda kowanne gida garƙame ya ke da get, tsakanin get ɗin ma zuwa gidan sai an yi tafiya mai nisa, wanda ko da yanka ka za a yi in maƙogoronka zai tsago saboda ihu, babu wanda zai ji ka. Akasarinsu ba su san me ake nufi da talauci ba, ba su san me ake nufi da sanyi ko zafi ba. Kullum suna cikin A.C, ba a taɓa ɗauke wuta wuta a wannn unguwar, duk da suna amfani da sola, shirun unguwar tamkar ba a duniya ba, in ka ji hayaniya sai ta motoci.


Wannan kenan.


Yana zaune a babban sitroom idanunsa a kan akwatun talabijin, yadda ya ga talakawa na kukan farin ciki, tare da sanya masa albarka ya dinga jin tsigar jikinsa na tashi. Burinsa kullum ya ga ya sanya talakawa farin ciki, hakan ne kaɗai ke sanya shi nishaɗi. Daga can bayansa Hajiya Khadija ce wadda ya ke kira da Ummi, motsinta ya jiyo ya yi saurin miƙewa ya ƙarasa gare ta. Zai yi magana ta riga shi.
“Ka kalli yadda talakawa ke farin ciki, zuciyarsu fari ƙal! Deedat ɗina, kai ma Allah ya faranta maka”.
Ya riƙo hannunta.
“Ummina, duk ke ce. Komai na zama ke ce sila, ke ce ki ka ɗora ni a wannan turba. Na gode miki ƙwarai da gaske Ummina”.
Ya kwantar da kai a kafaɗarta. Ta shafa gashin kansa.
“Allah ya yi maka albarka”.
Komawa su ka yi suka zauna, tare da sake mai da hankali a kan akwatun talabijin. Daidai lokacin da wasu matasa ke roƙon ya fito ya tsaya takarar kujerar gwamna. Ummi ta dube shi, “Ko bayan raina ban amince ka tsaya takarar siyasa ba, ban ƙi ka yi ja-gaba gurin cicciɓa na gari ba har ya kai ga gaci kamar yadda ka ke yi, amma siyasa? Sam ban lamunta ba”.
Yana murmushi, “Ki kwantar da hankalinki, ɗanki ba shi da wannan ra’ayin, burina da man a kada wannan gwamnan, kuma na ji daɗi da ya faɗi tun a primary election, na san gaba ma ba zai taɓa cin nasara ba”.
Ummi ta dinga kallonsa cike da wani irin tausayinsa.
“Ummina, kina tuna baya ko? Ka da ki damu, da izinin Allah sai mun ga bayan wannan gwamnan”.
Ta dinga kaɗa kai.
“Ka bi a hankali, ka dinga sassautawa…”
Kuka ne ke ƙoƙarin ƙwace mata, da sauri ta bar gurin.


*** *** ***
Gaba ɗaya ‘yan jam’iyyar hankalinsu a tashe ya ke, cikin kakkausar murya Injiniya Usain ya ke magana.
“Ba mu san me ye dangantakanka da shi ba, mun sani ka sanshi, kai ne kaɗan ka san ta in da za mu gane waye shi, amma ka qi ba mu haske, yaro qarami yana faman shigar mana hanci da qudundune. Ka gaya mana sa, ko mu ɓatar da shege”.
Dr. Munir ya furzar da huci mai zafi, wani irin miki ne ke taso masa.
“Na kasa tantance shi ɗin waye kun fi kowa sanin in da ya ke yadda bami, shu’umi ne shi tamkar aljani”.
Ya sauke ajiyar zuciya, “Mu dai mu tsananta bincike”.
Ahmad Deedat kwance a kan wani faffaɗan gado lulluɓe da wani lallausar bargo ruwan damusa. Idanunsa a lumshe shi ba bacci ba, ba kuma ido biyu ba, muryar Sudais cikin rairo Suratul Mulk ne ke tashi a hankali. Ya so ma jin rurin wayarsa. Muskutawa ya yi cikin gyara kwanciyarsa ba shi da alamar kai wa wayar agaji har ta katse. Ba a ɗauki wani lokaci ba ta sake ɗaukar ruri. Ya ja tsaki ya miƙe zaune, ya dubi windo yana kallon in da sojoji ke faman shawagi. Ya ja tsaki, “Idan mutuwa ta zo ba za ku hana ta ɗauke ni ba”. ya ce a ransa.
Ya miƙa hannu zai ɗauki wayar, ta sake katsewa. Ya maida kai ga kallon agogon da ke manne a jikin bango. aƙarfe shida na safe.
“AAZEEN!” ya faɗa a ransa.
Da sauri ya sake ɗaukar wayar ya shiga jujjuya ta a hannunsa.
“Yau akwai rigima kenan”. Ya sake ayyanawa a ransa. Ya yi murmushi, daidai lokacin ya sake jin rurin wayar, ya yi saurin amsawa tare da karawa a kunne.
“Me ya sa ba za ka ɗaga min waya ba”. ɗasasshiyar muryarta ta ratsa kunnensa, muryar da ya fi ƙauna fiye da kowacce murya, muryar da ta fi kowacce murya burge shi. Haka kawai sau tari ya ke kewar muryar, bai san dalili ba idan bai ji muryar ba ya kan ji tamkar ya yi missing ɗin wani abu mai muhimmanci.
Ta ci gaba da faɗa, “Jiya na kira ba ka yi picking ba, yau ma ba ka da niyya”. Ta wani taƙƙaƙare.
Shi kuma sai murmushi ya ke yi, acting ɗinta na burge shi.
“Au ina ta magana ka ƙyale ni ko?”
Ya ƙunshe dariya a ciki.
“Ki yi haƙuri ƙanwata, ba zan sake ba”.
Duk da bai san wace ce ita ba, amma ya gama karantar halayyarta, akwai ƙuruciya a tare da ita, haka ne ya sanya ya ke biye mata.
“Au? Ka ci gaba da shirun ko?”
“Kin ga ai na ga bai kamata ina katse ki a magana ba…”
“To gaya min”.
“Ba ni da lafiya ne shi ne na sha maganin bacci, wannan shi ne dalilin da ya hana in ji kiran wayar taki”.
Tausayinsa ta ji sosai har zuciyarta.
“Oh! I’m sorry, me ya sa ba ka sanar da ni ba?”
Ya fahimci akwai alamun ruɗewa a cikin maganarta.
“Ta ya ya zan sanar da ke? Kin mance dokar da ki ka saka min na cewar kada na kira, kuma da tuni sai dai ki ji na mutu, kin ga da a ce ma ina kiranki da yanzu na sanar da ke”.
“Sannu, yanzu me ke yi maka ciwo?”
Ya ce, “Ciki da zazzaɓi”.
Ta zaro ido kamar yana a gabanta.
“Tab! An fa ce ba a son namiji ya yi ciwon ciki”.
“Ai na ji sauƙi, na je kyamis…”
Ta katse shi a zabure, “Kana son mutuwa ne? Kada ka sake zuwa kyamis, asibiti za ka je a duba ka. Shi kyamis zuwa ake sayen magani, ko karɓar taimakon gaggawa. Yanzu ka shirya ka je ka ji. Bara na turo maka kuɗi, sai ka je…”
Zai yi magana ya ji ta katse wayar.
Yana zaune a dinning room yana kallon inda Ummi da masu aikinta Dije da Dela suna ta sintiri daga kicin zuwa dinning room. In ka ga yadda ta yi kwalliya sai ka rantse wani gagarumin bikin ko taro za ta je, komai nata abin burgewa, ba ta yadda wani ya yi ma Deedat girki da duk abin da zai kai bakinsa, ba ta da yarda a kan Deedat. Ba ta lamunce kowa ya shige masa in ya wuce Salim da Sulaiman. Ita ke tsara masa komai tun yana yaro burinta ya zamo mutumin da za ta yi alfahari da shi, duk wani mai ƴyamarsa ya yi alfahari da shi ta koya masa dabaru, da duk wani salo, ga shi yanzu ya girma, Allah ya amsa mata dukkan addu’o’inta, ko yanzu ta koma ga Ubangiji ba za ta yi baƙin ciki ba. Abin da kawai ya rage mata shi ne, ya yi aure ta ga jikanta.
Ummi ce ke wannan tunanin a taƙaice, kawai Deedat ya zuba mata ido, da alama ta yi nisa. Ya shafi gefen fuskarta. Ta yi firgigi tare da sauke ajiyar zuciya.
“Ummina, me ke damunki ne?”
Ta taɓe baki haɗe da ɗaga kafaɗa.
“Me ko zai dame ni bayan ga ni ga ka?”
Ya yi murmushi, ya ɗan kurɓi shayi.
Da sauri ya ajiye kofin saboda zafinsa.
“Oh God! Sannu”.
“Shi ke nan Ummi… da ma ina son zan je gurin Kabir, kuma…”
“Ya isa, ban amince ba”.
“Don Allah Ummi ki bar ni, babu abin da zai same ni”.
“Idan ka je ba da yawuna ba, in kuma ka ƙi ji ga hanya”.
Ya lura da yadda ranta ya ɓaci. Ya miƙe ya ƙarasa gabanta, ya dire a kan gwiwoyinsa.
“Afuwan, ba zan sake ɗaga maganar ba”.
Ta ɗan saki fuska, ta sa hannunta biyu ta tallafi haɓarsa.
“Ka tabbata?”
Ya jinjina kai.
“That’s good! Na mance ban gaya maka ba, jibi Nabila za su dawo, Hajiya


*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*



*NA*




*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_










*Free page 2 3 4*








*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*




*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*


*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*




_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*


```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```




*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*




*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*


*B* an taba ganin mutum irinsa ba, ina da tambayoyin da zan yi masa bila adadin, ban san me ye ribarsa na tuna in boye kansa ba”.
“Rangida na fi tunanin asalinsa talaka ne, kai ni gani nake ma kamar babu shi, kawai ana son yawo da hankalin mutane”.
“No Dad, na ji a majiya mai qarfi akwai shi, duba ka ga yadda yake sakar wa Malaman addini miliyoyin kudi duk wata, sauka ko musabaqar alqur’ani da za a yi sai ya kashe miliyoyi. Na fi tunanin qila aljani ne. In ba aljani ba, waye zai yi abin da yake yi? Duk wani mai kudii yana so idan ya yi abin bajinta a san ya yi. Yana son duk inda ya sanya qafarsa ana girmama shi”.
“Dad su ma wadan da suke program din nan ba su sanshi ba kenan?” Nurat ta tambaya.
“Haka na ji ana cewa”.
Aazeen ta ce, “To me ye amfanin abin da suke yi?”
“Saboda suna son ya san taimakon da yake yi, saqo na isa gare su”.
“Mtsew! Ji wani shashanci”.
Alhaji Usman ya ci gaba da fadin, “Wannan da zai fito ya zama dan siyasa ba zai wani sha wuya ba, don abin ma da yake yi zai zamo kamar kamfen ne”.
“Dad bana ji an ce ba shi da aure ba, kuma mara aure ba ya tsayawa takarar neman gwamna?”
“Wannan ai mai sauqi ne, daga ya amice cikin lokaci qanqani zai iya yin aurensa”.
“Dad idan na kwanta ina mafarkin ya zama mijina. Dad ina ma zan ganshi ko da sau daya ne?”
“To Dad ta yaya taimakonsa ke isa hannun mutane?” Nurat ta sake tambaya.
“Ya kan kintaci duk lokacin da yake da buqata ya je inda yake buqata, bayan kiran assalatu yake isar da zakkarsa ko sadaka, sai dai ka ji an dan qwanqwasa maka qofa. Kana budewa za ka ci karo da abin da yake rabonka, duk nacinka ba za ka ga kowa ba. Da yawa an sha yin dako sai kun gama hada target da inda za ku ganshi, sai kawai ya sauya yanayin lokutan rabon babu zato babu tsammani ka ke ganin kayan arziqi, kama buhun shinkafa, taliya, kudi, sutura da sauransu. Ba qananan kudi yake badawa ba, kudi ne wanda zai ishe ka ka ja jari, wanda in ka yi dace ka yi sallama da talauci. Dadin dadawa yana da asibitoci, makarantu wadanda an gina su ne kawai saboda talakawa”.
“Tab! Ka ce shi kawai don taimako aka halicce shi?” Aazeen ta fada.
“kila ma na sanshi”.
Alhaji Usman ya yi dariya, “Babu mamaki don an ce yana nan yana mu’amala da mutane ba tare da sun sanshi din ba ne”.
“Gaskiya wannan batan basira ne, shi ke nan ya dauki kansa kamar kowa, ba ya son idan ya shiga guri a dinga nuna shi ana b shi girma? Shi sam bai damu da ya yi suna ba Dad? Wadannan abubuwan fa su ne jin dadin, kamar ni in na shiga guri za ka ga yadda ake girmama ni, ina taka duk wanda na so”.
“Yaya Aazeen wannan riya kenan fa, kuma duk mutumin da yake riya ladansa iya nan kawai za ta tsaya. Sai dai mutane su yabe shi. Shi ya ji dadi gurin Ubangiji komai fanko yake”.
Ta ja tsaki, “Ai kin ji irinta. Dad shi ya sa na qi amincewa da makarantun nan, islamiyya tahfiz, makarantar magriba ko yaushe ba ta da hutu tana zuwa ana zura mata al’adun mutan da. Ta sauke abin da aka ce an fi buqata, wato alqur’ani mai girma, amma har yanzu ta qi ta haqura”.
“Ke ma da a ce kina zuwa duk za ki watsar da wadannan shirmen da ki ke yi”. Hajiya Rahma ta fada.
“Hum Ammi kenan, da girmana da komai kawai sai na je na zauna ana koyar da ni salon kowa ya raina ni? Ita dai da ta ga za ta iya sai ta je ta qara ta”.
“Da Allah malama rufa mana baki”. Ammi ta ce da ita.
A take ta ji haushi, Alhaji Usman ya dubi hajiya Rahma.
“Ba kya kyautawa”.
“To yanzu me na yi ne?”
Bai ce da ita komai ba ya miqe ya rufa wa Aazeen baya.
A lokacin da kowa ke bacci, a lokacin ta ke sake sabon zama a gindin akwatun talabijin, a nan ne ta ke cashe mata kallon. Qarfe goma sha biyu tana zaune a sitroom dinta ta dora qafa daya kan daya, lokaci-lokaci ta kan dauki tea ta kurba. Rimot ta dauka tana canza tashoshi. Ta ji dadin film din da ta ga ana yi. Ta ajiye rimote gaba daya hankalinta ya karkata daidai lokacin da aka nuno jarumin da budurwarsa rungume da juna suna yi wa juna wani irin wasa, yadda jarumin yake ba ta wani hot kisses tare da sake rungume ta tsam-tsam cikin wani irin salo, ji ta yi gaba daya hankalinta na neman fita a jikinta.
“Wayyo! Tana son wannan rayuwa, su kam Turawa sune suka zo duniya a sa’a, sukan yi duk abin da suka so a gaban kowa ba su da shamaki da duk wata rayuwa da holewa.
Ta lumshe ido tare da kwantar da kai a allon kujera tana saukar da numfshi, ina ma a Turan aka halicce ta? Ba za ta iya jurewa ba. ta zaro waya ta shiga lalubar wata lamba.
Ringin daya aka dauka daga dayan bangaren aka ce, “Ya na ji muryarki haka? Me ke faruwa?”
“Komi ma ya faru. Ya za a yi ka zo gare ni?”
“Ke ba ki da hankali? Idan na zo in ce me? Ba ki ga dare ya yi ba? ki lallaba zuwa gobe, amman gaya min duk me ya janyo hakan”.
Ta ja tsaki hade da katse wayar. Ta yi lamo cikin wani irin shauqi, shi ne kawai yake dan kwantanta yadda ta ke so, shi ne yake fahimtar feeling dinta, shi ma din tana tunanin don ya yi karatu a Turai ne.
“Mtsew!” haka ake ta faman son ta yi aure, to ta auri me? Babu abin da auren bahaushe ke haifarwa sai bacin rai. Su dai burinsu idan suka tashi da safe Allah-Allah suke yi su wuce gurin neman kudi, idan suka tashi a kasuwar su wuce majalisar gulma, wanda su abokan nasu ke dora musu wani tunanin ko layin rashin mutunci. A nan suke koyon tsumulmula, suke

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login