Showing 27001 words to 30000 words out of 34150 words

Chapter 10 - KYAUTAR ZUCIYA Book Complete By Bilkisu H. Muhd.txt

14 Jan 2025

3060

ni da tamkarka. Ina yinka wallahi ka fidda ni kunyar qawayena, zan nuna musu taka kyautar’.
Ya mirgino da ita gabansa yana murmushi.
“Rangida zan iya yin komai domin farin cikinki. Ba ma haka na so ba”.
“Dad taho mu je ku yi sallama da su, suna xaki”.
Ta janyo hannunsa. Hajiya Rahma ta kawar da kai ba ta ma san suna yi ba, ita dai ko ba komai ta rabu da qaya.
Nurat ce ta shigo, ta bi ta da kallo.
“Ina kayanki?”
“Ammi na yi kyau ko? Kwata na faxa shi ne na saka kayan qawata, maqociyarsu ce, ina Yayata?”
“Tana can xaki ita da qawayenta’.
“Okey, bari in je na ci abinci, yunwa nake ji”.
Ta yi waje, ta bi ta da kallo.
“Aazeen ina ma za ki zama kamar Nurat?”
Ta kaxa kai kawai.
Washegari da sassafe su Zee suka wuce, ranar Hajiya rahma ji ta yi kamar an sauke mata dutsen dala daga kanta.
Alhaji Usman ne ya shigo sitroom yana faman cika da batsewa. Ta yi kamar ba ta ganshi ba, ya zauna xaya daga cikin kujerun.
“Sun tafi hankalinki ya kwanta, ban ce zan auri xaya daga cikinsu ba. Da sun ci gaba da zama ina jin sai kin qone su. Ni ban tava jin uwar da ke kishi da yaranta ba, ita kanta Aazeen kishi ki ke da ita, ko wata kyautar na yi mata sai kin nuna damuwarki. Wallahi sam ba ki da tunani”.
Ba ta so tanka mishi ba, sai dai a wannan gavar ba ta jin za ta iya yin shiru.
“Ko a tarihi ban tava jin inda aka ce ga wata uwa can na baqin ciki da abin da uba ya yi ma xiyarta ba, ballantana Aazeen wadda nake jinta tamkar numfashina. Aazeen na fara samu a duniya, ina sonta fiye da komai, duk son da za ka yi mata ba za ka fi ni ba. Don haka nake kiyaye duk abin da zai rusa mata tarbiyya, idan za ka siyi duk abin da ke duniyar nan ka ba ta zan fi kowa farin ciki, amma ka dinga yin abin da addininmu ya halatta”.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*



*NA*




*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_










*last Free page 15*








*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*




*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*


*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*




_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*


```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```




*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*




*_____________________________________*


*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_____________________________________*








*“T* unda dai su xin sun tafi komai ya wuce ko?” Ya faxa yana qoqarin matsawa jikinta.
“Ki yi haquri, taso mu je ciki zan nuna miki wani abu”.
Shi kanshi ya yi mamakin yadda yake faman kimtsa kansa kamar wani mace, wankan shadda ya yi gizna, ash colour, hularsa ma ash, hatta takalminsa ash ne, ya feshe jiki da turare ya fito sitroom cikin qoqarin gyara link xin hannun rigarsa.
Maryam zaune tana kallon talabijin.
“Wow, qaramin maigidan ka fa yi kyau, sai ina?”
Ya yi murmushi, “Matar Yaya yau zan tunkari mutuniyar. Yau zan yi mata zuwa na musamman”.
“Okey, kana son ka ce iyanzu ta san komai kenan?”
“Ke dai kawai ki yi min addu’a, ki bari sai na dawo mun yi maganar”.
Ya xauki key xin mota ya yi waje. Ta bi shi da kallo cikin tave baki.
Da alamar Hajiya rahma ba ta nan, hakan ya yi masa daxi, kai tsaye ya doshi vangaren Nurat.
Tana kwance a gado, bacci ta ke lakadan, iskan fanka na faman watsi da gashin kanta. Gabansa ne ya faxi, ya wani irin bugawa wani abu ya tsarga masa tun daga tsakiyar kai har zuwa yatsunsa. Duk yadda yake zana halittarta ta wuce nan, ashe dai bai ga komai ba?
Wani irin sha’awarta ya dinga shigarsa, zuciyarsa ta dinga ingiza shi da ya afka mata. Ya yi tattaki zuwa gabanta, ya xan ranqwafa a kanta, wani qamshi ya shaqa nan ya qara fitinuwa. Hannu ya kai zai xauke gashin da ya zubo fuskarta, ya ga ta xan motsa.
Tsam! Ya qame a tsaye, can ta qara nutsuwa cikin baccinta haka ya ba shi damar tattare gashinta yamaida shi baya. Ya xan matso da kansa daf da fuskarta zai sumbaci xan mininin bakinta. A karo na biyu ta sake motsawa, ya tuna idan ta farka ta ganshi akwai matsala. Da sauri ya fice daga xakin cike da tsananin so da sha’awarta, sai kuma ya jira ta a gurin Aazeen.
A daidai wannan okacin ta fito daga bathroom, bai san sa’ar da ya afka mata ba. sun gama shagalta da juna, gaba xaya sun mance a inda suke, hankainsu ya fita a jikinsu, shi kam Zaruk ji yake yi kamar tare yake da Nurat, surarta ce ta dinga yi masa gizo.
Daga vangaren Nurat firgigit ta farka, ta dinga ji a jikinta tamkar wani abu ya faru da ita. Ta miqe zaune, qamshin turaren Zaruk ta shaqa. Dam! Gabanta ya buga, da sauri ta dubi jikinta, riga ce a jikinta iya gwiwa mai xan siririn hannu. Ta miqe cikin sauri, hijabi ta xauko ta xora a kai ta shiga bathroom ta wanke baki. Al’adarta ce ko da baccin minti goma ta yi ba ta iya fuskantar kowa sai ta goge baki, ta xauraye fuska.
Ficewa ta yi daga xakin, kai tsaye sashen Aazeen ta nufa, duk takun da ta yi yana daidai da bugun zuciyarta. Haka kawai ta dinga jin wani tsoro na ziyartar zuciyar tata. Daf da za ta kutsa kai ciki ta dinga jin wasu irin surutai marasa kan gado, ta xan yi turus! Abu ya qi qarewa kawai sai ta tura kai ciki da qarfi. Gabanta ya buga, kanta ya yi wani irin sarawa yana kuma juyawa, jikinta ya hau vari. Ta yi saurin runtse idanunta ta kasa aminta da abin da ke gabanta, me ya sanya ta yi irin wannan mafarkin? Me ke faruwa da ita? Idan bacci ta ke Ubangiji Ya gaggauta farkar da ita.
Ta buxe idanunta, har yanzu suna nan, wayyo Allah ba mafarki ta ke yi ba, “Allahumma ajirni fi masibati…” Ta shiga maimaitawa cikin zuciyarta.
Kunyar kanta ce ta kamata, ta juya cikin matsanancin kukan da ke son qwace mata, gudu-gudu, sauri-sauri ta nufi xakinta inda ta zube a qasa. Wani irin azababben kuka ya qace mata, wani irin tsanar Zaruk ta dinga xarsuwa a zuciyarta. Tana ji a ranta ba ta tava tsanar wata halitta kamarsa ba.
Yaya Zaruk mutumin da ta ke matuqar ganin mutuncinsa wanda magana ba ta cika damunsa ba, idan yana magana wani lokacin tamkar wani limami.
Ta runtse idanu, kuka ya sake qwace mata, ‘Babu kama Yaya Zaruk babu kama, waye ya san tsawon lokacin da suke aikata hakan?”
Hirarsu da Fa’iza qawarta ta faxo mata, “In dai riqe hannu ne ashe da kowa ya samu ciki, da shegu sun cika duniya. Ke da Allah can tsokanarki Amminki ta ke yi, kawai tana tsoratar da ke ne kawai, ba kya ganin ‘yan Indiya har rungume juna suke yi da namiji, to su me ya sa ba su tava samun cikin ba? ‘Yan matan zamanin nan iyayen shan minti duk me ya sa ba su samun ciki?”
Nurat ta ce, “ko ma me ye ni dole ne in kiyaye, mahaifiyata ce yadda uwa ta ke da girma zai iya yiwuwa idan aka riqe hannun nawa in iya samun ciki”.
Ta dawo daga duniyar tunani, lokaci guda abin da ta gani ya dinga dawo mata.
“Yayata kin ci amanar Ammina, Zaruk na tsane ka, ba zan yafe maka ba”.
Taqarqarewa ta yi ta turar da shi, ya zube gefe yana faman ajiye numfashi.
“Kai wai ka mance a inda muke ne, ba ka tsoron wani ya ganmu?”
Da sauri ta janyo rigar ta saka.
Ya dube ta da lumsassun idanunsa,
“Aazeen, ina son Nurat, ki taimake ni kada in rasa ta”.
Ta xaure fuska tamau.
“Ba ka tava ganewa furta mata wani kalaman so zai iya nesanta mu da juna. Ka bari da zarar ta zana jarabawa sai ka yi duka xaya xauka”.
‘Ba zan iya ba, ba zan tava amincewa ba. wannan karon dole ne kowa ya sani. Na gaji, ina zuwa”. Ya ce da ita ya miqe.
Ta bi shi kawai da kallo.
Nurat ta gaji da kuka, idanun nan sun yi jawur har wani tasawa suka yi.
Takun tahowa ta ji, ta yi saurin kifa kai cikin filo, ga mamakinta muryar Zaruk ta ji a kanta.
‘Nurat, tashi za ki yi, ina son za mu yi wata magana da ke. Na zo ne kawai don ke, na san kina jina’.
Ji ta ke yi kamar ya watsa mata garwashi. Ya kaxa ya raya ko motsawa ta qi yi. Ya koma yi mata magiya tamkar dutse haka ta koma mishi, kamar zai yi kuka, tilas ya bar mata xakin, takaici bai sa ya bi ta kan Aazeen ba.


*** *** ***
“Sam-sam sonka ne ba ta yi, ta gane inda ka dosa shi ya sa ta xauki wannan matakin”.
“Ba zai tava yiwuwa ba akwai alaqa mai qarfi tsakanina mahaifina da nata, in na ga dama sai dai kawai ta ga an xaura aure. To amma don in fita haqqinta ne ya sanya na shaida mata. Amma ita xin ma…”
“Zaruk kenan, kada ka mance kamar yadda Dad ke qaunarka ita ma haka nata ke qaunarta. Ina ba ka shawara in ka ga ba ta ra’ayinka ka haqura ga mata nan da yawa?”
“Matar Yaya idan na qyale ta mutuwa zan yi, ni kaina ban san yadda nake sonta ba, wallahi dole sai na aure ta duk bala’i sai na mallake ta”.
“Uhum Zaruk kenan, shi kenan Allah ya ba ka sa’a, Ubangiji ya zava mana abin da ya fi alkhairi”.
“Daga baya kenan, ni kam ko babu alkhairin zan aure ta, sai fa na auri Nurat. Shekara kusan goma ina gadinta, lokaci xaya na faxo? Ina! Allah ba zai xora mini wannan ba, ba zai tava xora min ba’.
“Shi ke nan”.
A can bedroom xinsa sambatu ya yi ta yi tamkar mahaukaci. Ya sha sigari babu adadi duk ba ta gamshe shi ba, ya buxe firij ya xauki kwalbar giyar da rabonshi da ya sha ya fi wata uku, tun lokacin da ya yi ma Dad xinshi alqawari, bai ma san akwai ragowa a firij xin ba sai da ya hange ta.
Kafa kai ya yi bai sauke kwalbar ba sai da ya ga babu komai a ciki, ya kwanta rigingine, Nurat ce ke masa gizo. Ya miqe tsaye yana sanxa wai zai kamo ta. Haka ya yi ta yi, daga qarshe ya yi wani irin wawar faxuwa, har sai da ya faxa kan kwalbar ta fashe ta yi masa wata muguwar yanka a gefen fuska da qirji, jini ya valle.
Daidai lokacin Alhaji Aminu ya turo qofa, duk warin giya ya cika xakin, ga xansa kwance cikin jini yana faman amai. A sukwane ya qarasa gare shi ya janyo shi kan cinya yana jijjiga shi. Sunan Nurat kawai yake faman kira, a ruxe ya kira likitansa a waya tare da yi mishi bayanin abin da ke faruwa.
“Zaruk ashe qarya ka yi min, da man yaudara ta ka yi ka ce ka daina? Me ya sa?”
Qoqarin qwacewa ya dinga yi daga jikinsa yana kiran sunan Nurat.
Kuka Alhaji Aminu ya saka, yadda ya ga jini ya tsananta zuba. Likita ne ya turo qofa. Shi kanshi hankalinsa ya tashi.
Ya dubi Alhaji Aminu, “Garin ya ya hakan ta faru?”
“Ban sani ba, kawai na xai ji yana ta ambatar wata Nurat”.
Likita ya sauke ajiyar zuciya.
“Ko wacce tana da alaqa da shigarsa wannan yanayin”.
Allura ya yi masa ya yi dressing xin raunikan, ya kuma xora masa da allurar bacci, kafin wani lokaci bacci mai qarfi ya yi awon gaba da shi”.
Hajiya Amina da Maryam sun dawo daga gidan suna, suka riski mummunan labari.
“Da na san abin da zai aikata ma kansa da ban barshi shi kaxai ba”.
A nan ta kwashe labarin komai ta shaida musu.
“Ban da abin Zaruk ya sani dole ma ya aure ta ko da ba ta so, da ita da Baban nata duk a hannun Alhajina suke shi ne fa qarfin arziqin ba ko wannan uwar girman kai ya ce yana so dole ne ta amince, balle ita Nurat baiwar Allah, yarinyar da babu sa wa ba fitarwa”.
Yana zaune a tsakiyar gado ko a jikinsa halin da ya ganshi a ciki, ya sani hakan zai xaga ma Dad hankali, ba zai bari ya rasa Nurat ba, sigarinsa ma ya ke faman zuqa.
Hajiya Amina da Alhaji Aminu suka shigo xakin daidai lokacin wutar sigarin ta cimma hannunsa. Da gudu Alhaji Aminu ya zare tabar a hannunsa ya cillar a qasa haxi da mitsike ta a qasa. Suka zauna a gefe, gaba xaya yanayinsa ya nuna yana cikin damuwa, ya yi ramar wuni xaya.
Ya raunana murya, “Haba Zaruk har kana da damuwar da ka ke tunanin ba zan iya magance maka ba? Maryam ta gaya min komai kai ma da gangan ka tada hankali, ka sani ni da Alhaji Usman mun zamo xaya babu abin da ba zai iya mallaka min ba”.
“Daddy, Nurat ba za ta so ni ba, ta daina kula ni, ba zan iya rayuwa babu ita ba, ina tsananin sonta, da ita kaxai nake son rayuwa, ka taimaka kada ta guje mini”.
“Ya isa haka, na ji za ka auri Nurat, amma sai in na ga ka raba kanka da waxannan mugayen xabi’un, domin babu uban da zai so ka zama surikinsa in har ba ka daina ba, zan fita a harkarka…”
“Ban da ma abin Zaruk, ai ita xin taka ce, ko da ba ta so dole ma ta so ka, ka kwantar da hankalinka in ba haka ba za ka kashe rayuwarka a banza, kana ji kana gani wani nan zai aure ta”.
“Mommy na yi muku alqawarin na daina har abada, ku yi haquri”.
Suna zaune a falo dukkansu, kallon suke yi, hankalin Alhaji Usman ya karkata ga Nuratm ya fahimci kamar akwai abin da ke damunta. Kallon ta ke yi amma tunaninta na wani guri.
“Nurat wai me yake damunki?”
Ta tilasta wa kanta sakin murmushi, wato yaqe.
“Dad me ka gani? Lafiya ta qalau”.
“Tunda na dawo na ganta a haka, na tambaya ta ce kanta ne ke ciwo”. Hajiya rahma ta faxa.
“Ai na sha magani, ya daina ciwo”.
Aazeen ta xan dube ta, ta kawar da kai, don idan tana kallon program xin Ahmad ba ta son abin da zai katse ta, tana tunanin kamar za ta samu hasken inda za ta same shi.
Wayar Alhaji Usman ta shiga ruri, ya xaga.
‘Subhanallahi, yaushe? Okey za mu shigo gobe, Allah ya ba shi lafiya”.
Gaba xaya hankalinsu ya koma kansa. Ya ajiye wayar cikin dubansu.
“Lafiya kuwa?” Hajiya Rahma ta tambaya.
“Wai Zaruk ne ya yi hatsari”.
Aazeen ta ji wani shook, “Daddy xazun fa ya bar gidan nan?”
Ta iya yuwuwa ko a hanyar komawarsa ne ya gamu da tsautsayi”.
Duk ta gigice.
“Dad yana asibiti ne?”
“A’a yana gida”.
“Allah Sarki Zaruk”.
Ta wutsiyar ido Nurat ke duban Aazeen, ji ta ke yi kamar ta shaqe ta, ta ja tsaki a zuciyarta, dole ta damu tunda abokin fasiqancinta ne.
‘Idan Allah ya kai mu gobe, sai ku je gaba xaya”.
“Ni dai ba za ni ba, gobe wuni za mu yi a school”.
“Qarya ki ke yi, ba ki isa ba, wallahi sai kin je, mara mutunci”.
Yadda ta hayayyaqo mata ne ya sanya ta tsuke baki.


*** *** ***
Alhaji Usman ya nuna farin cikinsa sosai, “Ban da abinka Alhaji Aminu, kai fa me iya xaukar Nurat ne ka bada aurenta, ballantana yarona ne mai sonta”.
“Eh na na sani, amma duk da haka ina son ka ji ra’ayin Nurat”.
“Kada ka damu, ban da lalacewar zamani, auren fari iyaye ne ke sama wa ‘yarsu miji. In dai Nurat ce kada ya damu an gama, kawai bari zai yi ta qarasa karatu, lokacin ta qara tasawa, don ita xin har yanzu akwai quruciya a tattare da ita, shekara sha shida”.
“Gaskiya ne”.
Duk wannan hirar a ofis xin Alhaji Aminu ake yinta.
‘Yanzu ya jikin nasa?”
“Da sauqi”.
“Yanzu na barsu sun tafi duba shi dukkansu”.
Sun zube a sitroom, ita kam Aazeen har ta isa xakin Zaruk, Hajiya Rahma suna gaisawa da Hajiya Amina da tambayar yadda mai jiki ya qara ji, hankalin Hajiya Amina na ga Nurat, tana mamakin me Zaruk zai yi da wannan tatsitsiyar yarinyar, ina ma a ce ta xan fi haka? Babu matar da ba za ta so Nurat ta zame mata suruka ba, duk xabi’unta abin so ne, kunya, biyayya, kawaici da ibada. Nan-nan ta dinga yi da ita, ta so su xan tattauna maganar da Hajiya Rahma sai dai ta ga alamar kamar ita xin ba ta san komai a kan zancen ba.
“Ya aka yi na ganki ke xaya?”
Cike da jimami ta ke dubansa.
“Dukkanmu muka zo, to ina ki ka baro Nurat?”
“Tana can sitroom”.
Ya xan yi shiru, zuwa wani loakci ya koma ya numfasa, “Aazeen, na karaya, kamar Nurat ba za ta so ni ba”.
Ta xan murmusa, “Ka daina shakka Zaruk, babu macen da za ta ganka ba ta yi fatan ta mallake ka ba”.
“Ki gaya min me zan yi ta so ni?”
Lakuce masa hanci ta yi.
“Dube shi don Allah, duk qaramar yarinya ta gama rikita shi’.
“Don ba ki san yadda nake ji ba ne”.
“Ta ya za a yi na ji?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login