Showing 15001 words to 18000 words out of 34150 words
Chapter 6 - KYAUTAR ZUCIYA Book Complete By Bilkisu H. Muhd.txt
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 9*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
*L* abari sai dai kai, ni da kullum ke kulle a cikin gida… amma dai yanzu gaya min yaushe zan ganka?”
Ya yi ajiyar zuciya, “Saura qiris na zo, to amma idan na zo gurin wa zan ce na zo in na tura kiranki, ke kuma wa za ki ce ya zo?”
Ta yi shiru.
“Sai ki ce abokinki ne?”
“Kai ai namiji ne, ba zai yiwu ba’.
“Ok, to za ki ce saurayinki ne ya zo?”
Nan ma ba ta iya magana ba. qoqarin share caftar ya yi, ta yi saurin dawo da zancen.
“Da gaske ni xin budurwarka ce, kana sona kenan?”
Ya yi murmushi yana jin daxin yadda yake zolayarta.
“Ina sonki mana”.
Da sauri ta katse wayar ta yi ciki da shi. Ta yi rigingine a gado haxi da runtse ido kawai, kunyar kanta ta ke ji. Ji ta ke yi kamar ta aikata babban zunubi, amma a can qarqashin zuciyarta wani irin nishaxi ta ke ji, ko me hakan ke nufi?
*** *** ***
“Ji yadda duk ki ka tada hankali kamar wadda ki ka aiki jaririya, wai ke ba kya ganin yadda hadari ya haxo, ga gari ya yi baqiqirin? Ni ba abin da ke tayar min da hankali irin iskar da ke tasowa, kin san Nurat da tsoro, na sani duk inda ta ke tana cikin ruxu. Na kira Hajiya Fati ta ce tun xazu ta fita a gidan, sai yanzu nake jin haushin rashin waya a hannunta, da sai mu kira ta”.
Shewa Aazeen ta yi ta qaraso gaban Amminta tare da rungumo ta ta vaya.
“Dube ki don Allah, inda a ce ni ce da yanzu kina nan hankalinki a kwance, da yanzu ma kina bacci, amma dai ki kwantar da hankalinki ‘yarki na da wayo, za ta dawo lafiya kin ji Amminmu, kuma na yi miki alqawari da kaina zan siya mata waya”.
Daga can vangaren Nurat hankalinta ya yi qololuwar tashi, musamman yadda ta ji ana ta tsawa gaba xaya a qanqame ta ke tafiya, cikin sharar qwalla duk motar da ta tsayar kko kallonta ba su yi. Tasowar iska ya tsananta sanadiyyar haka aka xauke wuta, gari ya soma duhu, jama’a sai gudu ake. Cikin lokaci qanqani ruwan sama mai qarfi ya sauko haxi da walqiya.
A hankali yake tafiya saboda kada ya haifarwa kansa matsala, lokaci xaya ya dallaro fitila ya yi arba da fuskar Nurat. Dam! Ya ji gabansa ya buga, sauran qiris ya saki sitiyari. Ya sake rage gudu, ya san rasa mota ta yi a daidai gabanta ya yi parking, bai fito ba bai kuma kashe motar ba, tunaninsa za ta doso shi don neman taimako, maimakon haka gani ya yi tana neman kwasa da gudu, haka ne ya sa ya tada motar. Gabanta ya sha ya sake tsayawa, ta yi saurin kauce wa motar. Bai sake mamaki ba in ya yi la’akari a abin da ya faru a makaranta, dole ya yanke shawarar yi mata magana. Kashe motar ya yi ya fito cikin sauri ya qarasa ya sha gabanta. Ta tsaya qyam kanta a qasa, jikinta na rawa.
“Ki shigo mota in kai ki”.
Ta yi saurin kaxa kai cikin tunanin inda ta san wannan muryar.
A hankali ta xago kaiza ta saci kallonsa, aka yi sa;a gari ya haska da walqiya idanunsu suka gauraya da juna. Gaba xaya Deedat ya kixime wani irin bugawa gabansa ke yi, shin wace irin yarinya ce wannan wadda yake jin abin da bai tava ji ga wata mace ba a yayin da ya xora ido a kanta, ko da kuwa a hoto ne tana yi masa kwarjini, ji yake yi ma kamar yana tsoronta, ita ma xin ta gane shi.
Abokin Principal xin sune sai dai haka ba zai sa ta shiga motarsa ba, ko da hakan na nufin za ta kwana tana tafe a qasa ne.
Ya sanyaya murya, “Ke fa xalibar abokina ce, na san kin gane ni, ba zan cutar da ke ba”.
“Ka yi haquri na gode”.
Yadda ya lura da ita ya sani ba za ta tava shiga ba, ga dare na daxa yi, ya xan kausasa murya wai ko da za ta ji tsoro.
‘Ki shiga na ce!”
Ta raunana murya kamar za ta rushe da kuka.
“Allah ba zan shiga ba”.
Takaici ya sanya ya shige motar, ya murxa key, amman ya kasa tafiya. Wayarsa ya xauko ya shiga kiran xaya daga cikin masu adaidaita sahunsa tare da yi masa kwatancen inda ta ke.
Bai bar gurin ba, har sai da ya tabbatar an xauke ta tukunna ya samu nutsuwa.
*** *** ***
“Ammi ga ‘yar mitsilanki nan ta dawo ba a cinye ta ba”.
“Za ki ci gidanku, ce miki na yi ba za ta dawo ba?”
Aazeen tana dariya, “Kin ga wannan Umman taki gaba xaya ta sukurkurce kamar ce mata aka yi an sace ki”.
“Ai ko ba don wani abokin Principal ya yi gadina ba da yanzu na sume a gurin, don ba kowa a gurin, ya yi ta nacin in shiga motar ya kawo ni, na qi shiga, har sai da na samu adaidaita”.
“Kin yi daidai”.
“Ammi, haka ne daidai? Inda ba ta samu abin hawa ba fa?”
“Na ma san Allah ba zai sa hakan ta faru ba”.
Yana gaisawa da Hajiya Rahma idanunsa na yawo, yana tsammanin ganin Nurat. Ya numfasa, “Ba kowa a gidan ne sai ke kaxai?”
“Mutuniyarka na xaki bacci ta ke yi, ba ta da lafiya, ita kuma Aazeen na shashenta”.
Ya miqe, “Bari in je mu gaisa”.
“To”. Ta ce da shi.
Ta miqe a doguwar kujera tana jin kixa.
Ta faxaxa fara’arta, “Yanzu nake shirin kiranka”.
“Kirana? Kina da magana kenan?”
Ta kaxa kai, ‘Kawai kewarka na ke yi”.
“Sai ga ni na zo ba, amma ni ma tawa ce ta kawo ni’.
Ta miqe zaune cingam ta xauka a kan table ta vare tare da cillawa a baki, ta tauna, ta yi qwai haxe da yin qas-qas ta koma ta tattara hankalinta kanshi.
“Ina sauraronka”.
Ya zauna kusa da ita, ya marairace kamar mai shirin yin kuka.
“Na kasa jurewa, ba zan iya ba”.
Ta bi shi da kallo, ‘Wai me ke faruwa?”
“Ina son Nurat, lokaci ya yi da zan furta mata. Rashin furtawa a wanan lokaci zai iya haifar da komai”.
Tuntsirewa ta yi da dariya, har da qyaqyatawa.
Ya qulu sosai, miqewa ya yi zai fita, ta sha gabansa ta kama hannunsa ta zaunar da shi.
“Afuwan, mu yi magana, amma ranka ya daxe ka rasa wadda za ka zava ta zame maka mata sai qwaila, kuma ma wacce ba ta waye ba? kuma wai har ma ka dubi idanuna ka ce kana son qanwata? To wai ma gaya min da me na rage ka?”
Ya watsa mata harara, “Ok, haka ki ke son na yi ta zama babu aure ko?”
“Why not, yanzun da me na rage ka ko kana son ka ce ni xin na gundire ka?”
“Kin ga Rangida wannan daban ne, kin san kamalar mutum shi ne aure ko?”
“Na ji wannan, amma me ya sa ba za ka samu gogaggiya irinka ba? Ka san Nurat qarama ce ba za ka samu yadda ka ke so daga gare ta ba”.
“Kin ga Rangida kada ki ce kishi ki ke da ita?”
Ta ja wani dogon tsaki.
“Matar arziqi ma ban yi kishi da su ba sai wannan? Kawai dai ina tsoron alaqarka da ita kada ka laluve mini ita’.
“Kin ga ki ajiye zancen wasa ju tausaya mini ki gaya min ya zan yi, ta ina zan fara?”
Ta lakuce masa hanci, “Dube shi don Allah ko kunyata ba ya ji. Ka ga shawarata ka bi a hankali, muddin ka kuskura gurin furta mata kalmar so, kai da ita, kun soma wasan vuya kenan in ma ba ka yi sa’a ba kun qulla gaba kenan don haka ka bi a sannu cikin dabara za ka fahimtar da ita a aikace”.
Ya miqe ya shiga zarya.
“Nurat, ban ga damar canza ta ba ne yarinyar bagidajiya ce amma ka ban lokaci, da sannu zan fahimtar da ita abin da duniya take ci….”
“Ban amince ba”. Ya yi saurin katse ta cikin gigita, “Ni rayuwarta ta yi min a haka nake son rayuwa da ita”.
Ya koma ya zauna cike da tsananin tsoro “Come down, abokina, kana tsoro ko, amman ba ka tabbatar ita din matarka ba ce ballantana ka…”
Turo qofar da a ka yi ne ya katse daga maganar da take son yi, sanye ta ke da zumbulelen hijab, Aazeen ta saci kallon Zaruk cikin muryar raxa.
“Haka xin yayi maka ko?”
Ya xan lumshe ido ya buxe alamar hakan ya yi masa.
“Yaya Zaruk sannu da zuwa”.
“Yauwa qanwa ta gwara da Allah ya kawo ki, daman ya dame ni da surutu”.
Shigar jikinta ya sanya Nurat jin kunyar Zaruk, three quater a jikinta na wando, sai riga plat, kan nan ya sha attach, ta lura da yadda Zaruk ke faman satar kallonta. Yana ji tamkar ya bi ta.
“Ya Zaruk me ya sa ba ka yi mata faxa na ga kamar tana jin maganarka”.
Ya maida kallonsa gare ta, “A kan me fa?
“A kan me? Ba ka ganin yadda ta ari al’adar da ta sava wa addininmu na islama?”
“Kada ki damu da hakan, ra’ayinta ne haka, wataran za ta daina da zarar ta shiga daga ciki shi kenan komai zai sauya, kamar ba a yi ba, kin ji?”
A hankali ta rausayar da kai.
“Haka ne Yaya Zaruk, Allah ya nuna mana lokacin”.
Wani mayen kallo ya dinga bin ta da shi har sai da ta tsargu.
Ya yi murmushi, “Ba kya son kallo da yawa ko? Ki yi haquri qanwata, kina da kyau da yawa. Ban gajiya da kallonki, da ma a ce mu dauwama a haka”.
Ta xan murmusa, “Yaya Zaruk ka iya zolaya”.
Ya sake riqe hava cikin kallonta.
“Murmushi na yi miki kyau, ina ma kada ki daina?”
“Yau ka zo ne musamman don ka tsokane ni ko? Ka san wani abu?”
Haka kawai ya ji zuciyarsa ta buga.
“Sai kin faxa”.
“Ammina tana son Yayata ta yi aure, na ga kai ma ka faxa idan ta yi aure za ta daina duk waxannan abubuwan shi ya sa nake ta neman taimakonka”.
“Shi ya sa na ce ki ba ni lambar mutumin nan”. Ya katse ta da faxin haja.
“Na san yadda zan bi in daidaita komai”.
“Ba ka sani ba, komai ya daidaita har na zurmo shi da bakinsa ya furta cewar yana sona”.
Lokaci xaya ya firgice duk walwalar fuskarsa ta dusashe, cikin shaqaqqiyar murya ya soma magana, “Kina son ki ce kin zubar da qimarki gurin roqonshi ya so ki ko? Nurat kin hauka ce? Me ya sa ki ka fitini kanki da yawa a kan wannan? Ki gaya min ki ke sonsa ko? Ki gaya min gaskiya”.
Ta tsorata da sauyawarshi.
“Yaya Zaruk ni in ce ina sonsa? Wace irin magana ka ke yi haka?”
“Shiru! Na ce ki rufe min baki, ni za ki raina ma hankali? Ni za ki yi wa haka?”
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 10*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
*A* zahiri ta gama tsorata ba ta tava ganinshi cikin irin wannan yanayin ba, gani ta yi ya miqe a zafafe ya fice ya turo qofa da qarfi har sai da ta firgita, kawai ta bi shi da kallo, ta rasa me hakan ke nufi.
Ta sauke ajiyar zuciya, a sanyaye ta miqe ta yi waje.
A harabar gidan ta samu Ammi zaune tana alwala, Aazeen na qoqarin ficewa.
“A’a sai yanzu ki ka bar Ya Zaruk ya tafi?” Aazeen ta faxa.
Nurat ta xaure fuska.
Aazeen ta maida kallonta ga Ammi tana faxin, “Ammi da alamun tuwona maina za mu yi”.
“Ammi kina jinta ko? Wallahi za ta sa na daina kula shi”.
“Me ya yi zafi? Allah ya ba ki haquri, ai shi xin Yayanki ne”. ammi ta ce tana murmushi.
“To ai Ammi shi ma babu abin da zai yi da qwaila”.
“Eh xin na ji”. Nurat ta faxa a qufule kamar za ta yi kuka.
Binshi kawai ta ke da kallo, yadda ta ga yana faman dudduba ko’ina na gidan.
“Yallavai lafiya kuwa?”
“Ina duba ta inda zan fara ne”.
“Me za ka fara?”
“Rangida za ta yi manyan baqi daga Jos, tana buqatar a yi wa gidan kwaskwarima”.
Ta jinjina kai cike da takaici.
Ya janyo kujera kusa da ita ya zauna, ta dube shi cikin sanyin murya, ya fahimci haka, “Da magana ne?”
“Ina ganin bai dace a ce ‘yar da muka haifa ta dinga tsara mana abin da za mu yi ba, hatta da girki sai wanda ta ke so ake yi? Ya kamata ka yi nazari watarana fa gidan wani za ta je, za ta iya rayuwa da kishiya ko uwar miji, kana ganin za su xauki wannan? Waye zai iya zama da ita da wannan xabi’un? Ya kamata ka duba ka koma ka sauke ta daga wannan layin ya kamata Aazeen ta san rayuwa, sangartar nata ya yi yawa, rayuwa na iya juyawa a kowane lokaci bana fata, amma…”
Ya yi saurin katse ta, “Ba za ta tava ganin duhu a rayuwarta idan kina tunanin gidan aurenta ne, su kansu mazan yanzu har da iyayen nasu duniya suke bi, idan za ta ce mijinta ya durqusa ta hau bayansa ina rantse miki sai ya durqusa”.
“Shi kenan”. Ta ce da shi, ta koma ta tsuke baki.
“Kin yi shiru, ba gaskiya na faxa ba ne?”
“A naka ra’ayin ka yi daidai amma don ya kamata a qalla mu koya mata mu’amala yadda za ta jeranto wa wanda ya girme mata magana”.
“Okey, gaya mini wa ya tava kawo qararta? A kunnena ina jin yadda ake yaba mata, ba ta tava yin ba daidai ba”.
Ta miqe cikin qoqarin barin gurin, ta xan dube shi a qufule.
“A ganinka ba…”
Kan ya kai ga magana ta yi saurin barin gurin.
*** *** ***
Da murnarta ta danno kai hotel xin har zuwa xakin da yake, yana tsaye ya juya baya da gudu ta rungumo shi ta baya, ta daxe a haka ba tare da ya tanka mata ba. Ta sake shi ta zagayo gabansa, fuskar nan ta gani a xaure.
“Why?”
Ya kamo hannunta suka zauna.
Ya xauki tsawon lokaci kafin ya yi magana, gaba xaya ta gama kafe shi da ido, cikin son ji daga gare shi.
Ya furzar da wani huci.
“Ke ce ki ka lalata komai”.
Cike da mamaki ta dube shi.
“Ni kuma? Da na yi me?”
A qufule ya zayyane mata komai, hankalinta ya yi matuqar tashi. Ta miqe a zuciya, “Zan yi maganinta. Wallahi sai ta gane kurenta”.
Ta nufi hanyar fita, ya yi saurin janyonta ta zube a jikinsa, za ta yi magana ya danna harshensa cikin bakinta. Sun daxe a haka, cikin wani irin salo ya janye harshen nasa, sai dai tana manne a jikinsa.
“Ina son mu bi komai a hankali kamar yada ki ka ce yarinya ce za mu bi da ita ta dabara. Ina so ki samu bayanin komai daga bakinta, ina son ki yi mata wayo har ki samo mana lambarsa, inyaso sai ki bar min ragowar aikin, ni na san yadda zan ji da komai”.
“Okey, to shi kenan, ni zan tafi”.
Ya sake qanqame ta.
“me ki ke nufi, haka za ki tafi ki bar ni?”
“Na ga kai ma ya ba wannan ce ta kawo ka ba”.
Ya sanyaya murya cikin salon yaudara.
“Kin sani duk yanayin da nake ciki da zarar na ji ki a jikina na kan ji sanyi, bana iya jure rashinki, don Allah kada ki yi min xangwalilliya”.
Ta daddage ta tankaxa shi, “Ba za ka samu komai ba yau ko da na amince da kai babu abin da zan xorar, ni kuma ba zan yi abin da zai