Showing 9001 words to 12000 words out of 27791 words
Chapter 4 - ZARINAT (زرينة) book 1 free page's by zainab dodo.pdf
ya laluba ya kunna dim light, tashi tayi zaune ta fara cire masa botiran rigarsa ya taya ta,
ta cire rigar itama ta cire tata takoma daga ita sai pant, bakin su ya had'e waje d'aya suka shiga
tsotsar bakin juna, hannun sa yakai tare da cafkar breast d'in ta tayi wani irin nishi romantic d'in
junan su suke sosai
Tashi d'aya ya samu hanyarsa, yayi mamaki matuk'a kuma bai sha wata wahala wajen shiga ba,
'Bangaren husna kuwa itama bata sha wata wahala ba sai dai tad'an ji zafi lokacin da zai
shigeta, itama tayi mamakin jin bata ji zafin da ake fad'a akwai ba, tasan d'ah namiji bai ta'ba
sex da ita ba iya kajin ta da maza romantic ne bata ta'ba yarda wani yayi sex da ita ba
Firgit ta tashi daga baccin da ya d'auke ta tare da tashi zaune tana murza idanunta, agogon
dake manne a d'akin ta duba taga k'arfe uku har ta gota, ta sauko saman gadon ta bud'e ledar
da yah ansar ya ajiye mata, taga kaji ne guda biyu a ciki sai yogurt shima biyu d'auka tayi ta fito
tayi kitchen ta bud'e fridge ta saka ruwan da tagani a ciki ta d'auka har sun fara k'ank'ara ta
koma bedroom ta ajiye ruwan gefen gado ta shiga toilet tayi tsarki tare da d'auro alwala tazo ta
shimfid'a sallaya tayi nafila raka'a hud'u tayi addu'oin ta ta Mik'e ta nufi akwautunan ta na lefe ta
bud'e ta sleeping dress ta ciro wasu riga da wando masu had'e da hula yellow ta aza saman
gado ta koma toilet tayi wanka ta fito d'aure da towel, cikin k'ank'anin lokaci ta shirya ta haye
gado taja bargo sai bacci
Yah ansar kwance fuskar sa na kallan sama, kan husna saman k'irjin sa ta wani k'ank'amesa,
fuskarta ya shafa ta d'ago tana kallan sa yace "Muje muyi wanka" fuska ta yatsina tare da fad'in
"Wallahi zafi nake ji a gabana" Ayyah sorry sannu muje idan kika shiga ruwan zafi ko zai rage "
To amman sai dai ka d'auke ni dan inaga harda tafiya bazan iya ba" bata ko ida rufe bakin ta ba
tayi ya tallabeta suka nufi toilet, ruwa ya had'a mata masu d'an zafi ya sata a ciki, sai narke
masa takeyi shi kuma abun har yad'an fara bashi haushi yadai danne dan shi baiga wata
wahalar da ya bata ba dahar take masa haka, ya cigaba da fad'a mata "Sannu" sukayi wanka
sannan yace suyi na tsarki yah ansar tsinkewa yayi da lamarinta dan tsaye tayi ita harga allah
bata san yarda ake wankan tsarki ba, ganin dagaske take yasa yace tayi duk abinda taga yayi,
da haka dai itama tayi, bayan sunyi yace ta sakeyin wani dan ya tabbatar da idan ta iya yanzu,
sake yi tayi ba laifi ta iya yanzu suka d'auro towel suka fito
Suka saka kayan su, agogo ya duba yaga hud'u tayi dan haka ya fasa kwanciya yaje ya d'auro
alwala yazo ya kabarta sallahr lafila, husna kam gado ta haye nan da nan bacci yayi awon gaba
da ita
"Abban humaira wallahi yau jin nake kamar kayi zamanka mu kasance a tare basai kaje kasuwa
ba" Hhhhhhh maman humaira kenan idan banje kasuwar nan ba akwai matsala"To shikenan
ubangiji allah ya dawo min dakai lafiya allah ya kawo kasuwa mai yawa mai albarka "Amin
amin, har yayi gaba yad'an dawo tare da fad'in"kinga har na manta kema kuma baki tuna min
ba ko kin fasa zuwa kitson ne?" Aah na sha'afane nima"To ai kinga gwauda da na tuna "Ya fad'a
tare dasa hannu aljihu ya ciro kud'i
Yace"Nawa ne?" Duk abunda allah ya hore"Dubu da d'ari biyar ya kawo hannu zai Mik'a mata
har zata kar'ba gani kawai sukayi inna tazo kamar wacce aka koro da gudu tasa hannu ta kar'be
kud'in har na ga hannun sa tace " Wai kai wane irin sakare ni bakasan kud'i al'aura ce ba ba'a
nunasu gaban mutane bare kuma matar ka yanzu wad'an nan kud'ad'en har dubu da d'ari biyar
duka na kitso ne kawai ehhh lallai dole ne tunda kana tsoron kazo jan ruwa ta hana ma idan ba
haka ba taya zaka bata har dubu da d'ari biyar wai na kitso"Haba inna wallahi ba haka bane
kinga unguwar da zata je nisa ne da ita a k'allah cikin ma an maka sauk'i a kaika d'ari uku to
kinga zuwa da dawowa d'ari shida cikin naira dubu sauran d'ari hud'u kinsan mata ba'a rabasu
da y'ar ciye ciyen kaulama sauran d'ari hud'u sai tayi amfani dasu d'ari biyar kuma ta bama mai
kitson" Ahhh lallai to sannu alhaji ke"inna ta fad'a tare da Mik'a ma fatima d'ari biyar tace kar'bi
"Wannan ta isa ki bama mai kitson d'ari uku ki samu abun hawa ki talla'basa ya kaiki d'ari biyu
ga dawowa kuma ki dawo k'asa wallahi tafiyar k'asa ma tafi dad'i ki wana jinin jikin ki ki k'ara
samun lafiya " sauran naira dubu inna ta soke ta gefen zanen ta, ta lissafa kud'in da ta kar'be na
nasir taga dubu takwas da d'ari biyar ne ta cire dubu biyu da d'ari biyar ta Mik'a masa sauran
tace"Kar'bi maza boye ba'a wasa da kud'i kud'i al'aura ne " kar'ba yayi yasa aljihu har ga allah
abun da Mahaifiyar sa ke masa yafara isar sa sai dai ba yarda zai yi, fuskar fatima ya kallan
tare da yi mata magana da idanu d'aki ta shigewar ta yace sai na dawo"To allah ya bada sa'a
adan sayo muna abun motsa baki
Fatima jin ya fita yasa ta fito tayi hanyar d'akin inna tare da kiran ta ta fito "Lafiya?" D'ari biyar
d'in ta Mik'a mata tare da fad'in "Gashi ki k'ara kiyi abunda zakiyi" tana fad'in haka ta juya tayi
d'aki, inna tabi bayan ta da kallo tare da ta'be baki ta shige d'aki.............................................
*Hohohooooooooooo akace wasu kayan sai amale hajiya kina da labarin maman afnan kuwa?*
*Shahararriyar likitar nan wato maman afnan da tayi fice wajen ganin ta gyara zaman takewar
ma'aurata*
*Hmmmmmm to idan ma bakyada labarin ta to yanzu kin sani likitar mata ce da tayi fice wajen
ganin ta inganta zaman takewar ma'aurata yarda zaku zauna lafiya keda mai gidan ki da izinin
allahu mai gidanki zai ji dad'in zama dake har yaji baya sha'awar ko wace mace face ke*
*Ga neman ka'rin bayani zai iya tuntub'arta ta wannan number kamar haka *
*09039506644 or 09133559099*
*Maman afnan likitar mata ta k'aure wajen kawo muku kaya masu kyau da inganci kad'an daga
cikin kayakkinta sune*
*Tana gyaran amare ciki da waje*
*Had'in uwar gida*
*Had'in mai jego*
*Turaruka jiki dana kaya masu saukar da nishad'i*
*Maganin matsi, hajiyata ki matse gam_gam*
*Maganin sanyi*
*Maganin mallaka*
*Maganin farin jini*
*Maganin k'iba*
*Maganin hips, ki samu na juyawa mai house asamu na zama falo*
*Maganin breast, su ciko sosai su tsaya k'am*
*Maganin lalata sihiri*
*Takalmi*
*Ribon na gashi*
*Hulah & safuna*
*Mayafai, na yan k'aulisa*
*Kayan kitchen, da*
*Nesa tazo kusa kudai Kawai ku kasance tare da maman afnan in Sha Allah zakuji dad'in huld'a
da ita*
*Sanyen nagari maida kud'i gida*
Comment and share fisabillilah ♥️
ZARINAT ( ةنيرز )
Mallakar
Zainab dodo✍️
Maison magana dani zata iya tuntub'ana ta Wannan number
09046495943
Chart only
_____________________________
_______________
________
TASKIRA WRITER'S FORUM
T. W. F
Rubutu Baiwace Ga Wanda Allah Ya Baiwa Da Hikimar Mu Muke Alfahari
TASKIRA ASIRIN MARUBUTA
_____________________________
_________________
________
________
BISMILLAHI Rahmanirahim
________
Page 8️⃣
Kiran sallah da ake ne ya tadata daga bacci ta tashi zaune bakin ta d'auke da addu'a, sallahr da
taji ana k'ok'arin tayarwa ne yasa tayi saurin saukowa saman gado ta nufi toilet ta d'auro alwala
ta shimfid'a sallaya ta bud'e wardrobe ta d'auko hijabin ta ta saka har k'asa
'Bangaren su yah ansar kuwa, yana saman sallaya har aka fara kiran sallah ya tashi yaje yayo
wata alwala ya fito zai wuce masallaci ya tada husna dan tayi sallah yana fita ta koma baccin ta,
koda ya dawo ya tambeta tayi sallah tace,eh
Shima kwanciyar yayi suka ci gaba da bacci
Misalin k'arfe sha d'aya na rana bugun Kiran da ake masa ne a waya ya farkar da su,
Tashi yayi ya sauka saman gadon ya nufi inda wayar take, yana isa kiran na tsinkewa saiga
wani ya sake shigowa, sunan minal yaga na yawo akan screen d'in wayar, D'auka yayi
Daga d'aya 'bangaren akace "Yaya gani bakin k'ofa tun d'azu nazo ina ta kiran wayarka ba'a
d'aga ba "Okay ina zuwa"ya fad'a tare da kashe kiran
Ya kama hanya zai fita " Dear ina zakaje?" Minal ce tazo tana waje "Okay"
Bud'e mata yayi ta shigo hannun ta d'auke da basket, gaidasa tayi tare da tambayar su zarinat
suna lafiya, ta Mik'a masa sukayi sallama ta wuce, kulolin abincin guda hud'u ne dan haka ya
cire guda biyu ya nufi d'akin zarinat dasu ya kai mata, da alama ma bata tashi ba dan haka kai
tsaye ya nufi bedroom d'in ta, hangota yayi kwance tana bacci screen d'in wayarta dake kusa
da ita yaga yakawo haske,
tsaye yayi yana k'are ma surar jikin ta kallo tun daga sama har k'asa, kayan baccin dake jikin ta
sun masa kyau sosai, gasu irin wad'an nan ne na roba wad'an da ke mannewa a jikin mutum,
juyawa tayi cikin baccin ta basa baya, saurin d'auke idanunsa yayi a kanta ganin yarda
mazaunanta suka fito sosai cikin wandon, gefen gadon ya nufa ya ajiye kulolin, hannu yasa ya
janyo wayar ta data haye wajen juyi, har yanzu screen d'in da haske dubawa yayi yaga karatun
k'ur'ani ne take yi, bacci ya d'auke ta,
Danna power yayi ya kashe wayar ya aza mata ita saman drawer sake kallan ta yayi tare da
sakin murmushi wanda shi kansa baisan yayi ba ya wuce
Yana fita tana bud'e ido, k'amshin turaren sa da taji ne yasa ta tashi zaune tare da dube_dube
idanun ta suka sauka akan kulolin da ya ajiye, wanda ya tabbatar mata daya shigo d'akin ne
Saukowa tayi saman gadon ta bud'e kulolin, d'aya dankalin turawa ne da kwai d'aya kuma
dafaffiyar kaza ce, rufewa tayi ta gyara gado d'akin baiyi datti ba amman sai da ta d'auko
mashari tad'an sharesa sama_sama ta kunna turare sannan ta fad'a toilet
Nasu abincin ya d'auka ya nufi d'akin husna, tana nan zaune saman gado saima wayarta data
janyo tana charting, ganin sa yasa tayi saurin kashe wayar tare da fad'in " Abinci ne aka kawo
muna?" Eh ki tashi kije kiyi wanka sai mu ci "okay,ta fad'a tare da sauk'owa tayi toilet shima fita
yayi ya nufi d'akin sa
Zarinat, wanka tayi ta had'e cikin wata atamfa d'inkin doguwar riga, tayi d'aurin ture, ta gyara
face d'in ta, sai lipgloss d'in da ta shafa ta saka awarwaro masu kyau sai k'amshi take zubawa
tayi kyau sosai, ta d'auko kulolin abincin ta yo falo ta nufi dinning table ta ajiye taje ta d'auko filet
ta zuba iya wanda tasan zai isheta ta d'auko ruwa tayi zaune ta fara cin abincin ta
Wanka yayi ya shirya cikin wani yadi mai fari mai kyau kallo d'aya zakayi ma yadin kasan na
manya ne, an masa d'inki mai kyau na zamani, k'amshin turaren sa keta tashi, ya nufi d'akin
husna, tsaye take gaban mirror tana gyara d'aurin da tayi, tana sanye cikin kamfala d'inkin bubu
ta zubo kitson nan na attach a baya tayi kyau abinta
Murmushi ta sakar masa shima ya mayar mata, takawa tayi har inda yake ta mak'ale hannun ta
a kafad'arsa " Dear" uhm "Banyi kyau bane"Kinyi mana sosai "ya fad'a tare da k'ara matsota
jikin sa"Naji baka yaba ba "Uhm saurin magana ne kawai kika yi"dagaske?" Yeah" ya fad'a tare
da d'aga mata gira " To abani goron wannan wankan"Okay, ya fad'a tare da had'e bakin su waje
d'aya ya shiga tsotsa, sunyi wajen 5 mint suna tsotsar bakin juna sannan ya saki bakin ta tare
da fad'in " Muci abinci sai na baki babban goru" Murmushi tayi tare da shafo gemun sa
D'aukar abincin sukayi suka dawo falo...............................................
Comment and share fisabillilah ♥️
ZARINAT ( ةنيرز )
Mallakar
Zainab dodo✍️
Maison magana dani zata iya tuntub'ana ta Wannan number
09046495943
Chart only
_____________________________
_______________
________
TASKIRA WRITER'S FORUM
T. W. F
Rubutu Baiwace Ga Wanda Allah Ya Baiwa Da Hikimar Mu Muke Alfahari
TASKIRA ASIRIN MARUBUTA
_____________________________
_________________
________
________
BISMILLAHI Rahmanirahim
________
Page 9️⃣
Abinci suka ci suna gamawa suka koma bedroom suka fad'a duniyar ma'aurata, yin ranar duk a
d'akin husna yayi shi kiran sallah kawai ke fitar dashi yaje yayi sallah, ita kuma daya fita ta
d'auro sallaya ta shimfid'a ta saka hijab ta d'auko waya tayi zaune tana charting da yan
samarinta ba tare da tayi sallahr ba, koda zai dawo masallaci ya tarda ta zaune saman sallayar
duk a tunanin sa tayi sallar ne ta zauna tana lazumi
Ammi ta aiko musu abincin rana dana dare
Yau sati d'aya da auren su, amman tun ranar da ya shiga 'bangaren zarinat ya kai mata abinci
ya sameta tana bacci har yanzu bai sake shiga 'bangaren nata ba kuma bai sake ganin ta ba,
saboda minal ke kawo musu abinci sai ya d'auki nasu ya Mik'a mata na zarinat ta kai mata
Soyayyar su suke sha sosai shida husna suna gurzar amarcin su yarda ya dace
Husna tuni tasa Mahaifiyarta ta nemo mata yan aiki wand'an da zasu rik'a yi mata girki da
gyaran d'aki
Sai dai basu fara girki ba saboda ammi ke aiko musu abinci gyaran d'aki kawai suke yi
Yau minal bata samu zuwa ba aka bama driver ya kawo musu, bayan driver ya kawo ya wuce
yah ansar ya kira ammi tare da fad'a mata, ta bar girkin haka nan sun gode sosai, ammi tace to
shikenan daman na sati d'aya taso ta musu amman tunda yace tabarsa hakan shikenan
D'aukar nasu yayi yakai 'bangaren husna tana kwance tana bacci, ya fito ya d'auki na zarinat
yayi 'bangaren ta, murd'a hannun k'ofar yayi ya jisa a bud'e ya tura tare da yin sallama ya shiga,
Yana tura kansa wani irin ni'iman taccen k'amshin turaren garwashi ne ya ziyar ci hancinsa sai
da ya lumshe ido ga sanyin AC daya ratsa sa, kwance take saman had'ad'd'un kujerun ta na
alfarma mai mazaunar mutum hud'u, idanunta na ga TV da ta kunna tana kallo amman kallo
d'aya zakayi mata kasan hankalin ta baiga kallon ta fad'a duniyar tunani ne, tana sanye cikin
wani material yellow d'inkin riga da siket irin d'inkin nan na dai_dai jikin ka wanda za'a fito maka
da shape d'in jikin ka sai yan kunnen sarkarta ta gold da tasaka, bata son sark'a shiyasa bata
cika sakata ba sai dai idan ta belo mata wani lokacin ta saka, hannunta kuma sanye da wani
awarwaro mai kyau sai kyalli yake yi, tayi kyau sosai
K'afafuwan ta yake kallo k'unshin da akayi mata wanda ya fara gogewa sai ya bada wata kala
mai kyau,
Dogon numfashi taja tare da rufe idon ta ta sake bud'ewa k'amshin turaren sa taji duk ya
mamaye hancinta ta d'ago kanta tana dubin hanya had'a ido sukayi ta tashi zaune, d'ankwallin
kanta ya Fad'i gashin ta ya bayyana, "Ya salam" yah ansar ya fad'a lokacin da ta Mik'e zaune
ganin yarda breast d'in ta suka cika tam kamar zasu fasa rigar su fito duk sun bullo ta saman
rigar
D'ankwallinta ta d'auka tare da aza d'ankwallin a kai yarda ta d'ora sa saima yafi mata kyau bisa
ga d'aurin da tayi
K'arasowa yayi wajen ta tare da ajiye kular hannun sa ya zauna saman kujerar da take zaune,
sauka k'asa tayi tare da duk'awa cikin girmamawa tace "Yaya ina wuni" Lafiya k'alau, ya fad'a
murmushi d'auke akan fuskarsa yace "Fatan kina lafiya?" Alhamdulillah " Ma sha Allah, taso ki
zauna" ta fad'a yana nuna mata inda ta tashi
Ba musu ta tashi ta zauna, dukan su shuru sukayi saima shi da ya mayarda hankalinsa kan TV
ita kuma kanta a k'asa tana wasa da awarwaro dake hannun ta
" Tunanin me kike yi?" Taji ya jefo mata tambaya, d'agowa tayi ta kallesa taga fuskarsa nakan
TV sake duk'ar da kanta Kawai tayi taci gaba da wasa da awarwaron
Juyowa yayi ya kalle ta tare da kallan hannun ta da take wasa dashi " Tunanin me kike yi?" Ya
sake tambayar ta
Ahankali ta furta "Ba komai" ba tare da ta d'ago kanta ba "Bakomai zan shigo tayi ta sallama
amman bakiji ba" yayi maganar tare da k'ara gyara zaman sa yana kallan ta, shuru ta masa
batace komai ba ganin bata ce komai