Showing 1 words to 3000 words out of 39554 words
[05/05, 8:53 PM] UMMU AFAN :
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION
(F.C.T.W.A)
HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Hauwa'u idris ( maman daddy )
Allah yabar zumunci inajin dadin comment din ki Allah yabar kauna keep it up
AKWAI lokaci
PAGE 101to105
PROF yashigo direct dakin amaryar ya wuce sai yaji kofa gam
Kuma gashi bashida spire key
Duk guda hudun suna hade da juna
Ya koma dakinsa yayi wanka
Ya koma kan bed dinsa yadauki waya
Yasoma dialing din number husnah yayita ringing
Husnah bata daga wayar ba
Prof yayi mirmushi Wanda shikadai yasan abinda yasashi murmushi
Ya rufe ido Dan bacci amma bacci yace baisan zancenba
Yadauki wayarshi kawai yakira Ahmad
Saida yakira Ahmad sau biyu kafin ya dauka
Ahmad yace kai ango yadai kira da wannan lokacin
Hakeem yace kai dai bari wallahi man
Wallahi yarinyar nan ta kulle min kofa
aikafin yakai karshe Ahmed yafashe da dariya sosai yayi dariyarshi
Kafin yace amma wallahi husnah ta burgeni
Sosai
Hakeem yace Dan iska dariya zaka min ko
Ahmad yace aikaine abokina duk kabi ka tsorata masu yarinya aidole ta kulle kofarta
Dan batasan mezaifaruba idan akabarku Ku biyu
Hakeem yayi murmushi yace duk tagama buyanta badai ta shigo hanu ba
Zanbata mamaki zata shigo hanu ai
Ahmad yace wallahi dai kabi yarinyar mutane a hankali
Bafa babbar mace bace
Dan nasan kasaba da manyan mata
Yayi dariya yakashe wayar shi
Hakeem cikin murmushi yabi wayar da kallo
Yace zanrama ne
Kafin yakoma amma bacci fa yaki Sam
Daya rufe ido zaiga husnah alokacin da yake kissing dinta
Sai yayi murmushi ya rungume pillow kawai bacci yayi awun gaba dashi
Laila duk abinda kefaruwa tana lebe tana gani aikuwa ganin Hakeem ya burda kofa yaji akulle
duk ta gani
Har wayan dasukayi da Ahmad taji aikuwa cikin farinciki ta koma part dinta ta sanar da su
hajiyarta da kanwarta suby
Dan basu komaba ita suby auran nata ya mutu shiyasa zata zauna gurin Laila
aikuwa cikin farinciki hajiya rukayya tace aikin banza Ashe ma duk abinda suke yarinya bata so
Suby tace a a karku manta dama boka yace zai sa gaba a tsakaninsu
Watakila aikin ne boka ne yafara aikitakanta
Inbahakaba wazaiki yaya Hakeem a matsayin miji
Hajiyarsu tace tabbas maganarki hakatake
Kunga ganiba gwamma da muka sake mishi kudi gashi anfara aganin cigaba
Laila dai da farin ciki ta kwanta abinta zuciyarta fati kal
Karfe hudu dai dai na asuba Husnah tafarka cikin nannauyar baccin da ya dauketa
Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi kafin tayi nafilfilunta kamar yarda tasaba ana kiran sallar
asuba tayi sallarta tayi adduointa da karatun alkur'ani
Kafin tacire kayan jikinta Dan jiya bata samu daman cire kayan ba saboda gajiya
Tashiga wanka kafin tafito
Spray kawai da shuwa tashafa sleeping dress tasaka duguwar riga abinta tafada gado abinta
Sosai taji dadin baccinta Hakeem bayan yadawo daga sallar asuba yasake tana dakin husnah
shiru bata budeba
Direct dakinshi ya wuce dakinsa
Shima baccin yakoma
Karfe bakwai da rabi dai dai mai aikin mummy ta buga kofa
Suby kanwar Laila ita tabude kofar
Taga me aikin mummyn Hakeem ce
Tace sannu suby ta yatsina baki yadai ina zaki da basket din abinci haka
Tace hajiya ce ta aikeni nakawo ma amarya abin karyawa
Suby ta kebe baki tace to aikuma basu tashiba amma kawo saina na mika mata
Tabata abincin
Suby ta karba tashige dashi part dinsu gurin su Laila da hajiya rukayya
Laila cikin murna tace yauwa suby dauko maganin a side drawer kikawo
Aikuwa haka suka barbade komai da maganin nan
Farfesuf na kayan ciki sai kunun gyada da kosai
Kai kuma farfesun ganda Wanda yasha kayan hadi sosai
Haka suka bikomai suka badeshi tas
Hajiyq rukayya tace maza ke suby tashi kikaimata
Laila tace abarta ta kai Dan tanason ganin amaryar
Hajiya rukayya tace a a idan kika kai dakanki za azargi wani Abu
Zakiganta ai mudai burinmu kawai tabar gidan
Suby tace wallahi nimafa basanin amaryar nayi bama dan haushi
Husnah cikin bacci taji ana buga mata kofa ta tashi tayi hanyar falonta
Tayi kofa tabude sukayi ido hudu da suby
Suby sai tadauka kaman gezo idonta suke mata wannan irin zukekiyar yarinyar kuma daga ina
Husnah ta ce sannu suby tace ina antyntaki
Husnah ta yatsina fuska tace antyna kuma
Suby tace ina nufin amaya
Husnah tayi murmushi tace OK ai tashiga wanka
Tana ganin suby tasauke ajiyar zuciya
Husnah ta kibata hanya kuma
Suby tace ga shi inji hajiyar yaya Hakeem akawo mata
Husnah tace OK angode barin kaimata
Suby ta mika mata basket din husnah tarufe kofarta
Murmushi husnah tayi ta ajiye basket din ta ajiye kan dining kafin ta koma kan bed koma bacci
Sai karfe goma dai dai ta tashi
Ta gyara bedroom dinta da falonta ta badeshi da kamshi
Ko ina yadau kamshi kafin tashiga bathroom tayi wanka tafito ta shirya cikin wani tsadaddar
super Holland dark blue sai adon pink ajikinsa
Yadda dinkin yazauna ajikinta shizaifi Baku sha'awa sosai das yamata dinkin ma kawai a in
kallone
Matsalarta daya bata son dankwali ta tace gashinta takama da ribbon pink
Kafin ta murza daurin Dan kwalinta abin wuyanta ma pink ne
Gaskiya husnah tayi kyau matuka
Tadauki ta kalminta plate shoe tasaka
Har ta zauna zatafara break fast saikuma taga rashin dacewar hakan
Bata je tagaida mummy ba
Gyalenta tadauka maishegen kyau tayafa
Pink colour
Tafita tayi hanyar kofarta tasaka key ta kulle
Bayan ta fita
Dama dole saitabi ta main falonsu gabadaya tana fitowa kuwa taga mutan gidan gaba dayansu
a falo
To itabasaninsu tayi ba
Ganin harda manya yasa husnah ta durkusa tana gaida su hajiya rukayya da kuma Laila
Laila ta watsa mata harara
Wai ita hakimar bata fitowa ne saike
Hajiya rukayya tace inazata fito ansamu duniya
An auri mekudi an asirceshi
Suby ta kalli husnah tace 'yar buzuwa kotafiya za ayi ne
Husnah ta kalleta tace inje ina ai munsamu gida nida antyna
Dan nadawo kenan gwamma muma muzauna muci arzikin Dan da alama bamu kadai bane 'yan
cin arzikin
Husnah tana gama yada musu magana tayi waje abinta
Har suby zata bita hajiya rukayya tace a a kyaleta kar ajimu tun yanzu mana
Laila race lalle ma Dan talaka be iya samun wuriba
Wannan zakewa haka harda dauko 'yar riko
To wallahi wannan yarinyar kamar aljana bazata tazauna min agida wallahi
Kalli yadda take tafiya kamar wata 'yar sarki
Hajiya rukayya tace aibakisan halin talakabakenan idan yasami guri
Kuma ke Laila da kike cewa bazata zauna ba yayar tata ma ba zaman zatayi balle ita 'yar cin
arziki
Nan dai suka muna funcinsu
Husnah tayi sallma a falon mumy shiru ba kowa
Ta nemi guri tazauna a tafkeken falon su mummy
Mummy ta sauko daga sama bata lura ba harzata shige kitchen
Husnah tayi saurin sauka kasa tace mummy ina kwana
Mummy hafsat tajuyo tayi tazali da surukar tata
Tace a a husnah ai ban lura bama meyasa kika zauna nan baki haura saman ba saikace
bakuwa
Husnah tace bakomai mummy nan ma yayi
Mummy hafsat tace a a nan gidanku ne ko ina zakishiga
Kina da damar hakan kinjiko
Ya bakunta husnah tayi murmushi kawai batace komai ba
Mummy tace kinci abinci ko husnah tace yanzu zanje nayi
Kafin mummy tayi magana Abdul Hakeem yayi sallama yashigo wata tsadaddiyar shadda milk
colour sai wata hadaddiyar hula da ya murza akansa Wanda yasake fito da kyakkawar
fuskarshi mai kewaye da kwantacen saje dayakarawa fuskar tashi kyau
Gaskiya PROF Fa kyakkawar mutumne bankarya
Yashigo idonsa yakai kan Husnah dake zaune kan kafet
Wani farinciki yaji sosai
Ya kalli mummy
Yace mummy na antashi lafiya
Mummy tace lafiya kalau son maza kuwuce dining kawai kuyi break idan kungama kukirani
zanje nayi salar walha
Hakeem yace angama dalibata
Mummynsa tayi murmushi tace a a tun yaushe daliba ta canja malami ai
Hakeem yace amma tunda yanzu nadawo gida
Sai kisake sayan form agurina Husna da mummy sukayi murmushi
Mummy tace kaga idan nabiye maka sai lokaci ya wuce banyi sallar ba
Ta kalli husnah tace 'yata tashi kije dining kinji kikarya abinki kinji
Ina zuwa yanzu
Mummy tayi sama tabarsu anan
Hakeem yakure wa husnah ido yace wana kama
Husnah ta saukar dakai kasa
Hakeem shima zamayayi shima tabayanta yakamota yasakalo Kansa tagefen wuyarta
hanunshi yakai cikin rigarta ta yashafo cikinta
Yace bakice abinciba baby jicikinki fa kaman zai hade da baya
Itadai husnah wani iri takeji tabatan dayakeyi
Yace tashi muje nabaki abinci banason musu
Cikin shagwaba husnah tace ni anan zanci ba a dining ba
Prof yace angama baby dakanshi yatashi yakawo musu komai plate daya yazuba musu
Yace oya bude bakin bayan yadauko kofin kunun gyada tace dakaina zan sha kabari kawai
Yace bason musu fa
Badan tasoba tabude baki yabata
Nan yabata farfesun ma kosai da duk wani abin dake gun saida yashiga cikin husnah tace
mishi ta koshi yaki
Yace daman ya shamsu yamishi bayanin bata cin abinci
Cikin shagwaba husnah tace wallahi inaci kuma nakoshi sai da yaga tana shirin dawo Dana
cikin nata yabarta haka kafin shima yafara cin abincin
Bayan yagama ne yasa hanu zai dauke tiren abincin husnah targashi yace yadai yakureta da
ido
Tace kabarshi kawai zankai
Bai hanataba husnah tadauka tayi hanyar datake tunanin nan ne kitchen din
Tana zuwa ta ajiye a sink din wanke wanke ta wanke tas duk wani abin da za a wanke saida ta
wanke
Shikuma prof be biyo sa wuba saboda yana waya ne
Mummy tasauko daga sama tagashi shikadai ne a falon
Tace a a asmaun
Hakeem yayi sallama dawani abokinshi yace tashiga kitchen
Kai kwanuka
Mummy taleka kitchen dintaga ko ina tsaf an goge
Mummy tace kai haba husnah da kanki Aida kinbarima yanzu mai wankewar zatazo yau tayi
ranar dawowa ma
Husnah tace bakomai mummy
Mummy tace maza jeki huta kafin nafito
Husnah tayi murmushi tace
a a mummy meza adaura Dan naga kaman abinci kikeson daurawa
Mummy tace a haba dai daga zuwa harkifara shiga kitchen a a jeki huta
Idan kunyi sati saikifara dafa abincinki
Husnah tace mummy kigafarceni amma banzan taba zama inga kina shiga kitchen
Yakamata kema kihuta Dan Allah
Tunda na taso agidan mu Nina ke abinci umma ta na hutar da ita saboda haka Dan Allah
mummy kibari na ringa miki abinci kihuta kema kisan kinada yarinya a yanzu
Cike da mamakin kalaman husnah mummy tace lalle husnah kin haifu Allah ya wa iyayenki
albarka dasuka miki tarbiya maikyau
Nagode da kika daukeni matsayin uwa
Allah yabaku zaman lafiya keda mijinki yazaunar daku lafiya kinjiko
Husnah kai akasa tayi shiru
Mummy tace na'amince zaki rinkawa mummy abinci amma fa mummy ma tayi alkawarin satayi
sati kina cin abincin mummy kinjiko
Saboda haka kibar mummy tacika alkawarin ta
Husnah tayi murmushi kawai kafin tayi magana
Hakeem yayi gyaran murya mummy da husnah suka kalleshi
Mummy tace wato labe kake mana ko
Hakeem yayi murmushi yakaraso cikin kitchen din
Yakama hanun mummy yace haba mummy please kibar yarinki tasamu ladarki
Allah ne ya amsa adduarki yakawo mana husnah cikin rayuwar mu
Kinji mummyna
Mummy hafsat tayi murmushi tace shikenan tunda kunmin yawa Allah yayi albarka
amma bayanzu za adaura abinciba sai yamma idan anyi la'asar
Yanzu muje kawai muyi hirar mu
Mummy taja hanun husnah wacce tunda Hakeem yashigo takasa magana
Ranar dai a sashin mummy husnah ta wuni sai da ka kira isha tabar dakin mummy ganin
Hakeem da daddy sunfita sallah
Mummy tace yau husnah Allah yatashemu ki huta gajiya ko
Ita mummy a tunaninta husnah zata je tashirya ne kafin mijinta yasameta
Husnah kuwa tashiga falon taga Laila da suby a zaune
Ta wuce abinta batareda ta kalli kowa ba
aikuwa suby tace ke zonan
Kojuyowa husnah batayi bare ma tasan da ita sukeyi
Ke 'yar talakwa bakiji menace bane husnah tayi banza dasu kafin suby ta karaso husnah
tashige ta banko kofarta tasaka key
Direct wanka tafara kafin tayi sallah tayi karatun ta data saba
Suby tace anty anya kuwa ba wannan aljanar yarinyar bane kishiyarki kuwa
aikuwa jitayi Laila ta zabga mata mari
Suby tace mena miki anty Laila
Cikin tashin hankali Laila tace damme zaki min wannan mugun fatan
Taya za ayi yaje ya auro 'yar cikinsa
Bama hakaba idan yakasance wannan yarinyar ce ai yayi abinkuya
Nikuma nashiga uku taya zafara kishi da wannan yarinyar
Suby tace aiko dai koki kokiso itace
Dan agabanki tasa mukulli ta bude sashinta kuma dazu Dana kai mata abincin ma ita nagani
kawai raina mana hankali take
Laila ta daura hanu akai tace nashiga uku ni Laila wannan ai inaganin ko meenat ma ai tagir
meta
Lalle Hakeem yacuceni
Yanzu sakayya da zaimin kenan ya auro 'yar cikina inyi kishi da aita ina Sam bazaiyuba wallahi
Suby tace wallahi idan kika bari aljanar yarinyar tazauna agidan nan
Zikidawo jaka wallahi Dan abinda kike samu bazaki samu ba
Yarinya kaman ita tayi kanta Dan kyau tahada komai da d'anamiji yake bukata
Laila tace ya isa haka suby zakisa zuciyata tafashe kibarni naji da Abu daya Dan Allah
Hakeem yashigo falon da sallama Laila ta taso sannu da zuwa baban meenat
Hakeem yace yauwa yashige bedroom dinshi Dan karya taba kofar husnah yaji akulle agabasu
su fahimci wani Abu
Laila tabishi har yafito Daga wanka yana yashirya ya kwanta
Laila taga bashida niyar kulata yasata ce baban meenat har yanzu fa bansan kanwartawaba
Sai kanwarta muke ta gani tana shige da fice
Hakeem yayi murmushi Dan ta tabo inda yake mishi kaikayi
Yace kanwa kuma ai bata da kanwa itadai wacce kikagani din itace amaryata
aikuwa Laila ta tashi tace amma wallahi kaji kunya Hakeem yanzu da girman ka da darajarka
zaka auro 'yar cikinka wannan ma ai zubda mutuncin Kaine da zubar wa 'yarka da mutunci
Prof baki kawai yasake kallon ta
Yayi murmushi yace kinyi sake maman meenat da kika auri mijin asmau saboda yanzu nasan
nima namijine kuma na auri dai dai Dani kije aduba miki nidake bamu taba dacewa ba kuma
bazamu daceba
Meenat da Allah yabani na karba kuma inason 'yata
Idan tazo ruwantane taso matata ruwantane takita
amma zanfada miki wannan Kalmar mummy da daddyne kawai bazan iya rabuwa dasu ba
saboda husnah
Amma bayansu zan sabama kowa akan matata so get out of my room
Cikin tashin hankali Laila tafito Daga bedroom din Hakeem
Kuka sosai taci suby nabata hankuri
****
Bayan sati uku Hakeem ya Dade da komawa aikinsa gashi aikin yamishi yawa ga kullum
tunanin husnah ne da sha'warta acikin ranshi
Ba inda yake samun ganinta sai a part din umma Dan Anna take wuninta
Tana fita sallar isha zata gudu
Hakeem zaune kan kujerar office dinsa Ahmad kuma yana cike wani file's
Ahmad yace yauwa kagani ko yana nuna wa Hakeem abinda yacike