Showing 30001 words to 33000 words out of 39554 words

Chapter 11 - AKWAI LOKACI Book 2 end BY UMMU AFAN .pdf

02 Jul 2025

2114

🖊🖊🖊🖊🖊🖊📚



�FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION�


�� (F.C.T.W.A)��



�HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION�




🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MAMAN MUFIDA
Ina alfahari dake wallahi kina kasheni da wannan nice comments din naki Allah yabar
kauna🎗😘😘😘😘😘






🎗AKWAI LOKACI 🎗




🎗PAGE 153 to 155🎗

YA SHAMSU yace inajinki honey

Kubra tace wallahi inasha awar naga yara agidan
Koda kuwa bani zan haifesu ba inason ganinsu

Ya shamsu yace bangane mekike fada ba kubra


Kubra tace nazauna nayi tunani
Halaccin da kukayi min a rayuwa Dan me nima bazanso abinda zai faranta ran ka Dana su
umma ba


Wallahi koba afadamin ba nasan yadda kakeson yara
Koba kaiba ma su umma fa girma ya kamasu zasuso suga yaranka kafin sukoma ga
mahallincinsu


Saboda son dasukeyi min da nuna kulawa agareni yasa bantaba jin umma tayi magana akan
rashin haihuwataba

Kuma nasan dole abin zai dameta

Kaga idan har nacika masoyiyarka ta gaskiya dole ne nayi kokarin ganin farin ciki arayuwarka
idan har INA da damar hakan


Ya shamsu yace duk meyakawo wannan maganar kubra mekike nufi kenan


Kubra tace ina nufin kayi aure Dan Allah muna bukatar muga yara acikin gidan nan
Dan Allah karki yadda da bukatuna
Kayi tunani mai kyau akan magana bakai zaka duba ba su umma zaka duba



Ya shamsu Wanda mamakin kubra yakeyi tubaran
Yace anya kina cikin hankalinki kuwa kubra
Meyasameki

Bantaba ganin macen datake jawa kanta kishiya ba saike
Kokuma kindaina sonane yasa kike fatan nakawo wata cikin rayuwarmu


Please banason sake jin wannan maganar a bakinki Dan Allah bana samum sabani dake amma
akan wannan zan baki mamaki


Kubra tasauka kasa tazuba gwiwarta akasa tana kuka tana rokanshi akan yacika mata burinta

Yaga abin nata ma dagasake ne yafita daga dakin yakoma dayar dakin yasaka key


Kubra kuwa ganin yabar mata dakin
Yasa tama rasa tunanin dazatayi


ahaka bacci yadauketa rana nafarko dasuka fara raba shimfida kenan da mijinta


Washagari da safe bayan sungama karyawa meenat tace zata ta kwanta Dan tana komawa
baccin safe falon yarage daga husnah sai umma sai anty kubra


Umma ta lura da kubra yau kaman bata lafiya takasa yinshiru tace khadijah lafiya kuwa

Kubra tayi murmushi tace umma ina da magana amma keda Abba nakeson magana daku

Umma da husnah suka kalli juna Dan basu taba ganin kubra cikin wannan halin ba


Umma tace to kutashi mutafi can falon abban naku sai kiyi maganar acan


Tare umma da kubra suka wuce sukabar husnah da damuwar rashin sanin maganar da kubra
zatayi

Can husnah tace kodai fada sukayi da yaya shamsu
Tace haba ya shamsu me anty kubra zata maka da har zai kasata adamuwa irinhaka

Haka ta tashi ta wuce part dinsu anty kubra tanazuwa tasamu ya shamsu a falo yana kwance
fuskarshi nakallon sama husnah tashiga


Husnah tayi sallama ya shamsu ya amsa tare dayin yaken dole

Husnah tace ya shamsu wai meke faruwa kaida anty kubra ne

Yatashi da sauri yace tafada miki wani abunne

Husnah tace a a amma yau bata cikin walwala kuma tace tanada magana da Abba

Ya shamsu yace ita kubaran yanzu tana ina husnah tace suna falon Abba

Dasauri ya shamsu yafita yayi hanyar falon Abba yanazuwa yace kubra wai meyasa bakya jin
maganane Dan Allah


Abba yace karaso mana ubana yafi nakowa sham sudden
Ya shamsu yashiga yasamu guri yazauna

Abba yayi gyaran murya yace matarka tasamemu da wata magana wacce da bamu amince da
itaba sabida ganin rashin dacewar hakan amma kuma tafimu hujja da da dalilu masu yawa




Ya shamsu yadaga kai yace Abba yanzu inbanda shirme irin na kubra ta ina zanfara Neman
matar aure


Abba yace ai har matar ma tariga tasama maka ita

Dasauri yadago kai yakalli kubra wacce tamaida kanta kasa


Yace bangane tasamamin matar aureba
Abba yace wannan yarinya amina

Ya shamsu yace amina kuma wacece wannan kuma

Husnah dake bakin kofa tace meenat kenan

Duk suka kalleta anty kubra tace a itanake nufi
Na tabbatar a yanzu duniya ta mata karatun tanutsu zata zauna lafiya


Kuma meenat bakowa takeso sai yayanki
Tana son ya shamsu kobadan itaba ai zamu duba babanta da kakaninta tashiryu duk abinda
tayi da ina da tabbacin yarinta ce amma yanzu hankali yazo mata Dan Allah ke ma husnah
kifahimce ni



Husnah tace yanzu anty kubra dakanki kikeson janyo meenat ajiki bayan munsan ta musan
halinta

Anty kubra tace sanin da kika ma kuma kema na San kinyarda meenat ta canja

Abba yace duk kuzauna mufahimci juna

Nan Abba yayita musu nasiha
Sannan kuma yanuna musu faidar yin abinda kubra tace


Umma tace gaskiya khadija samun mace irinki awannan zamani maison farinciki Wanda take
taredashi koda ita zata rasa nata farincikin

Kai kuma shamsu idan wannan aure dazaka yi zaisa kubra tayi farinciki to kaje kanemi auran
amina


Abba yace wannan banyarda kabata wa kubra ba shamsu a rayuwar ka mace ce tagari
Wacce samun irinta a rayuwa sai antona


Kubra tace nagode dakuka fahimceni

Abba yace Allah yamiki albarka yabaku masuyi muku abinda kukamana

Anty kubra ta tashi tafita

Abba yakai kallonshiga shamsu dayayi suman zaune

Abba yace abinda yakamata yarinyar tayi a yanzu tabbas lokaci yayi dayakamata karamawa
kura aniyarta ba abinda zamuce ga wannan yaro Abdul Hakeem da iyayensa saidai Allah

yasaka musu da gidan aljanna


Kaduba yadda suke kula da 'yar uwarka ba abinda tanema tarasa


Baka tunanin hanyar dayakamata kaima kamishi wani Abu dazaiyi jidadi a rayuwarshi


To Allah ne yabaka damar dazaka sakamasa shima shine ka auri yarinyar nan amina kariketa
kamar yadda yake rike maka naka 'yar uwar


Nan dai su Abba sukayi ta fahimtar dashi faidar yin hakan




Da daddare kubra da yashamsu sunyi shirin kwanciya

Sunkwanta kubra kallon kayan da akaturo mata nasiyarwa ne wata kawarta ce take kawowa
daga Dubai

Ya shamsu yakarba yana kallo shima yace kai amma sunyi kyau wanne kikazaba


Kubra tayi dariya tace daga ganin Abu a waya kuma saina hau zaba kawaidai ita tafara
nunamin ne inga irin kayan data saro kuma nagani kaga nace mata ma sunyi kyau sosai



Yace hakane to ninace kizaba muku masu kyau keda asmau

Kubra tace a a fa wallahi bada niyar kasayamin nabude kaganiba kawaidai nabudene Dan
nasan ta turo sai dai nazabawa

Husnah dai tunda kayi niyya saya

Ya shamsu yace kizaba muku banason musu

Kubra tace to ai kabari muji kudinko
Ya shamsu yace bakyajin magana ko

Kubra tayi murmushi tace shikenan angama rankayadade

Saikuma tace muka saya mana kanwata fa meenat kagafa tunyanzu yakamata ka kafara
kwatanta adallcin fa


Ya shamsu yace yasalam kubra rigima wai ba anwuce wannan shafin bane


Kubra tayi murmushi tace yanzu aka bude shafin kuwa kasan fa jibi zasu koma gida yakamata
kagabatar da kanka agurin meenat


Ya shamsu yace Ashe kuwa saidai afasa kenifa barin fada miki wallahi bayadda na iya ne yasa
na amince muku keda su Abba

amma wallahi duk abinda yafaru dake zanyi kuka


Kubra tayi murmushi tace ba abinda zaifaruma sai alkairi


Yanzu dai mu uku zan zaba mana ko
Ya shamsu yakwanta yace yadda kikace

Murmushi kawai anty kubra tayi tace shikenan

Tace nazaba mana nida husnah katashi kazabawa meenat nata

Duk kubarshi amfasa indai nizan zaba mata

anty kubra ta kunshe dariya acikin bakinta Dan yadda yayi maganar yabata dariya




Husnah da meenat suna kwance sunyi shirin bacci

Husnah tacewa meenat duk da kinfada min Wanda kikeso yanzu idan Allah yacika miki burinki
kika aureshi Wanda kikeso yazakiyi wani irin tanadi kika mishi wurin faranta mishi

Meenat ta tashi tazauna tayi murmushi tace hmm wannan sirri nane tsakanina da mahaliccina

Dan Allah yaga niya ta akan shi idan Allah yacikamin burina Wanda banma taba mafarkin
cikansaba

amma wallahi Allah yasani inason shi sona hakika so mai tsabta


Husnah tayi murmushi tace Allah yacika miki burinki
Zaki auri Wanda kikeso meenat



Cikin tsananin mamaki meenat tace taya akayi kikasan Wanda nakeso bayan nasan banfada
mikiba


Husnah tace labarin zuciya a tambayi fuska kawata kuma nima antyna a yanzu

amarya agurin anty kubra mace daya tamkar yadubu
Mata agurin masoyinki ya shamsu


Meenat da mamaki take kallon husnah tace ya akayi kika fahimci asirin zuciyata


Husnah tayi murmushi tace karkidamu Allah dai yanuna mana lokacin


Ni husnah nafi kowa gata da samun matan yaya guda biyu masu sona Allah yabaku zaman
lafiya

Bana son tambaya bacci zanyi idan kika dameni zanfada wa dad dinki
Kin hanani bacci ta kwanta abinta tana cike da farincike



Meenat tarasa abinyi murna zatayi kokuma akasin haka
To kodai shima ya shamsun yanasonta ne kai a a akwai dai wani Abu



Kuma mai bata amsar taki fito da daita daga duhu

Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi tana Neman zabin Allah



Washagari da safe meenat takasa fita falo tayi takasa hada ido kowa inba husnah ba


Umma ana cin abincin rana
Anty kubra ta kalli husnah tace wallahi baki kyauta ba yanzu gashi kinsa tunsafe takasa fitowa
cikin mutane


Husnah tayi murmushi tace
ai dole takasa fitowa tunda bata da gaskiya takarasa maganar tana dariya


Umma tace tashi wa husnah kitashi kije kikiramin ita

Husnah tace to ta tashi ya shamsu yayi kaman yayi magana sai yabasar kawai




Next page

Yau kunga typing din kadan watspp ne yakebani matsala


Please marasa comments ina ganinku fa kara nake muku


Masu comment ina alfahari daku Allah yasaka da alkairi

Love you all

😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘
[06/05, 11:21 AM] UMMU AFAN �: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗

🎗🎗
🎗🎗
🎗

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM



STORY & WRITTEN
BY
THE SPECIAL AUTHOR /WRITER

UMMU AFAN 🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊




�FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION�

�F.C.T.W.A.�



�HOME OF QUALITY AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION�


🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SISTER SHAFA'ATU (UMMU KHALEEL)
Ina alfahari da comment dinki over kina kokari sosai wajen suburbudo comment Allah yabar
zumunci🎗��������������





🎗AKWAI LOKACI 🎗




🎗 PAGE 156 to 157🎗

HUSNAH tashiga dakinsu da sallama tasamu meenat kwance dawa a hanunta

Tana chart husnah tace anty meenat umma nakiranki


Meenat tadafa kirji tace nashiga ukuna
Wallahi ina matukar jin kunyar 'yan gidan nan


Husnah ta ballawa meenat harara tace saikizaba

Ko zuwa kiran umma ko jinkunyar

Meenat tayi saurin saka hijabin dogo har kasa

Tace muje amma Dan Allah ya shamsu yana falon wallahi banason hada ido dashi
kunyarshi nakeyi wallahi



Sosai dariya yakama husnah tace yaukuma kece da kunya meenat


Meenat tazunburo baki tace bake kika fada ba kuma alhalin niban fada miki da bakina ba



Husnah tayi murmushi tace to ai labarin zuciya atambayi fuska



Husnah taja hanunta suka fito alokacin ya shamsu yadauki cup din tea dinshi


Yayi gefen kujera yazauna yana shan abinshi


Meenat suka fito da taga baya falon tayi hamdala azuciyarta

Ta durkusa harkasa tazauna gaban umma tace umma ina kwana

Umma tayi murmushi tace haba amina kinbuya adaki kinki fitowa kisha iska

Meenat tayi murmushi tace ba komai umma tace umma azumi nakeyi

Kafin umma tayi magana anty kubra tafito daga part dinta tace yauwa kokefa meenat amma
kinki fitowa kisha iska


Meenat kanta akasa tace anty ina kwana anty kubra tace lafiya qalau antashi lpy


Umma tace wani irin azumi yau lahadi

Husnah tace au umma har kinyarda ma azumin takeyi


Wayace tayi ringing kan dining din dasuke husnah tace ya shamsu ankiran wayarka

azabure meenat ta kalli bayan ta kan kujera aikuwa caraf suka hada ido
Tayi saurin saukar da fuskarta kasa tana

Shima ya shamsu baisan lokacin da yakalleta ba yakau da kansa


Husnah ta kallesu tayi murmushi kawai


Umma talura da yadda meenat tarikice tace tashi mana kici abinci

Meenat tace to umma amma kasa yafi min dadin cin abinci


Anty kubra tadauki wayar ya shamsun takai mai

Yakarba yace tazauna anan
Tayi murmushi tace ina karyawa nefa honey

Ya tashi yadauki wayarsa da yace biyoni

Anty kubra tabi bayansa sukatafi part dinsu meenat ganin sunbar falon yasa tadan sake kadan

Prof da Ahmad ne sukawa kano diran bazata

Ya shamsu sosai yakarbesu a falonshi prof yakira wayar husnah yace baby kufito mutafi ko

Husnah tace badai kunzo kanoba

Murmushi prof yayi yace naki wasane ke atunaninki zan iya barinki har kwana hudu ukun ma
dakyar nayi


Yashamsu yashigo falon yaga Hakeem nawaya

Ahmad yace kaga wannan romeo din barnar kati baya mishi wahala

Wai kuna gida dayama amma kana kashe murya a waya

Ya shamsu yayi murmushi kawai yana jin dadin yadda Abdul Hakeem yake ba wa kanwarsa
kulawa ko agaban wayekuwa


Kodan wannan zai auri meenat zai riketa tsakaninshi da Allah




Meenat da husnah suka fito cikin rakiyar anty kubra da umma

Sosai umma tahadawa meenat tsarabar su humra ne da dai sauransu anty kubra ma tabasu
nata

Sosai sukayi kewa meenat dai Allah Allah take sutafi Dan ta takura sosai wallahi








********
Bayan sati biyu da komawarsu Abban su husnah da wani abokinshi sukatafi Kaduna

Dama daddyn Hakeem yasan dazuwansu

Shida daddyn Ahmad suka karbesu

Bayan anci ansha Abba yakawo musu bukatarsu

Daddyn Hakeem yanisa yakalli daddyn Ahmad yace lalle wannan yarinya amina Allah
yanasonta

Mutum kamili mai nutsuwa kaman shamsu yanemi auranta bayan duk Abu abuwan datayi
abaya


Abba yace duk wannan yawuce alhaji muyi maganar yanzu kawai



Daddy yace duk da bani ubanta jikatace to amma da ubanta da itadin duk mallakinane wallahi
naba wa shamsu ita halak malak


Nan sukayi hamdala da godiya

Abba yace idan bazaka damuba tunda ba auran farko bane daga ita harshi shamsun zanso a
yanka mana sadaki mubiya


Daddy yace hakane amma naji wannan alamari sosai



Daddyn Ahmad yace tunda hakane ga sadakin nan nabiya wa Dana shamsu


Abba yace a a haba alhaji karmuyi haka daku mana wallahi da komai mukazo


Daddyn Hakeem yace haba ba komai karka daga hankalinka dan yabiyawa danshi sadaki kuma
ma ai shamsu Dan mune kana nufin da wani guri yaje Neman auren aimune masu biyamasa
sadaki bawai Dan bashidashi ba sai Dan can cantarsa

Hakadai sukata raha abinsu har suka tsaida lokacin aure nan da wata biyu masu zuwa


Abban ya shamsu ya fito da kudi yace tunda anbada nasadaki to ga kudin Nagani inaso


Dakyar daddyn Ahmad yakarba



Da daddare daddy da Hakeem sun gama cin abinci
Daddy yace akwai maganar danakeson nayi daku kaida mummynka


Mummy hafsat tayi murmushi tace to tasamu kenan tunda naji meeting

Daddy yayi murmushi yace sosai kuwa


Nan daddy ya sanar dasu komai

Hakeem yace daddy kar ayi haka wallahi matar shamsu yarinyar kirkice

Aje amina taje tabata musu zaman dasukeyi mai cike da kwanciyar hankali


Daddy yace duk namusu bayanin wannan sai suka nuna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login