Showing 33001 words to 36000 words out of 39554 words

Chapter 12 - AKWAI LOKACI Book 2 end BY UMMU AFAN .pdf

02 Jul 2025

2113

min matar ma bata da matsala itama
tabada goyan baya kuma tayi alkawarin zama da meenat tsakani da Allah


Hakeem yace aidama itabata da matsala su laila ne damuwata kunsan halinsu

Suje suyita abin kunya mummy tace Gaskiya kam

Kuma gaskiya yarinyar nan kubra bata can canci kishiya ba

Muna zumuncinmi gwanin sha'awa da mutane azo ana raba mana abin kunya


Daddy yace to duk naji baya ninku

Nan yadauki waya yafada wa abbansu husnah komai abban su husnah yace bani Abdul

Hakeem din


Abdul Hakeem ya yakarba da ladabi kaman yana gaban abban sun dade suna magana kafin
sukayi sallama


Abdul Hakeem yace Allah yasa dai karsu dinga jamana abin kunya a inda ake ganin
mutuncinmu


Dadddy yafito da sadakin da kudin Nagani inason yakuma fada musu ranar da suka tsayar


Mummy tace har cikin raina naji dadin wannan Abu sai dai ita aminar akira ajamata kunne sosai
tazauna lpy dasu



Hakeem yakira wayar meenat tazo tazauna akasan carpet

Ke yaushe kuka fara soyayya da shamsu

Mummy hafsat ce ta wurgo mata wannan tambayar duk ta gigice tayi shiru kawai

Daddy yayi murmushi yace yanzu dai mamana kinason asake minkafa kenan ko akaro na biyu


Mummy tayi murmushi tace ai gwamma da aka maka kafar taje can nima na huta da zaman
kishi da ita


Daddy yace kai mummyn Hakeem badai kishiba
To nikuma ba inda za aje min da mata inasonta


Meenat dai yau duk surutunta bakin ya mutu

Hakeem yace amina Dan Allah karkisake biye ma su laila kizo kibamu kunya

Kinga dai gidan mutunci ne ko
Meenat tadaga kai sama tace to daddy

Hakeem yawa mummy da daddy saidafe yawuce part dinshi
Daddy da mummy suka cigaba dawa meenat nasiha harshima daddyn yaje byakwanta




Hakeem nashiga part dinsu yaga husnah kwance tayi bacci cikin wasu fitunannun sleeping
dress

Ya karasa kusa da ita yakwantar da kashi a kirjinta husnah dai bacci yayi nisa

Yaga dai bazata tashiba Dan tunda tasamu cikin intafara bacci kaman ta mutu

Yashiga yayi wanka kafin yafito yayi shirin kwanciyar sa

Ya kwanta tare da manno husnah ajikinshi Dan harsunsaba baya iya bacci saiyajita jikinshi haka
itama idan tabude ido taga yana kusada ita tofa tana jikinshi


Yana nashafa mata kanta yaso yatasheta sai kuma yafasa

Dan yaga taji dadin baccin ta




******
anty kubra zaune itada umma suna lissafin kudin dazai kawo na sayayyar kayan lefe itafa anty
kubra komai takeyi daurewa kawai saboda kwata kwata bata jin dadi sosai

Taki nunawa ne saboda karaga kaman saboda maganar auren yasata damuwa


Suna gama wa ta tashi tadauki hijabinta tace umma barin shiga nan makwafta yarinyar salma
ba lafiya manal


Umma tace ayya koshiyasa bana ganinta kwana biyu anty kubra tace wallahi

Umma tace kigaishemin Da ita

Anty kubra tana fita gidan doctor salma tashiga taci sa akuwa tana gida


Doctor salma tace kai yau kubra kece komafarki nakeyi anty kubra tayi murmushi tace nice
wallahi doctor

Tace mushiga daga falo

Nan suka shiga bayan sungaisa

Takewa doctor salma bayanin yadda takeji kusan sati uku da suka wuce

Doctor salma tayi mata tambayoyi ta amsa

Tace kitashi kishiga kiyi fitsari zanmiki P T test


Anty kubra batayi musuba
Tayi doctor tayi gwaje gwajensu

taga yasa mata positive aikuwa da murna tasanar da anty kubra


anty kubra tsaban farin ciki saiga hawaye sharshar yana bin kuma tunta


Doctor salma tace haba kubra ai murna yalamata kiyi ba kukaba

Kubra tace hakane Allah nagode maka

amma Dan Allah karkifa dawa megidanki Kinsan idan megidanki yasani zaifadawa shamsu
kuma banason mijina yasan da wannan cikin


Doctor salma ta gwalo ido tace kekuwa kubra meyayi zafi haka abinda kukadade kuna nema
Allah yabaki kice kar a fadawa mijinki


Kubra tace ina da dalili mai karfi ne yasa nafadi haka kuma zanfada miki yanzu
Nan anty kubra tabata labarin komai
Tace kinga idan wallahi nasan zaice yafasa auran

Kuma idan yafasa auran bazan yafewa kaina ba zanga kaman nice sila

Kuma gashi gidan mutunci zai yi auran idan yace yafasa ai zasu daukeshi karamin mutum



Doctor salma baki tasake kawai tana sauraron karfin hali irin na kubra
Gaskiya ko ita kubra ta matukar burgeta
Tana hali mai kyau Wanda kowani miji zaiyi alfahari da ita



Murmushi salma tayi tareda jinjina mata tace Allah dai yabiyaki kubra wannan jahadi da kikeda
niyyar yi
Kuma insha Allah keda kanki zakifadawa mijinki alokacin daya dace



Nan sukayi sallama kubra ta koma gida



*******


Biki ya rage saura sati kowani bangare sunata shiri kamar masu aurar da budurwa ko saurayi
komai da ake bukata ya shamsu kubra yakeba itakuma tazage tsakaninta da Allah tanayin
komai
Ba Wanda ya lura da cewan tana da shigan ciki ajikinta saboda komai da jikinta takeyi abunta



Kayan lefe kuwa masu kyau da tsada guda dozin wato shabiyu itama kubra yasake mata komai
kuma yabata makudan kudi taki karba yanuna rashin jindadinshi

Saita karba tamishi godiya


Kamar kullum sunzo kwanciya tace honey yanzu Dan Allah abinda kakeyi ka kyauta

Ya shamsu dake aiki a lap top dinshi yajuyo yace meya faru honey

Anty kubra ta ce yau kusan saura sati fa auranka amma Baku taba magana ba aizaka sa
iyayenta suji badadi suzargi basonta kakeba kaman dole akama

Ya shamsu ai basonta nakeba kubra inada mace kamanke mezan nema agun wata mace

Kubra ta taso ta ringumeshi tabaya tace nasani mijina amma inason kaduba iyayenta Dan Allah

Ya shamsu yasaukar da ajiyar zuciya yace yanzu yakikeson ayi
Kubra tace gobe kaje Kaduna kufahimci juna Dan Allah kabata abinda take bukata na hidimar
biki


Ya shamsu yace naji Allah yakaimu shikenan hankalinki ya kwanta
Kubra tadaga kai tace yauwa honey

Yanzu kabar wannan aikin Dan Allah kazo mukwanta bacci nakeji gashi gobe zakayi tafiya ta
kashe computer taja hanunta mijinta zuwa kadu gado




******

Washagari kubra takira Husnah tasanar da ita zuwan ya shamsu
Tace tasanar da meenat
Husnah tace toshike nan kifada mishi yataho minda furar umman nan Dan Allah


anty kubra tace to mama food
Husnah tace anty hardake ko kinacemin mama food ko


Anty kubra tayi murmushi tace aidole wannan babyn dai yasaki ci wallahi




Suna gama waya husnah ta kalli meenat tace yaufa mijinki yanahanya saiki tashi kifara shiri


Meenat tace banason wasafa niwacece da zakice zaizo domina tadafa kirji


Husnah ta ce ke amatarshi mana

Meenat tayi murmushi tace hmm ninasan fa bawani sona ya shansu yakeba

amma zanmishi biyayya insha Allah zaiyi alfahari dani

Yauwa antyna meya yashamsu yafi so acikin abinci amma fa saikin tayani kisan har yanzu
hanun baifada ba
Tayi murmushi

Husnah dai tausayin meenat yakamata ashema itama tasan ya shamsu bayasonta

Tare sukaje kitchen sukayi aikin abinci



Large shabiyu da rabi sukagama

Kowacce tashiga wanka

Meenat tasha gayu sosai da taimakon husnah





Yashamsu karfe daya darabi



Next page



Your comment is needed fans

Ina alfahari da Ku over wallahi


🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊
[06/05, 11:22 AM] UMMU AFAN �: 🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗🎗
🎗🎗🎗🎗

🎗🎗🎗
🎗🎗
🎗🎗
🎗

BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM



STORY & WRITTEN
BY
THE SPECIAL AUTHOR /WRITER

UMMU AFAN 🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊🖊




�FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION�

�F.C.T.W.A.�



�HOME OF QUALITY AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION�


🎗I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SISTER BALARABA
Ina alfahari da comment dinki over kina kokari sosai wajen suburbudo comment Allah yabar
zumunci🎗��������������





🎗AKWAI LOKACI 🎗




🎗 PAGE 158 to 150🎗

Afalon su mummy aka sauki ya shamsu shi sosai suka gaisa da
Da mummy Husnah dake da mummy tace yaya ina furana


Ya shamsu yayi murmushi yace mummy kina fama da shawagwabar husnah umma dai huta sai
mummy kuma



Mummy tayi murmushi tace tayi abinta lokacinta ne ai tana debe min kewar yarinya mace

Yashamsu yace aitagirma dayawa mummy tace mummy tace wadin ai husnah yarinya ce idan
batayi shagwabar ta yanzu sai yaushe zatayi


Husnah tayi murmushi tace to yaya kaji daiko
Saika bani furana kawai

Ya shamsu yace ai na manta da furar ki

Husnah tayi murmushi tace caf ai kuwa da bazan bari kaga matarka ba nima sai ka koma
kakawo min kafin kaganta


Mummy tayi murmushi yanayin shakuwar ya shamsu da husnah yabata sha'awa


Sosai duk da yagirme mata hakan bai hanashi Jan kanwarshi ajikiba


Key din motar yabata yace tadauko a mota
Da murna ta karba tayi hanyar waje


Mummy tace yi a hankali 'yata kefa saikace bame cikiba bakya nauyin cikin ma kai yarinta me
dadi


Mummy tace to nibazan Barka kaci abinci
Barin turo ma ita aminar

Ya shamsu wayarsa yadauka yayi Dial number din kubra tana ganin kiranshi tadauka tayi
sallama tace honey ka isa lafiya ya kanwata


Ya shamsu yace zakifara ko nifa nakiraki ne naji nice voice dinki

Kubra tayi murmushi tace nagode mijina dafatan kasamesu lafiya yace kowa lafiya

Husnah tashigo falon ganin yana waya yasa ta haura sama gurin mummy can falon daddy

Clashing sukayi da meenat zata sauko husnah tace kai matan yaya kinyi kyau wallahi kar ki
safa saikuma tayi shiru tana murmushi meenat tace karnasa me kinganki

Kina nan sai tsokana ko am kinsan meye husnah wallahi kunya nakeji sosai

Husnah tadafa kafadarta tace kisawa kanki kwarin gwiwa kefa mace ce haba yakikeson badani
ne kaman ba meenat din Dana sani ba


Kinsan Allah saikinyi da gaske kafin kisamu kan yayana wannan kunyar duk bazai fishshekiba
wallahi
Saboda bahaka antyna take mikishiba
Beside ma fa namiji baya son yawan kunya
Saboda kunyar yana cutar dasu dayawa


Meenat tace nagode da shawararki yar uwa kuma small mama na
Zanyi aiki dashi

Ta kalli ledar hanun husnah tace karfa kishanye kekadai please nasan cinki

Nasan wannan furrar tunda kika damu dashi zaiyi dadi over wallahi


Husnah tace jeki fa kinshanya min yaya na a falo

Meenat tayi murmushi ta karasa sauka


Cike da ladabi da kunya ta durkusa kasan carpet tana jiran yagama wayar sa

Shikam ya shamsu soyayya sosai suke zubawa a waya da anty kubra

Yadau kusan minti talatin kafin kubra tace Dan Allah idan kana kusa da kanwata ka kashe
wayar nan
Ba dadi wallahi cin fuskane

Ya shamsu ya kalli gefen da meenat take tunda ta ajiye kanta kasa bata dago ba saita bashi
tausayi

Yacewa kubra gata nan yamika wa meenat wayar batayi tsamma niba taga wayar dago kai tayi
suka hada ido yace karba

Ta karba suka gaisa da anty kubra meenat ta tambayi umma kubra tace umma lafiya qalau


Kafin sukayi sallama kubra ta kashe wayar Dan karma yakarba wayar yasake wata maganar

Meenat ta kalli screen din wayar ya shamsu hoton taga hoton anty kubra dashi sunsa kaya
iridaya suna murmushi hoton yamata kyau sosai

Ya shamsu ganin bata mika mishi wayar ba yasa ya kalleta da kyau yaga metake kallo yaga dai
tazubawa
Wayar ido


Meenat tamika mika mishi wayar
Tace ya shamsu ina wuni yace lafiya ya mutan gidan

Tace kowa lafiya yace madallah

Daga nan kowa yayi shiru

Tsawon minti goma daga baya yace amina bakya maganane ko kuma nine bakyason ma
magana


Meenat tace bahakabane to bakaci komai na gashi ankawo ma komai

Ya shamsu ya kalli kayan gurin yace ai bakiso naciba tunda baki bani komaiba haka ake barin
bako

Meenat tagirgiza kai tamatsa kusada abincin ta saving dinshi komai

Tace bissimillah ya shamsu yace to anty meenat

Tayi murmushi batace komaiba kasa yasauka yafara cin abinci


Meenat haka kawai tatsinci kanta da sahanu tadauki wayar ya shamsu

Ya shamsu ganin tadauki phone dinshi murmushi yayi kawai yacigaba da cin abincinsa

Meenat kallon hotuna take sosai daga hotunan shi saina kubra saina husnah da su umma

Ta dauki wayarta tayi connecting ta xender tayi ta tura pic masu kyau na shi Dana anty kubra


Ya shamsu yace mekike turawa tace hotuna
Yace nawa kenan tace na anty kubra

Yace banyarda ba inga wayar idan dagaske kike

Meenat tayi murmushi yabashi wayar duka yaduba yaga abinda ta tura

Yadauki number dinta yabata wayar

Yaciro kudi bai Masan tawansuba ya ajiye yace ga wannan kiyi hidima dasu

Meenat tace wallahi kabarsu niba abinda zanyi
Sai walima kuma mummy ce zatayi komai

Yace yace nariga nayi niyya

Tayi godiya kawai daga nan ya kalli agogo yaga time yace zan wuce kinsan sainabi office din
daddynki Dan baimasan na zoba



Meenat dai tana ta wasa da hanunta

Duk wayoyin ya kwashe yazuba a aljihunshi meenat kuma takasa magana

Yace kikara su mummy muyi sallama

Meenat ta wuce yabita da kallo harta sama amma batasan yana kallon ba

Sunyi sallama da mummy tace Dan Allah kagaishemin da umma kace mata munga tsaraba
mungode tabashi aika yakaiwa umma

Husnah tace to yaya sai munkawo ma amaryar ka

Yace shikenan yar kanwata kikula da kanki
Tace insha Allah yaya sakon gaisuwa na zuwa ga antyn data fikowacce anty aduniya

Ya shamsu yayi murmushi yace zataji insha Allah meenat tadauki kayan da mummy tabayar
akaiwa su umma

Tarakashi hargurin mota tabude tasaka kafin ta jingina da jigin motar tana son tambayar
wayarta tana kunya


Ya shamsu kuwa baimasan tanayiba tashiga motar shiyace to amaryar shamsu sakin kinzo ko
yana gama fadar haka yaja motarshi yayi gaba


Murmushi meenat tayi tace nasan bakasona ya shamsu amma ina fatan kasoni a ranka koda
bazai kai yadda kakeson anty kubra ba daman bankai kaina nanba
Saiga hawaye yana zubo mata

Saiji tayi ana share mata hawayen
Tabude ido taga husnah ce

Meenat bata San lokacin data fada jikin Husnah tana kuka ba
Kukan datarasa namenene shi





Da daddare YOUNG PROF da husnah falonsu Hakeem yace sweet albishirin ki Husnah dake
kwance jikinshi tace goro Prince

Yace saikinfada min goron albishir dazaki bani idan nafada miki husnah ta tura baki tace kaifa
Prince nasan irin goron ka fa tayi maganar tana shagwaba

Yayi murmushi yace to aike kekadaice me iyabani wannan goron

Husnah tasake kwantar da kanta a shimfudaddan kirjin mijinta tana shakar kamshinsa

Tunda tasamu ciki itakuma takeson kamshin Hakeem sosai kullum suna manne da juna idan
yadawo daga office


Tace inajinka yace angama miki gidan marayun nan da asibitin saboda haka bayan biki

Saimuje mukwaso su umma suzo sugani susa albarka aciki



Baiyi aune auene ba yaji hawaye a kirjinshi
Yadago kanta yace lafiya sweet meye kuma na kuka husnah tace bansan mezan maka
nabiyaka Prince kamin komai a rayuwata kacika min burina danake dashi tun ina yarinya Allah
ya

Kafin takarasa godiyar dai Hakeem ya hade bakinsu guri daya saidaya kusan minti biyar kafin
yace karkisake min godiya

Wallahi aini bawan Allah kuma ni bawankine kiyi yadda kikeso dani bayan su mummy banida
samada ke


Itama dai husnah ganin bazai barta tamishi asalin godiyaba
Yasa tafara nuna mishi farincikinta tahanyar abinda yafiso





*****
Hajiya rukayya da hajiya Laila

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login