Showing 1 words to 3000 words out of 30182 words
Chapter 1 - ZURFIN CIKI Book 3 end by halima Abdullahi K Mashi .pdf
IKI book 4 part 1
ZURFIN CIKI book 4 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:42
Inna harira tace, Allah ya kyauta ku tashi mu tafi.
Suka mike Suka nufi dakin ummi. Duk da ummi a
da bata tunanin tana da lokacin bishira, yanxu
kam dole tasan zaman da zasuyi. Su inna saratu
suka ce ma ummi duk abinda zatayi don allah
kada ki kulata. Suka ce tayi harkokin gabanta tayi
biyayya wa mijinta shine abunda zai fisheta.
Ummi tace To amma a zuciyarta bata tunanin
zata zuba ido a rainata. Suna tafiya fatima ta
shigo yiman sallama, ummi tace don allah fati ki
dan tsaya ni kadai fa zan zauna a dakin nan. fati
tace wayace kada kisan kawaye? Ummi ta ce
wane kawaye, auren da a ka daura cikin yan
mintina? Fati tace, Yau zakiji abinda mata kaji.
Ummi ta damko mayafin fati, ni fa inajin turo, wai
da gaske da wahala ko kina tsokanata ne? Fati
ta kamo kunnen ummi tayi mata rada. Ummi ta
zaro ido tare da cewa, Da gaske? Fati ta sheke da
dariya tace sai nazo jin batun. Ummi tace sirrine
ya za'ayi in fada miki sirrina? Fati tace au ni
shine na fadamaki nawa ko? Ummi tace kinyi
haram da kika fada fati tace, "ke kuma kinji
haram ko? Suka sa dariya. Duk yanda ummi taso
fati ta tsaya amman taki, don haka sukayi
sallama. Fati ta shige dakin bishira don yi mata
sallama. Bishira tace, fati fitar min daga daki
bana wasa dake, tunda kema naga kin koma
jam'iyar waccan yar iskar, fati ta fita, cikin ranta
tana cewa ba zanki yar uwata ba don kishinki na
banza tayi tafiyata. Ummi tsuru tayi tanaji tsoron
abinda fati ta fadamata, amman sai wata zucia
tace keda ba sonki yake ba kila ma bazaibi ta
kanki ba, sannan ta samu yar natsuwa. Abba ya
fito zai nufi gida sai kuma ya fasa ya nufi super
market, ya siyo audugar mata yana tsammanin
gobe ne zata tashi da al'ada a lissafinsa. Tun
sanda ta soma bai taba mance ranar ba, haka in
ya chanza mata lokaci duk yana lissafe. Ya sai
masu yan kayan masarufi sannan ya fito, gida ya
nufa amman gabansa yana faduwa kila har
yanxun ba a kai ummi ba. Da yayi fakin sai kuma
ya nufi gidan su umma duk kowa ya watse. Yayi
sallama tsohuwa tana alwala ta amsa. Umma
daga kicin ta amsa, tsohuwa tace "wane kinibibin
kuma ya kawoka mai sunan malam? Bayan an
kai maka ita? Yace kaji tsohuwa da wata magana
da gurin ummi nake zuwa? Ni gidan mu ne. Tace
kadaiji shi, takwara dai kada inji kada in gani, don
nace mata duk abunda kuka mata tazo ta
fadamin. Yarinyar nan tana kuka wiwi tabar gidan
nan. Umma cikin dariya tace "toh ai tsohuwa in
don Abba baza ayi fada ba, ummin ce dai abin
jama kunnen. Tsohuwa tace 'a' a daina zancen
nan suwaiba kada ma ya samu nayi. Abba yace"
Toh bari in zo in hada maki kayanki mu tafi can
don kada wani ya zafin cewa. Kinga kyafi tare
mata. Tace ina gana nan din ma zanji. Yace
Alhaji sun shigo kuwa umma? Tace A'a basu
shigo ba. Yace toh bari in isa gida. Tace toh
Abba ummi ma dazun aka rakata. Don allah Abba
ka kara hankuri a kan na da, sannan matarka
kuma kada kace zaka nuna mata bambanci a kan
ummi yar uwarka ce. Ka kwantar mata da hankali
ka mata adalci, sannan kada ka bawa ummi kofar
da zata raina bishira. Yace zan kiyaye insha allah,
kuma don allah umma ki kara mika godiata gurin
alhaji. Tace haba Abba yaya kake fadin haka?
Alhaji ai mahaifinka ne karka dinga kallon
alakarka da ummi. Yace haka ne duk da haka dai
a min godia, tsohuwa tace yaki godia ya samu
mata a sama don rashin imani mai sunan malam
ko gyauto bai sa mata ba, toh kasani tana binka
bashin lefe. Abba Yace umma ni dai na wuce.
Umma cikin dariya tace "Toh Abba. Yace tsohuwa
ni nayi gaba, don in na cika tsayuwa a nan kila
mu dambace, Tsohuwa tace kai dai jeka na baka
amana ya tafi yana dariya. Koda ya kai kofar
gidan sai ya bude mota ya dauki kayan
masarufinshi ya nufi cikin gidan salam dai duk da
jarumta irin tashi gabansa ne ke faduwa. Bai san
wace irin masifar bishira ta tanada ba. Ya shiga
da sallama. Bishira tana zaune akofar daki tana
goye da muhibba, amman bata amsa ba. Duhun
magriba ya soma dan daf da a kira sallah a ke,
yace bishira ya ba a tada inajin ba? Tace tunda
kazo yanxun ai sai ka tada kai. Da kafin wata
tazo ai baka taba zuwa kace a tada inji ba. "Abba
ya kalleta a zuciyarshi Yace" mata kenan masu
manta alhaji. Ya aje ledodin hannunshi ya nufi
injin. Bishira ta mike ta nufi ledodin tana fadin
Tun yanxu a aka shigo mata da kazar, alamun ba
za'ayi ada ba kenan. Ni lokaci na sa wuraren tara
ya shigo ina lissafe da komai, ta bude ledodin sai
taga kayan masarufi d kuma audugar mata. Tsaki
taja tare da dangwarar dasu yana kallonta da ya
kara mai ya tada injin sa yazo ya kwashe ledodin
ya shiga falonta.vels / ZURFIN CIKI book 4 part 2
ZURFIN CIKI book 4 part 2
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:44
Kujerun da aka chanza mata masu kyau, amman
a ran abba yace ya basu sati biyu. Ya cire riga ya
fito yana son yayi wanka ne kafin a kira sallar
magana,yaja ruwa da sauri da sauri yayi ban daki
ya fito ya shiga falo ya kwalama bishira kira.
Tace minene kake damuna? Yace ina aka kai min
akwatuna na? Tace tace ina kuwa gasu can a
kicin da sauri ya fito, kicin din lafia? Ya tsaya
yana kallonta bani da mutuncin da za'a sa min
kayana a daki? Tace ni da aka guji dakina da
kayan a kace ni kazama ce, me zaisa in sake
kaine? Daga baice komai ba ya nufi kicin ya
kwaso akwatuna shi da takalmin shi ya kai
falonta. Bai tsaya chanza kaya ba, ya nufi
masallaci don zai rasa sallah. Bai baro masallaci
ba sai bayan isha'i amman bishira tana zauna.
Ummi kam ta kasa fitowa don tana kyankyamin
ban dakin, gashi al ada ta sameta da yamman
nan, sannan duk tanajin abin da sukeyi da
matarshi. Ya shigo gidan ya chanza kaya sabi fil,
ya feshe jikinsa da turarukkanshi wayar shi ta
soma ringing ya daga salis ne. Yace aboki in ba
sallama akwai daga hannu ko? Kace an kai maka
rabin ranka koda ba zamu rakaka ba ai kayi
mana sallama. Cikin dariya Abba yace na yafe
salis yace To Allah ya bada zaman lafia. Suka yi
sallama zai aje wayar kenan sako ya shigo. Ya
duba ummi ce da wayar nan da ya bata ajiya
cewa tayi, ina da matsala, ina bukatar taimako.
Gabanshi ya fadi, sai kuma ya tuna kila al'adar
ce, don haka sai ya saka hularshi ya dauki ledar
audugar ya nufi dakinta. Har lokacin bishira nan
zaune inda take, tace au tun daga yanxu za'a
soma rashin adalcin? An dauki leda an nufi
dakinta? Sam baiko waiwayo ba, yayi sallama ta
amsa tare da gyara mayafinta, ya shiga suka kalli
juna Cikin ido zukatansu sukayi fari kal. Cikin
taushin murya yace, wane taimako kike bukatar?
Ta lumshe ido sannan ta juya masa baya domin
kunya ta rufeta. Yace To karba ya mike mata
ledar ta waiwayo ta ansa da hannu biyu. Mamaki
ya cikata ganin audugar, ya yayi har ya san tana
bukatar audugar kuma a ina yake sanin lokacin
al'adarta har idan ya chanza? Tace nagode yayi
dan murmushi nima ina godia. Ya juya har ya
daga labule tace "Em na ce....." ya waiwayo yace
kika ce mi? Tace don allah inason maganin
wanke bayi ne, tayi maganar Cikin kyankyami,
sakamakon irin dattin da tagani a bandaki tare da
gamsa kuka. Yayi murmushi wane iri kikeso?
(IZAL) yace ai akwai amman yanxu Bai kamata ki
shiga wankin bayi ba. Tace zan wanke in dai
akwai. Yace bari in wanke maki, da sa tace a'a
yaya Abba zan wanke. Falon ya koma ya cire
rigarshi ya shiga jan ruwa. Bishira tana zaune ta
mike ina badai abokitaina ba, in zaka kwashe
mata rijiyar kwashe, amman a juye ko in baras
kuma in dai ruwan da za'ayi amfani dashi ne
kakeja, To kesani nima duk lokacin da zanyi
amfani da ruwa saika dibar min, ehee. Ummi ta
fito da bokitai don duk tana jinsu, tazo wurin
Cikin sanyin murya tace, Ya Abba don allah ka
bari in ja ruwan nan. Ya kalleta, take ya manta da
duk bakin Cikin da bishira ta kunsa mashi.
Yanxun daga zuwa saiki fara jan ruwa? Ummi
tazo ta kama igiyar gugar, ai ba zama nazoyi ba,
Ya Abba bauta nazo yi, Aljanna sai an dage. Ya
saki dariya bishira ta dakatar dashi da ce wa
"Karuwanci za'a gwadaman? Ta daga ruwan da
ya zuba a bukati zata watsama ummi, yace kina
watsa mata zan baki Mamaki. Cikin tsawa yayi
maganar ta tsaya cak da bokitin yace, Sakarya
mai kishin hauka. Yaci gaba da jan ruwan yana
zubawa abokitan da ummi ta fito dashi. Bishira
ta aje ruwan sannan ta hankadar dashi a kasa,
Bai ko kalleta ba. Ya zuba ruwan sannan ya fito
da izal da omo. Daki ummi ta koma ta dauko
tsinsiyar da aka sai mata don wankin bayi, kin
tafiya Abba yayi tana wankewa yana zuba mata
ruwa har sai da taga bayin yayi yanda take
bukatar sannan ta hankura. kyankyami jikinta
takeji don haka taje ta hada kayan wanka har
lokacinzurfin Ya Abba yana wurin rijiyar. So take
ya matsa taja ruwan amman yaki, don ya lura
bishira shi kadai take shakka zata iya zartar da
komai kan ummi. Shine ya sake zuba mah ummi
ruwan wanka, sannan ya coge har ta gama ta
fito rufe da hijabi tayi dakinta, sannan ya dauraye
jikinsa yaje ya maida kayanshi ya nufi wane.
Bishira tana nan wurin kofarta ta kasa zaune ta
kasa tsaye, bakinta kuma Bai fasa sambatu ba
sai kace sabon kamun hauka. Fadi take kuma a
zo a biyani duk basisikan da nike, ehee. Kuma in
yarinya tamin in murji bukina. Ummi kam ta
gyara jikinta tsab ta saka sabbin kaya ta feshe
jikinta da turarokan da umma ta sai mata. Tunda
ba lefe aka mata ba bare ta samu kayan shiga.
Kan doguwar kujera ta mike, salam yanzu taji
yinwa tana tsammanin rabonta da abinci tun
karin safe. Ta shafa Cikin ta ina ma umma na
aiko man da abinci. Ta furta a fili WAYA nan ta
jawo tana tunanin sanar da Abba cewa tana jin
yunwa. Sai wata zucia ta hanata wannan ba
girman amarya bane. don haka ta share ta bude
shafin game tana ta bugawa. Sai sha daya Abba
ya shigo gidan, ya rufe gidan. Nufinshi ya wuce
kai tsaye dakin ummi, amma sai ya tuna da kazar
da ita bishira ya sawo mata. Duk da baya tunanin
ta karba ga mamakinsa tana tsaye a tsakar daki
har yanxu da daurin kirji take. Wannan ya nuna
batayi sallah ba, bare wanka. Ya mike mata wata
harara ta zabga masa banaci, ya juya batare da
yace mata kala ba, ta biyo bayan shi, A bani
basussukana da nike bi malam. Ya nufi dakin
ummi taba biye dashi, ummi ta turo kofa dama
yana kokarin tura kofa dama yana kokarin tura
kofar bishira tana rike masa riga ta baya. Ya
waiwayo Cikin zafin nama zai wanka mata mari
sai taci sa'a ta tsugunna, Cikin azama ta yunkura
tayi baya da gudu. Banda tsaki da yaja Bai ce
komai ba. Ya shige dakin ummi da sallama, ummi
bacci ya dan dauketa saboda gajiya. A kan kujera
take da waya a hannunta. 4rm Shamsy bello
balarabe.IKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 3
ZURFIN CIKI book 4 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:48
Niyyarta yau sai taji komai, don haka ta kai yarta
ta kwantar, dai dai lokacin ne abba ya fito don
kashe injin. Sake fitowar da tayi ne taganshi zai
koma. Wayan cewa tayi da daukar buta ta shiga
bandaki, shi kuma ya shiga daki ya kulle kofa,
tazo ta manne jikin kofar. Fitar abba shine yaba
ummi damar saka kayan baccinta, don bata iya
bacci da kaya masu nauyi. Fargabarta yaya
kwanciyar tasu zata kasance? Kan kujera ta
zauna tare da kwantar da kanta a hannun kujera.
Shima abba yana da jin zafi don baya iya bacci
da kaya sai da gajeran wando kurum, idanu ummi
ta kulle lokacin da taga ya abba ya soma cire
tufafinsa ga hasken cocilar da ya kunna. Filo ya
dauka ya jefa Kan doguwar kujera ya kwanta
rigingine, ganin haka sai ummi ta mike ta nufi
gado addu'a tayi sannan ta lumshe ido har bacci
ya dauketa. Fuskarta cike da murmushi zuciyarta
cike da godia allah yau gata dakin ya abba a
matsayin matarsa. Abu daya ya rage mata shine
ta koya masa yarda zaya sota. shima farin ciki
ne a ranshi yayi da idanuwanshi sukayi kuri a Kan
gado yana hango ummi ya ta zama halalinsa Abu
daya ya rage shine ya koya mata sonsa. Bishira
data labe bata jiyo komai amman kunnuwanta
suna jiyo mata magana kasa kasa,,hawaye na
zuba a idonta batasan iya adadin awanin data
dauka a kai ba. Koda ta koma daki juyi kawai
take a gado. Abbanta abun sonta yana can
kwance da wata, watar ma makiyiyarta wadda ta
tsana. Wata zuciya tace kije ki watsa masu man
petur wata tace ki bari da safe ki caka masu
wuka babu abinda bata rayaba har asubahin
farko. Labule ta daga ta shiga leke taga ko zasu
fito, lokacin ne kuwa abba ya fito yaja ruwa a
bokitai yayi wanka da alwala. Ba zata gane ko
wani Abu ya faru tsakaninsa da ummi ba don
wanka al'adarshi ce Koda bai dauki najasa ba.
Nafila ya shiga yi da rokon allah yasa ummi ta so
shi, ya kuma hada masa kansu. Koda zai tafi
masallaci bai tashi ummi ba tunda yasan ba
sallah zatayi ba. Bishira ta fito tasa kujera kofar
daki ta zauna, saboda tashi bai bar ummi bacci
ba, don haka ta tashi in tana al'ada yini take
wanka gaba daya sai ta tah ktankyamin jikin ta.
Ta fito da bokitai duk ta cika d ruwa, Bishira tana
kallonta sai da ta wanke bayi tas, sannan tayi
wanka. Sauri take tayi kwalliya don a cikin
nasihohin da umma tayi mata a safiyar da za'a
kawota gidan miji tace kada ta sake mijinta ya
ganta cikin kazamin yanayi. Kuma kada ta bari ya
shaki wari daga gareta, tayi shafe shafenta.
Atamfa ta saka riga da siket mai ruwan hoda
hoda da ruwan kwai. Daurin dan kwali ta kafa
sannan ta feshe jikinta da turaruka masu kamshin
gaske, sannan ta shiga gyaran dakin duk da ba
datti yayi ba. kayan da abba ya cire ta ninke don
da jallabiya yake zuwa masallaci, sannan ta dau
kujera ta kishingida saida gari yayi haske sannan
ya nufo gida. Tsaki bishira ta jamashi maimakon
amsa sallamar ta kara da cewa an girma ba'a
san an girma ba, an kwana da yar ciki abin
kunya. Ai wallahi baka cika dan halas ba da ka
auri yarinyar datayi sanadin kulleka kaci duka har
aka ballaka ba. Ya kalleta dalilin kenan da ban
cika dan halas ba? Tace eh baka cika ba, yace
toh jeka naji ni shege ne, in don dai na auri ummi
ne, tace munafuki dama can kana sonta. Ya sake
wai wayoowa yace so kuwa mai tsanani. Takaici
ya cikata ta daga murya allah ya isa munafuki.
Ya nufi dakin ummi wadda ke sauraren duk
abunda ake. A cikin ranta tace ina ma son da
gaske ne? Tasan ya fada don kawai yaba
matarsa haushi. Da sallama ya daga labulen,
ummi ta amsa tare da tashi daga kishingida da
tayi, ya zauna tare da lumshe ido. Lokacin daya
kuma ya shaki kamshin turarukan data fesa. Ya
kalli Fuskarta labbanta da yake matukar so sun
sha jambaki ruwan hoda. Take abba ya manta da
duk wata damuna koh kalma marar dadi da
bishira ta fada masa. Daga inda take zaune ta
dan rankwafa don girmamawa tace ya abba ina
kwana? Lafia qalau ummin abba ya bakon wuri?
Ta lumshe ido saboda jin dadi sunan daya fada
mata. Alhmdllh ya sake karkatawa yana kallonta
sosai yace to masha allah, yanxu kinsan minene?
Ta tattara hankalinta gareshi tace a'a? Yace kiyi
hnkr nasan a al'adar ta hausawa amarya ta Kan
yi sati daya cir ba tare data yi ko cangal ba. Toh
hnkr zakiyi kinga ke tun daga kawoki jiya kin
soma da wanki toilet. Sannan yanxu ma ina son
ki ciro rishonki a hada shi a sa kalanzir mu karya.
Kin dai ga yanayin yanda matar gidan take
gudanar da nata kishin. Ummi ta gyara zama ta
tuna nasihar ummanta da tace in zaki yima
mijinki magana kalaman ya zamana kin zabo su
ne ba wai kin sakesu ba. Ta kalle shi, shima ita
yake kallo, tace ya abba don wannan ne kake ban
hnkr? Yayi murmushi tare da lumshe ido ya kuma
budesu lokacin guda, a yaran soyayya yana nufin
eh, itama ta fahimci yaren don haka taci gaba da
cewa. Ya abba ni dama ba zama nazo ba, neman
aljanna nazo kuma zanyi komai don na sameta.
Don haka kadaina bani hnkr umurni kawai zaka
bani. Tun daga tsakiyar Kan abba har zuwa
babban yatsansa sai da ya motsa, don sanyin
muryar da ummi tayi amfani da ita tare da
kyawawan kalaman ta. A zuciyarshi yace tabbas
ummi haihuwar ummanshi ce, duk rainon umma
dole zai zama daban ciki ya'ya. Ya kalli ummi
allah yayi maki albarka tace amin. Ta mike ya