Showing 18001 words to 21000 words out of 30182 words

Chapter 7 - ZURFIN CIKI Book 3 end by halima Abdullahi K Mashi .pdf

wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin

Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
s / ZURFIN CIKI book 4 part 21
ZURFIN CIKI book 4 part 21
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19
Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo
lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara
don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole
suka haqura suka bar mata. Ta haifi 'yarta
budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura
inda suka sa mata walida. Ummi nason yara, don
haka in tana gida to tana manne da walida, Abba
yana damuwa da rashin samun cikin ummi,
wanda ita ummin ta barma Allah komai. Shekaru
uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake
haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.
Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru
tace ita Abba yama takwara amma bata son ya
duke ta irin yanda yayi wa ummi. Abba kullum
qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai
da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a
rage ciye ciyen dadin nan agina shì. Haka kuwa
ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya
bishira, sai nashi sannan na yara. Yayi qoqari
gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata
kayan daki don bishira an canza mata daza su
tashi agidan su. Yace tabishi bashi in ya samu
zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,
tace ta yafe. Ummi dake karantar (BUSSINESS)
har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.
Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda
tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda
take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa
jakunkuna. Abin ya amsheta don har kayan aure
tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da
chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani
wan kawarta. Haka kawai ummi ta samu kanta
da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai
sauransu, sam bata san takamaiman lokacin
al'adarta ba. Don bata wani lissafi in yazo shi
kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta

daga batun ciki. Abba ya kalli nonuwanta, baby
kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi
haske ko kin canza mai ne? Tace yaya yaushe
kazama likita? Yace, ummi kin fa canza shirya
muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni
nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni zan je inya
tambaya game da yanda ki ka canza. Cikin jin
haushi tace sai ka dawo. Ga yara atsakar gida
sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani
nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza
ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.
Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace
yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi tsiya da qyar
bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23
ZURFIN CIKI book 4 part 23
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22
Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi
gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa
ummi bata da wani ammafni. Wannan ne ma
yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah
yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda
umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo
kafin ta dawo an karba mata. Ta kuma kara bata
shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su
rabu, Bishira tace duk zata roko. Ko ranar da
zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta
sun shigo wato makotansu a tsakar gida take
fada musu cewa mijinta kurum take tunani. Wai
zai sha wahala kafin ta dawo. Wata cikin su tace,
wahalar me ga shi da amarya? Ta ce amaryar da
ta ke a toshe, ai bata da ammfani. Ummi duk
tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata
so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko
Allah zai sa ta dawo ta kama sallah. Dayar tace,
to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya
tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini
makka in roko ma kishiya abin arziki. Ummi ta
fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma
kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da
tsafta. To ban san ma yanda zaki kwashe da
ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke
ba. Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce
kyaleta bakin ciki ne. Abba ya fito wanka yana

cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko? Yana da kyau
hakan. Ummi ta koma dakinta. Tun bayan tafiyar
Bishira Abba ya shiga takura musamman irin
wannan lkc na sanyi. Ya dawo da yiwa ummi 'yan
wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi
damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta
fadawa umma....... Kuyi hkr da typing din banda
lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI book 4 part 24
ZURFIN CIKI book 4 part 24
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24
Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a
suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,
sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don
su tafi sun kssa sanar da umman komai, har
sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace
umma ta fada maki matsalarta? Umma tace wa?
Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna. Abba
kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya
ne? Umma tace mike damunta kuma? Yace ummi
fada mata. Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da
cewa shiya fada. Cikin sa'a aka kira wayarshi,
nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita
fada. Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,
umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko
tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu
tafi bane? Umma tace wai bata da lafiya ne,
kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi
waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira
ya dawo ya fadaman. Tsohuwa taja hannun
ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta
riko hannunta. Takwara fadaman abunda ke
damunki. Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa
magana. Tsohuwa tace inda baki fadaman ba
akwai wanda zai taimaka maki ne? Tunda naga
duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa
fadamata to abun mai girma ne. Ummi ta daure
tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka
salati, sannan tace yannan badai angurya ba?
Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko
shine. Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma
tazo dakin da sauri. Tsohuwa Tace ina ga
yarinyar nan angurya ne a gabanta. Umma Tace
shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,

dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa
Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan
yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin
wannan ciwon. Rabon da inji labarinshi tun muna
yan mata. Tsohuwa Tace kai nima na jima banji
ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.
Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye
a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba
yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji
suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma
keyi. Alhaji Yace lafiya? Umma Tace yaran nan
ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma
Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka
zaune. Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani
abu ne dake toshe mace. Nan fa suka shiga
tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa
Tace wanzami za a kira ya yanka mata. Alhaji
yace to gobe zai kira wanzami. ZURFIN CIKI book 4 part 25
ZURFIN CIKI book 4 part 25
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26
Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da
zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma? Ta ce
eh, aikin sune. Yace gsky umma ba za a kai ta
gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.
Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku
ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne. Abba ya
ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani
wanzami ba, umma asibiti zamu. Yanzu kai ya
waye wanzamai ba duka suke dafa kayan aikinsu
ba, haka kawai taje ta hadu da wata cutar? Alhaji
yayi murmushi yasan kishi ne ke damun Abba, ya
ce Babana kada ka damu, goben sai kuje asibitin,
in sun ce ba su san shi ba to sai a zo a yi na
wanzam ko ? Kunya ta kama Abba, Sam ya
manta Alhaji yana gurin ya ce to Tsohuwa ta ce
kuje in kun je ma dawowa za Ku yi dan me taurin
kan tsiya. Abba ya ce naji kin ji ummi taso muje
gda Tsohuwa ta ce oho dai, kuyi ta tafiya in dai
akayi mata aikin ai dole ka barta ta warke . Alhaji
da umma dai dariya sukayi ta yi musu, shi kuma
yayi musu sallama, ummi kam kasa magana tayi
don duk ta tsorata. Suna fita ta rike hannun Abba
gam tana cewa. Don Allah ya Abba kada kabari

wanzam yayi mini aikin nan, zan ji zafi. Ya
rungumota, Ba zan amince ba wani ya ganmin
al'aurar mata, likita ma mace zan nema ko nawa
zan kashe . Ummi ta ce, to zan ji zafi ya Abba?
Ya ce, made ki damu, in asibiti ne kila suyi miki
allurar kashe zafi amma in wanzami ne ina za ya
ga wata allura yayi mini. Ummi sarkin tsoro ranar
kwana tayi cikin damuwa, washegari kuwa tun
bakwai suna asibiti. Babban asibiti suka je sun
yanki kati likita me kula da fannin mata aka tura
su. Mata dayawa suna ta kallon su ummi
musamman yanda Abba ke nan-nan da ita,
sannan wasu sungane shi kasan cewar shi dan
jarida mai farin mini. Wasu mazan kuwa sai zuwa
suke suna gaida shi. An kirata dakin ganin likitan,
ta mike zata Shiga Abba shima ya mike, wata
Nurse ta ce, malam jira mana, ya ce ai duk Mu
biyu ne bamu da lfy, ya shige likitan namiji ne ba
yanda ya iya dole ya yi masa bayani likitan yayi
ma ummi tambayoyi in da duk ta bashi amsa/ ZURFIN CIKI book 4 part 26
ZURFIN CIKI book 4 part 26
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:27
Sannan ya bukaci ta kwanta kan gado ya saka
safar hannu, juya kai abba yayi don gaskia ranshi
ya baci, lallai ya kamata mata musulmai su dage
suyi karatun likitanci don su taimaki yan uwansu
mata. Sai da likita ya gama dubata sannan ya iya
dubansa, likita yayi wani rubutu ya mika abba
tare da cewa, an baku gado zayi mata aiki gobe
ko jibi. Abba yace likita zan iya sanin wane ciwo
ne wannan? Likita yace tsirone dake fitoma mata
dai daiku. Sam abba bai fahimta ba don haka yayi
mashi sallama. Umma ce a wurin ummi tana
shan magani kafin ranar aiki inda abba
hankalinshi ya rabu biyu rabi gurin aiki rabi garin
ummi. Don ma umma ta koreshi da so yayi ya
rika kwana, addu'a kam yana yinta. Ranar da
za'ayi aiki abba hankalinshi duk tashe. Yana
zaune bakin gadon da take kwance ita kuma tana
can ana aikin. Wayar umma ce a hannunshi yana
ta danne danne, ba don nishadi ba don kawai ya
rasa me zaiyi. Dript ya shiga yana ta bin abinda
ke ciki, mamaki ya cikashi lokacin da yaga irin

text din da ummi tasha rubuta mashi don ta tura
ma abba, sai kuma ta fasa. Tamkar cikin mafarki
abba ya rika karanta sakwanin dama ummi tana
sonshi zurfin ciki ne tayi? Ya sake bude wani
rubutu cewa, Ya Abba ina sonka, ina kaunarka
duk wani motsi na numfashina kara sonka nake,
ka tausaya mun sonka zai zama ajalina, duk
ciwon da nakeyi na sonka ne. Ko na rantse ba
zanyi kaffara ba, in kaji haushin kalamaina ka
yafeni, nasan ni ba ajinka bace, amman ka daure
kace kana sona koda bada gaske bane. Gama
karanta sakon yayi dai dai da dawowa da ummi
dakin, da sauri suka nufeta idonta biyu saidai
daga gani tasha azaba. Tayi wujiga wujiga. Abba
ya kama hannunta cikin matsanancin sonta da
tausayi. Sannu suka dinga yimata, nurse tabasu
magungunan da za'a rika bata, umma kuma ta
dauki wayarta don sanar da alhaji an gama aikin.
Abba yasa bakinshi dai dai kunnenta yace ina
sonki ummi, ina matukar sonki. Duk da tana cikin
wani hali taji kalaman nasa har a tafin kafarta.
Ta bude jajayen idonta ta dubeshi, ya sakale
hannunshi cikin tafin hannunta ya hade su. Ta
girgiza kai dai dai lokacin da nurse din ta sake
shigowa tace ga kayanta, ya amsa zaninta ne da
siket da sauransu. Tace ka barta tayi bacci kafin
ta tashi zafin gurin ya ragu, kila zuwa dare a
sallame ku. Umma tace to mungode. Nurse tace
yarinyarki nada dauriya, anyi mata allurar kashe
zafi bata kama jikinta ba amman bata yimuna ihu
ba. Likita ma ya yabata da kokarie ta, Abba ya
kalli ummi cikin tausayi. Sai gurin karfe ukku ta
farka wurin kam ya dan lafa da radadin, abba ne
yaje gida ya dafo masu abinci sannan ya nufi
wurin aikin shi. Don ranar bada wuri zashi ba.
Tunda ummi ta farka take ta kokarie tunowa shin
kalaman da taji cikin mafarki ne ko kuwa ido biyu
ne? Bakwai na dare likita ya shigo ya kara duba
ummi sannan yace suna iya tafia gida. Ya basu
maganin sha sannan yace ta rika shiga ruwan
zafi da dettol. Umma ta kira abba ta fada masu
batun sallama. Yace su jirashi yana zuwa. Ummi
tace da ummansu su alhaji pha? Tace sunxo kina

bacci harda ummanku sahura.els / ZURFIN CIKI book 4 part 28
ZURFIN CIKI book 4 part 28
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:30
Bansan lokacin dana dauka ina rigimniya da sonki
danqare a zuciyata.Ummi da ban sameki ba da
tuni bana garin Kano domin lokacin yanke
shawara nayi in nemi canjin aiki zuwa wata jihar
har yau ban daina yiwa Salisu addua ba wanda
shine mutum na farko da ya soma tsegunta min
kin zama mata gareni So, Ummi baya raina
abinda yake so da nayi zaton zubar da kima ne in
furta maki kalmar so musammam in na tuna ke
baki soma, zurfin a so bashida wani amfani don
na sha wahala.Ba zan Qara boye dimbin son da
nike maki ba Ummi ko gaban wa zan nuna kina
jina matsala? Ummi wadda ke zaton mafarki take
sai taji bakinta yana furta wayyo dadi Ya Allah
kada ka farkar dani in har bacci nike Abba yace
ciji yatsanki zakiji zafi Ummi nine Abban ki mai
sonki wanda ya reneki tun kina zanen gobe.
Hawaye suka soma zubo mata cikin muryar kuka
tace Ya Abba da gaske kana sona? Nafi zaton
tausayina yasa ka furta haka, Amma koba gaske
ba ne na gode kuma naji dadi Amma ka sani Ya
Abba ina sonka mai tsanani sai tasa kuka. Yace
ummi yi shiru, in kukan takaici ne kukan ya kare.
Nima na jima ina sonki jiya naga sakonki a wayar
umma da kike rubutawa mai dauke da nuna sonki
gareni. Sai zurfin ciki ya hanaki, don allah ummi
kada ki koma zurfin ciki a sona, ki zazzage min
duk irin sonki gareni. Ummi tace yau kam ji nake
kamar a mafarki. Sun nutsa a cikin hirar so suna
ta baiwa juna labarin halin da suke shiga a baya,
a lokacin daya ganta da wani namiji yace
hankalinsa yayi mugun tashi. Sai lokacin daya
fuskanci bashir na sonta, ita kuma Tace ta tsani
koh mace ta kira layin shi, zainab kuwa data
samu labarin ta kamar ta mutu. Tace ko bishira
bata kishi kamar yarda take kishin zainab, sunyi
nisa basu san sun kwana zance ba, sai da ummi
taji kiran sallah. Tace ya abba kaji abunda naji,
yace sallah ake kira naji, kin sani kwana zance.
Ban gaji dajin muryarki ba amarya tah. Ummi

tace gari yayi saurin wayewa kaje kayi muna
godia ga allah ta hanyar nafita, yace to matata.
Hamdala ta rikayi har bacci ya dauketa, muryar
umma taji tana cewa ummi ki tashi kiyi wanka ki
gasa jikinki. Tana zaune cikin baho wanda umma
ta zuba ruwan dimi da dettol, tsohuwa ta shigo
cikin bandakin. Ummi tace don allah tsohuwa fita,
tace don allah ja can anki a fita din, ta saka
hannu cikin ruwan wankan ummi dake gefe a
bokiti. Tace ina suwaiba? Ai karo mata ruwan
zafi, wannan ruwa yaushe zata gasa jikinta, idan
da dan tawul dauko in danna mata jikin. Ummi
tace nidai tsohuwa ki barshi don allah, sai kace
wata mai jego? Tsohuwa tace tafi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login