Showing 24001 words to 27000 words out of 30182 words
Chapter 9 - ZURFIN CIKI Book 3 end by halima Abdullahi K Mashi .pdf
dinga
matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan? Amma data
tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.
Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da
darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar
jumma'a ranar zai bar dakin bishira. Ya fito tana
sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,
tare dawani kallo mai fassarar in ba keba. Cikin
muryar data adana don shi kadai tace, ya abba
ina son in je ayi min zanen fulawa. Yace jiya kin
fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen
tazo ta miki. Ta marairaice, towa zan aika yaya
abba? Yace aike ni, ina ne gidan? Tace layin su
umma ne yace to za'azo ai miki. Bishira tafito
daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa
kisisina. Abba yakalleta, kema sai tayi miki. Tace
bana bukata, aikin banza, shikam yafice. Ummi
kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera
tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar
tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.
Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai
dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.
Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan
fa? Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan
bambance miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya,
ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta
dauki nama da bushasshen kifi. Sannan ta hada
musu kunun aya yaji dabino da madara, ta
aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar
na ummarsu. Tasheka wanka taci doguwar rigar
shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau
ne daurin aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya
akazo aka zana mata. Tanajin rigimar muhibba
tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita
akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki
tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda
bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na
turarukan da ummi ta fesa. Abba yana yin
sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,
bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.
Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.
Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa
sannu babyna tace inazan kai ledar? Yace akwai
ta bishira aciki ki ciro. Ta mika mishi ledar ta
wuce dajakar dakinta. Ya mika wa bishira lemo
da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce
danasu, awulakance ta aje. Yana shiga ummi
tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu
sosai ta gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje
akan madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya
masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka
suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.
Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,
wai kamar kada su goge. Kumatun shi ta shafa
nima yau kamin kyau, koda yake dama kai me
kyaune, ina sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi
ya mannota a jikinshi, nima ina sonki, ina manta
kowa da komai in muna tare, tace ina tsoron kada
wata rana ka juya min baya. Ya saqalo
hunnuwansa cikin nata ina fata in mutu kafin
lokacin. Ummi tasomayi masa wasu irin darussa
wadanda tasan yana saurin tada sha'awarshi
nanda nan kuwa tasa shi fita hayyacinsa yakama
surutai. Ummi ta tabbata bishira tana wurin ta
labe, don haka tai murmushi ta bishi suka tafi
duniyar ma'aurata. Bishira tamkar tayi hauka sai
kawai ta fado dakin tana fadin, maciya amana,
har yanzun ba afita daga lokacin girkina ba
munafiki. Abba ya tashi sannan yaja riga yasaka,
ok dama kina labewa ne kiji sirrinmu? Da taga ya
sauko da zafin rai saita gudu dakinta. Yabita
yamata tatas, kuma ya fada mata cewa tazo ta
shiga dakin ta zauna ba labe ba, yanzun zai
komane yaci gaba daga inda ya tsaya. Tayi ta
kuka gashi ba damar zuwa gurin umman bashir
dole ta tafi gidansu. Shi kam abba shareta ya yi
kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar soyayya ma
ya balle agidan, su ci abinci tare, wanka tare, su
fita yawonsu a qafa ko amota. In yana gurin aiki
bini- bini ya kira waya, ita kuma ko yaushe cikin
kirkirar girki da kwalliya tare da dadadan kalaman
dazata fada masa take. Duk lokacin datayi masa
zancen bishira sai ya ce, don Allah ta bar ta ta
huta, ummanshi kuwa 'yar bin qwaqqwafi sai da
tabi ta gano bishira bata nan. Don haka koda ya
shiga gaisheta sai tace kada ya yarda yaje yama
bata takardarta. Ita ko tana can uwarta tace ma
mahaifinta abba sakinta yayi, shi kuma yace to
sai tazauna tunda zaman gidan take so. Amma
su sani daga abinci sai ruwan gidanshi ya amince
tayi amfani dasu sai ko gurin kwana, amma bnda
wannan ko makilin dinshi ta taba bai yafe mata
ba, wannan hukunci yayi musu tsauri. Ko wata
bata rufa ba taji gidan ya isheta don hajiya zainu
taso maidata makaranta amma yace tagama
boko. Bishira na zaune ta zuba tagumi hajiya
zainu ta shigo dakiki tace tagumin menene kuma?
Tace, su sumayyah ne wai nace suyi ma muhibba
wanka sukace Allah yakiyaye. Wai tunda nazo
dakinsu ya lalace da kazanta, hajiya zainu tace
aiba karya suka yiba, don haka ma maida
yarinyar nan za ayi ke kuma ki koma gidan
antynku ko ki tafi abuja gidan aisha. Tace
baxanje gidan aisha ba, don itama bama shiri,
gara gidan antyn amma gsky ni abarmin 'yata
kuma fakinsan bai sakeni ba. Tace, inda ubanki
yasan ba saki bne da tuni bai kora kiba? Don
haka mubarshi haka amma batun 'ya nice zan
maidata. Ranar da ummi takira ummansu tafada
mata cewa bishirafa tuntuni tayi yaji amma Abba
yaqi zuwa, umma ta kira shi tace inya dawo gurin
aiki tana son ganinshi. To kafin yadawo ma saiga
hajiya zainu da direba tazo gidan su umma tadire
musu 'yar, sannan tashiga gidan umman bashir
tace, in kin haifi danki na halas ne ba shege ba to
kisa shi ya aiko wa 'yata saki. Umman tace zoko
kiga dan halas ne in yaso kuje ku nemi arne mara
sallah dan uwanta kazami kubashi. Nan fa zage-
zage ya tashi har su umma dasauran makota
suka shigo. Dakyar aka tura hajiya ta tafi, tace
kuma saita kira 'yan sanda anzo antafi da umman
bashir. Alhji qarami ma cewa yayi maza abba
Abba yarubuta takarda ya aika ma bishira.ZURFIN CIKI book 4 part 32
ZURFIN CIKI book 4 part 32
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:37
Shiko alhji babba da umma suka ce a'a abari
qura ta lafa sannan aje. Koda aka kwana 2 abba
kin bin alhaji yayi sai wani abokinshi alhaji
yasamu suka tafi tare. Mahaifin bishira yaji
mamaki cewa ba sakinta abba yayi ba. Kuma bai
san sun maida 'ya ba, tadai ce mishi kunzo kun
amshi 'yarku, to yanzun tunda haka ne kunga
kenan bishira da uwarta basa son takoma gidan
mijinta ko? Su alhaji suka ce eh, yace to ku sa
shi ya rubuto takardarta ku kawo min, su alhaji
sukace ba za'ayi haka ba. Yace, to kuje ku barta
zata gane gidan ubanta bananne yadace tazauna
ba. Sukai godiya suka tafi. Harta koma gidan
anty farida mahaifinsu yace tadawo nan gidanshi
badashi take takama ba? Wato ta kashe auranta
zata je ta kashe na yarta dole ta dawo, tsohuwar
dake musu aiki yace ta koma gida tahuta amma
duk wata tazo ta amshi albashinta. Sannan yace
bishira itace zata dinga wannan aikin duka ita
kadai, lamarin yayi wa bishira tsauri da yawa,
gashi ba fita duk ta rame ta lalace ga tunanin
'yarta. Muhibba kuwa tana gurin umma, ummi
ma takan daukota sannan ummi tasamu nasarar
rufe bakin umman bashir, ta hanyar yi mata
kyautuka ko me sukace sai ta aika mata. Tasa
Abba ya canja mata gado don nata ya lallace,
sannan da fati ta haihu tasa Abba ya sai mata
garar abinci, ita kuma tasa zani da rigunan yara.
Nan fa sai ga sahura babu ko kunya tana shima
ummi albarka, ko bashir ne yakawo gulmarsu
ummi sai tace ai ita bata yo halin uwarta ba.
Tafi-tafi ma in ya kawo sai tace ai su umma da
ummi sun gane kuransu. Haba sahura kodai ki
gane kuranki? Abba yasoma damun ummi da
batun ciki, wai shifa yana tsoro kada su gaji su
umma, ummi tace su dai yi addu'a sunje asibiti
ba wata matsala, likita yace in rabonsu yazo zasu
haihu. Da kyar ummi ta shawo kan Abba ya
amince ta zana (JAMB) don ci gaba da karatu,
sannan ta shiga islamiya. Abba yayi kyau yayi
kiba ya kara gogewa, haka nan ummi duk wanda
yaganta saita birge shi, daka ganta kaga wayayya
wadda mijinta yasan da ita. Taci nasarar samun
(POLY) saboda bata samu abinda take so don
zuwa (UNIVERSITY) ba, sai dai ba tasha dokoki
kafin ta fara zuwa. Bayason kawaye baya son
abokai, irin wanda wasu matan keyi sannan
yadinka mata manyan hijabai, kuma banda hawa
acaba, inya samu sarari zai dinga zuwa da kansa
yana daukarta. Sai kuma gargadi na karshe kuma
da babbar murya, in har ya daina samun kular
datake bashi ta kowane fanni wai saboda karatu,
to kuwa za adaina karatun gaba daya. Tace,
insha Allah sai abinda yai gaba. Ya canja mota,
umma tayi ta fada wai tafi son yasai fili yayi dan
gidanshi irin na zamani yace za'azo gurin
ahankali kada ki damu umma. Bishira ta sulale ta
tafi na'ibawa gidan anty da kukanta wiwi don
Allah ta taimaka mata taba Abba hakuri ya maida
ta, wlh tagane kuskurenta. Anty tace, nifa bazan
iya kiran Abba ba don kin riga kin bmu kunya, sai
dai in ke ce zaki kira shi ga waya can. Ta dauko
ta kira, shikuma ganin kiran anty sai yayi parking
yadauko ummi daga makaranta, ya daga sai yaji
muryar bishira. Cikin kuka tana cewa, don Allah
abba nice, kayi hakuri indawo dakina, wallh zan
canza, yace ok baki riga kin canza din ba, to bari
inkin canza din sai muyi magana. Yakashe haka
tayi ta kuka tagama anty tabata wasu kayan
sawanta sannan ta tafi. In lokacin labarai yayi
haka take zuwa ta tasa TV tayi ta kallonshi tana
kuka, kullum kara sonshi take gashi yayi kyau
idanunshi sun qara haske. Wata ranar jumma'a
wuraran karfe sha daya ta saci jiki tanufi gurin
aikin Abba, yana fitowa dakin daukar labarai
akace wata tana nemanshi. Baiji wani mamaki ba
don mata kanzo neman shi wasu suce suna
sonshi wasu suce ganinshi kurum zasuyi don
yana birge su. Yana zuwa sai yaga bishira, nan
take ya daure fuska tamkar bai taba dariya ba,
duk da cewa acan kasan zuciyarshi yatausaya
mata. Ta tsugunna gwuiwa 2 tana rokonsa, yace
ke tashi kada ki janyo min mutane, jeki zanzo.
Koda ta tafi cikin murna shi ko harkokinsa
yakama. Shiru-shiru tana saka rai bashi ba
alamarsa. Nan kuma tashiga daukar waya
kannanta tana kiranshi, harma yadaina dagawa.
Wataran taje tasamu ahmad tana kuka, ahmad
yace taje zai ganshi. Rannan kuwa har gida
ahmad yiyi sallama da abba yashiga rokon Abba
ya maidota. Abba yace taje taroqi mahaifiyarsa
dasu umma insun yarda shikenan. Har gida
ahmad yaje ya fada mata, bata yi sanyi ba tanufi
gurin umman bashir. Umman tana zaune da
'ya'yanta suna shan farfesun kifin da ummi ta
aiko musu dashi, tana ganin bishira ta hade rai.
Tace, lapiya? Bishira tace lpy lau umma zuwa
nayi in roqi gafararki. Tace nime kika min? Tace
don Allah dai ki yafe ni, ina son indawo dakina
Abba yace sai kin hakura, tace oho, yanzun kin
yarda ina da kima agurinsa? To bari kiji bazaki
dawo ba, mai baqar rowa kince nimai kwadayi ke
kuma mai rowa ko? To kin gani wannan ummi ce
ta dafo mana ta nuna mata kular kifi, sanda
kinanan bana cin komai bansan dana yana samu
ko baya samu ba. Yanzun abin arziki iri-iri
kidawo ki toshemana kofar samu? Tace, wlh
bazan toshe ba, umman bashir tace dukda haka
dai bazaki dawo ba. Tayi takuka sannan tafita,
har zata wuce gidan su ummanshi sai ta tuna
kada suyi mata dariya sai tace baridai ta shiga.
Kyakkyawar karba umma tayi mata suka gaisa,
tazauna umma ta kawo mata ruwa ta amsa
tasha. Muhibba tana ta tsalle tsallenta kan kujera
zuwa jikin umma, umma tace ji hibba ki gaida
mamanki, ga mamakin bishira sai yarinyar ta
kalleta tace. Umma niba wannan bace ba
momina, momina sun tafi da babana zaya kaita
makaranta. Umma tace, wannan ma ummarki ce
yarinyar taruga dakin tsohuwa tana cewa, ita ba
ummarta bace. Bishira ta bita dakallo, yarinyar
tayi bulbul gata cikin shiga mai kyau da tsafta
kanta yaji kitso da 'yan duwatsu. Saita soma
kuka tana fadin mahaifiyata ta cuce ni, umma
tace a'a kece kika cuci kanki, inbaki dauki
damuwarki kin kai mata ba yaushe zatasan anyi?
To ynzun dai dubi 'yarki tana gudunki sbd bata
sanki ba, ina amfanin wannan? Tsohuwa tace
kukan wanikeji ta shigo tana kallon bishira cikin
mamaki tace. 'yar nan kece haka? Ciwo kikayi ko
ko duniya ce ta juya miki baya? Kai jama'a dubi
yanda kika kare kikayi bikinkirin. Ita da tadukar
dakai tare da cewa bnyi ciwo ba nidai nazo ku
yafe ni, sannan ku roqa min abba ya yafe min in
dawo dakina. Yace, bazan dawo ba har sai kun
yafe min, amma naje gurin umman bashir ta kore
ni tace bazata bari in dawo ba. Kuma gidanmu
wuya nake sha, kusan rabin aikin gidan nikeyi ga
qannaina duk sun raina ni. Umma tace, yi shiru
share hawayenki bari zaki koma. Tsohuwa tace,
ke dai kin cika sa kai a uku suwaiba, gashi abin
kirki bai karbe kiba. Kina yi ana zaginki ana zagin
'yarki, bishira ta ce wlh duk na daina, yanzu na
gane kune masu sona, umma tace ba komai.
Tadaga waya ta kira alhaji ta fada masa komai
yace to yana zuwa donshi ya qosa asulhunta
yarinyar ta koma dakinta saboda darajar
tsohonta. Yana zuwa yaji komai nan ya daga
waya yakira Abba, yace yana zuwa yana hanya
ne yace to ya same su gida. Abba yana shigowa
ganin bishira yahade rai ya zauna nan dai alhaji
ya hada su yayi musu fada da nasiha, sannan
yace baya son abba yace komai komai kuma ko
sun koma gida banda tashin tashina. Bishira tayi
ta godiya alhaji babba yace su tashi ashiga gurin
umman bashir din tana ganinsu tahau cewa alhaji
dakanka? Maimakon ace in zo? Umma tace, a'a
keda zamu zo baki hakuri ai mu ya dace mu
shigo. Nai dai alhaji yayi bata hakuri tace taci
albarkacinta na hakura, amma da sharadi inta
sake maimaita halin da tayi abaya ko taje ta
takurawa ummi tofa saita tabar gidan. Bishira
cikin kuka tace ta daina insha Allahu, nan itama
umman bashir din tace dasu umma su yafe mata
sharrin shaidan ne da qaryar barayin imani wato
bokaye da 'yan tsibbu suka ce ba komai. Nan
alhaji yace da abba yakai bishira gida, ba don son
ranshi ba yadauke tazuwa gida, sam bata damu
da daure fuskarshi ba, dadi da murna fal ranta.
Yana sauke tazai wuce tace, don Allah ka yafe
min sannan ka gaida min ummi, yace zataji. Tace
to yaushe zan dawo? Yace, duk lokacin dasu
alhaji suka zo gurin dadynku. Nan yatafi, ita
kuma ta shiga gida, hajiya zainu ta tsareta wai
sai ta fadi inda taje, tunda ta kira anty tace, bata
can. Bishira tace naje ba mijina da surukaina
hakuri ne, hajiya zainu tace ni dazai maida ki ai
sai nafi kowa murna. Na gaji da zamanki da
qazantarki, tunda babanku yaqi ki koma
makaranta yakashe miki kudi ki goge ko kya
samu mai kudin dazai aure ki, to gara kin koma
can kin qarata. Abba kam shi tunaninshi ta ina
zai soma sanar da ummi dawowar bishira? Don
baya son ko kusa hankalinta yatashi, baya son
wani abu yayi musu katsalandan a cikin
daddadan zamansu, don haka ya share bai fada
mata ba. Da dare alhaji da umma suka je, an
sasanta sannan suka taho da alkawarin cewa
gobe zata dawo dakinta. Washegari umma ta kira
Abba tace ya share ma bishira daki yau zata
dawo, yace umma nifa gsky dabata hankalina yafi
kwanciya. Sannan ina ta tunanin yanda zan
tunkari ummi da wannan zancen, umma ta riqe
baki tare da rafka salati, yace ynzun tsoron
ummin ka koma ne? Yace, a'a umma kin gata
sakankance ynzun hankalinta yakwanta sai kuma
taji nazo mata da zance dawowar bishira? Tace,
shi kenan nina fada mata. Awaya ta kira ummi
tafada mata cewa bishira zata dawo, duk datasan
cewa matar mijinta ce dama, amma sai da
gabanta yafadi. Umma taja mata kunne da cewa
kada taji kada tagani, abba ranar sai kusan sha
biyu zaije gurin aiki. Don haka yace kannanshi
suje su soma fito da kayan kafin yazo sunzo sun
fada ma ummi, ita ce ta bude musu dakunan don
abba ya canza makulli bayan tafiyar bishira. Abba
ya shigo tana zaune kan kujera sai tunani take yi
na irin zaman dazasu yi in bishira tadawo.
Yazauna