Showing 12001 words to 15000 words out of 30182 words

Chapter 5 - ZURFIN CIKI Book 3 end by halima Abdullahi K Mashi .pdf

da bayan hannu,
kalmar da ya tsana kenan, zafi yakeji a Zuciyarshi
ko tunowa yayi da ummi bata sonshi. Daki ummi
ta fada, ta fada kan gado tana kuka, ya kalli
bishira kije gidan ku sai nazo, umman bashar
tace ba inda zataje kuma in ka sake na samu
labarin ta tafi saina debe maka albarka. Tasa kai
fuuuu ta fice, tunda ka dauki hukunki mai kyau ka
duki marar kunya ai naji dadi. Bishira ma taji
dadin haka, Shi kuwa ba don su yayi ba zafin
furta bata sonshi ne yasa ya daketa. Yana shiga
dakin ummi lokacin ta mike tana kuka, ta dauko
zane ta daura tana kuka sosai. Ta zari hijabi ta
zura zata fita, yace ina zaki? Taki sauraronshi
zata fita ya rikota, ina zaki nake? Tayi magana
cikin daga murya cikin muryar kuka tace gidan
ubana kai kuma ka zauna da warda kakeso,
tunda ya mareta nan ya gane bai kyauta mata ba,
don yasan ba dole bane ta fahimce Shi, sai ya
samu kanshi da jawota ya rungume. Duk da suna
cikin bacin rai Duk kansu saida sukaji wani irin
yanayi. Yace kada kiyi yaji ummi kinsan dai koh

kinje su umma fada zasu maki. Cikin sanyin
murya yayi maganar, kan ummi ya sara, ta kwace
daga jikinshi ta sake fadawa kan gado. Sabon
kuka ta saki, ya zauna bakin gado ya kamo
hannunta ta sarke ya tsunshi da nata ya dan
matsa, ummi! Ummi!! Tashi kiji, cikin kuka tace
mi zanji yaya Abba, kawai ka rabu dani, ni baka
man adalci ba. Ya za'a yi kaje kana fada mata ni
baka sona kasa tana man gori, umman bashar
harda ceman wai ni nabi maza. Ya sake kwantar
da murya yace ki yarda ni ban fadama bishira
cewa bana sonki ba, kuma batun umma kisashi a
gefe kawai don ni nafi kowa sanin halinki. Nafi
kowa sanin tarbiyar umma na... Duk da haka ai
baka kare kanka ba lokacin da take fada ba,
ummi ta katse kiran da yake mata, yasan ummi
sarai yanzu kam bazata saurari komai ba, koma
ta saurara zata ta kalubatanshi ne, don haka sai
yace to Tashi ki bani abinci. Kin Tashi tayi don
kanta jinsa take kamar ya fado, mi kewa yayi ya
fita, ya rasa sukuni, koda yaje shago kasa yin
komai yayi, sai murza hannunsa da ya mari ummi
yake. Ya ciro wayarsa ya kira ummin tayi ta
ringing kusan sau 3 kafin ummi ta daga yace
haba ummi, inata kira kayi banza dani? Shiru dai
tayi bata tanka ba, ummi cikin disashiyar murya
tace, dama haka ne, sai an kwance ma mutum
zane kasuwa azo gida ace za'a daura masa. Sai
ta kashe wayar. Daga nan gidan umma ya nufa,
tace anya Abba lafiyarka kuwa? Naga Duk ka ya
mutse. Ya zauna suka gaisa yace umma ina fa
lafia, dazun bayan sallar jumma'a ina iso wa gida
da yunwa sai kurum na samu gidan tam d
jama'a. Ummi da bishira na tarar suna ta zage
zage har aka samu wata shedaniya taje ta kira
umman bashar. Umma tace subhanallah! To ya
akayi yanzu? Yace tarwatsa taron nayi, nasan
koda ban tsaya bin bahasi ba ummi ce mai
gaskiya. Domin bata kula bishira, Duk yarda akayi
ta kure ta ne. Tsohuwa daga can gefe tace, wai
bayan zuwa na gidan sukayi fadan? Abba yace
oho ni ban masan mafarin fadan ba. Umma tace
kai wannan abu allah ya dai dai ta maka su.

Amman kyanshi kana zuwa ummin ya kamata
kayi wa fada, koma ka zane ta, don itace karama.
Abba har suna hada baki da Tsohuwa gurin fadin
"Haba dai". Abba yace umma in itace da gaskiya
kuma ai na zalinceta, yanzun da haka fushi take,
Duk na tsorata bana son fushinta, sai taki cin
abinci. Don allah umma bari in kira maki ita ki
bata hnkr, umma tace ba zan bata hnkr ba, abinci
kuwa kada allah yasa taci. Sai dai ayi tunanin
abinda ke cikin ta, Tsohuwa tace, wannan
sakaryar matar taka dama na lura fada takeji.
Sanda nayi sallama tana zaune amman amsawa
ta gagareta, don haka ma ko gaisheta banyi ba
na wuce. Ita kuma takwara ka hanata saka
wadannan kayan na arna. Abba yace, su ake yayi
Tsohuwa, Tsohuwa tace, tafdi lallai yayi ya zama
banza. Abba yake cewa Don allah umma ga nmbr
bari in saka maki a waya, ya dauki wayar umma
ya saka mata lambar wayar da ke hannun
ummin, yace umma na roke ki lallasheta ba wai
fada zaki mata ZURFIN CIKI book 4 part 17
ZURFIN CIKI book 4 part 17
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:17
Duk jumma'a abba yana dawowa gida
musamman in ranar girkin ummi ne don cin
abinci na musamman. Jumma'a biyu kenan bata
fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
tsohuwa tazo. Don haka suna gaisawa da umma
tace gurin tsohuwa nazo. Suka shige daki tace da
tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
Tsohuwa tace, name ummi? Ta ce na gyaran jiki
mana. Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
abubuwa. Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
bada ina fada miki kina sharewa ba? Ummi tace
haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
hankalin mijina. Ta ce, toda farko ki dinga kula da
jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
iska. Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da

ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi. Sannan ki
amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
matsa farin miski a ehem dinki. Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma. Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha. In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata. Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi. Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan? Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu. Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan? Tun ranar
alhamis din ta soma aiwatar da darussan da ta
debo daga tsohuwa, safiyar jumma'a ranar zai
bar dakin bishira. Ya fito tana sharar tsakar gida
ta gaidashi, ya amsa da fara'a, tare dawani kallo
mai fassarar in ba keba. Cikin muryar data adana
don shi kadai tace, ya abba ina son in je ayi min
zanen fulawa. Yace jiya kin fita yau kam a'a.
amma ki aika akira mai zanen tazo ta miki. Ta
marairaice, towa zan aika yaya abba? Yace aike
ni, ina ne gidan? Tace layin su umma ne yace to
za'azo ai miki. Bishira tafito daga daki tazabga
ma ummi harara, Tare dacewa kisisina. Abba
yakalleta, kema sai tayi miki. Tace bana bukata,
aikin banza, shikam yafice. Ummi kuwa tace gaba
da aikinta, ita ko sai tasa kujera tazauna tana

sakin zantuka, eh don kwalliyar tabanzanta tunda
ba a iya biyawa miji bukata. Allah dai yasa ya
fada min komai, to ni me zai dame ni don 'yar
aiki kawai na dauki yarinya. Tashare min gida,
tayi wa mijina abinci, daga nan fa? Saita saki
shewa, ummi ta ce aranta yau zan bambance
miki. Birabiskon shinkafa tayi da miya, ta wadata
birabiskon da kayan lambu, miyar ta dauki nama
da bushasshen kifi. Sannan ta hada musu kunun
aya yaji dabino da madara, ta aikawa ummanta
lokacin da kamal yazo daukar na ummarsu.
Tasheka wanka taci doguwar rigar shadda koriya
mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau ne daurin
aurensu. Ga fulawar da yaje ya biya akazo aka
zana mata. Tanajin rigimar muhibba tafito tazuba
mata adan kwano tazaunar da ita akofar falon
mamanta. bishira tafito kicin baki tasaki tana
kallon ummi da tazo wucewa harda bangazar
ummi, nan ko kamshi ya bude ta na turarukan da
ummi ta fesa. Abba yana yin sallama ummi tafito
da sauri, oyoyo yayana, bishira tana daga kicin
dinta tana kallon su. Ummi ta rungume shi,
sannu dazuwa sahibina. Ta amshi ledar
hannunshi dajakar, yace yauwa sannu babyna
tace inazan kai ledar? Yace akwai ta bishira aciki
ki ciro. Ta mika mishi ledar ta wuce dajakar
dakinta. Ya mika wa bishira lemo da abarba da
yayo musu tsaraba sannan ya wuce danasu,
awulakance ta aje. Yana shiga ummi tadan karo
kofar yanda bishiran zata iya lekensu sosai ta
gefen kofan. Ta cire masa hula ta aje akan
madubi sannan ta kunna fanka. Ta shirya masa
abinci, yauni zan baka har ka qoshi. Haka suka
yita baiwa juna abaki har suka qoshi. Yakamo
hannunta mai qunshi yana ta sumbata, wai kamar
kada su goge. Kumatun shi ta shafa nima yau
kamin kyau, koda yake dama kai me kyaune, ina
sonka ya abba sosai. Cikin jin dadi ya mannota a
jikinshi, nima ina sonki, ina manta kowa da komai
in muna tare, tace ina tsoron kada wata rana ka
juya min baya. Ya saqalo hunnuwansa cikin nata
ina fata in mutu kafin lokacin. Ummi tasomayi
masa wasu irin darussa wadanda tasan yana

saurin tada sha'awarshi nanda nan kuwa tasa shi
fita hayyacinsa yakama surutai. Ummi ta tabbata
bishira tana wurin ta labe, don haka tai murmushi
ta bishi suka tafi duniyar ma'aurata. Bishira
tamkar tayi hauka sai kawai ta fado dakin tana
fadin, maciya amana, har yanzun ba afita daga
lokacin girkina ba munafiki. Abba ya tashi sannan
yaja riga yasaka, ok dama kina labewa ne kiji
sirrinmu? Da taga ya sauko da zafin rai saita
gudu dakinta. Yabita yamata tatas, kuma ya fada
mata cewa tazo ta shiga dakin ta zauna ba labe
ba, yanzun zai komane yaci gaba daga inda ya
tsaya. Tayi ta kuka gashi ba damar zuwa gurin
umman bashir dole ta tafi gidansu. Shi kam abba
shareta ya yi kosu umma bai fadawa ba. Sabuwar
soyayya ma ya balle agidan, su ci abinci tare,
wanka tare, su fita yawonsu a qafa ko amota. In
yana gurin aiki bini- bini ya kira waya, ita kuma
ko yaushe cikin kirkirar girki da kwalliya tare da
dadadan kalaman dazata fada masa take.ZURFIN CIKI book 4 part 18
ZURFIN CIKI book 4 part 18
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 02:19
Ummi tayi alalar gwangwani ta sauke kenan sai
ga aunty farida da yake tunda akayi auren ummi
batazo gidan ba. Har daki ummi ta shiga suka
gaisa tayi masu addu'a zama lafia, tayi mata
nasihar zama da miji. Umman taji dadi tare da
kwadayin ina ma bishira take da halin yayarta, ta
zuba alala ta kaima aunty falon bishira. Ta isko
su tana mata fadan kaxanta, cikin murna aunty
ta anshi alalar taci bishira ta cika fam. Tun tana
jurewa har tace aunty ai kin zubar min da kima,
ya ya za'a yi ki anshi abun kishiya kici. Aunty ta
kalli bishira fuska daure tace ke da ita akwai
bambamci ne? Bishira tace aunty bambamci ma
nifa jininki ce ita fa? Aunty tace a musulunci fa?
Bishira ta hade rai tana kallon aunty, taci gaba
da cewa, A musulunci tama fiki don tana sallah,
Haka nima ina sallah, kefa kin faru? In kin soma
sallar to kin shigo cikin mu ni da ita. Domin
addinin mu ya nuna muna dukkan musulmi dan
uwan musulmi ne. Inji mai tsira da aminci. Haka
zan iya cin abincinta banci naki ba don bakida

tsafta. Ta daka mata tsawa tashi don allah
malama kije kiyi wanka, ki wanke duk jirwayen
nan naki kafin In daukeki da motata. Da zasu tafi
har kudi aunty farida taba ummi, ummi kam
godiya ta dinga yi. Haka nan da abba ya shigo ta
nuna masa tace ai abba ya ciri tuta a zuri'arsu,
halin mahaifinsu ne da ita. Wata rana aunty ta
bugo ma abba waya cewa aisharsu ta haihu don
allah ya fadama bishira koda ya iso gida ya fada
mata nan ta shiga murna. Washe gari tace zata
gida tama mahaifiyarsu barka. Sannan taji randa
zasu abuja wurin aisha. Yace ta shirya ya
sauketa, ta samu aunty tazo nan dai sukeyi wa
juna barka, mahaifiyarsu tace dubi yar uwarki sai
yanxu ta haihu gwanin shawa. Amman kinje kin
gwarje miji ma yayi maki kishiya, dubeki kamar ba
yar gidan nan ba. Aunty tace mummy ai ita taso
ta zama Haka, tunda kaxanta ce sana'arta.
Hajiya zainu tace ni wani lokacin bana ganin
laifinta a kaxanta, don a gida bata saba aiki ba.
Laifinta daya a gurina wannan abba data nace ta
aura, data tsaya ta gama karatunta ta auri wanda
zai dobo mata yan aiki komai saidai ayi mata
tana daga zaune, amman ta likema talakan tela
wanda bashida ko sisi. Aunty ta katse mamarsu
da cewa In tana da yan aiki shine har wanka
zasuyi? Ta cire dan kwalin dake kan bishira kalli
fa mummy har kanta zasu wanke mata. Mummy
tace aiki gida ya mata yawa, yaushe har ta gyara
jikinta? Aunty tace kawai mummy kina goyon
bayanta ne. Bishira tace aunty mummy ta
fahimta kece baki fahimta ba saboda kina da yan
aiki. Mummy tace duk ba kece kika yima kanki ba,
ga kishiya an maki, bishira ta tabe baki nima duk
nadama ta isheni. Kuma shi da matar duk bana
raga masu. Don ban damu ya sakeni ba, yaji ne
dai nace na daina, daddy ko nazo cin mutuncina
yake gabansu. Mummy tace kin man dai dai.
Haka yake bishira kullum cikin tsokanan hayaniya
da ita da miji ko kishiya. Amman ummi yamxun
bata kulata Domin umma ta gargadeta. Bishira
bata bar gidan ba saida mummy ta zugata
Sannan tace mata jibi kizo za a kai su innarku

yin barka abuja kije ki dan huta kafin suna.
Bishira tace daman ban taba zuwa ba, ko anyi
suna sai na huta. Aunty tace kada ku yanke
hukunci ba tare da sanin mijinki ba kije kiji ta
bakinsa. Bishira ta ce ina ruwana da yardarsa
aunty. Haka kuwa data dawo ta shiga tattaro
kayan ta dake jibge a gefen gadonta, don ita zane
ko yau a aka dinka shi In tasa ta cire duk In da
tayar kafin ta dauke shi yaji jiki. Wani ma saita
goge ruwa ne, kamu ne, duk kyan zani saita goge
tsakar daki dashi. Ranar dama abba dakinta
yake, tace mashi jibi zamu abuja Inji mummy.
Taso ya dan sai mata zani sabo wanda zata
danci suna ya dinka mata. Yace akwai wani leshi
dan sai maku yana shago, Tun wancan satin
naso In zauna In dinkashi da kaina don mai tsada
ne. Tace nawa ka siyeshi, yace dubu biyar ko
wane daya, bishira ta tabe baki. Na zaci zakace
sha biyar wai dubu biyar, yace matsalata da ke
rainuwa yace bari zansa a dinka maku gobe ashe
sunan har yazo? Tace a'a jiya pha ta haihu, ya
sake kallonta jiya? Shine zaku tafi jibi? Tace eh
mummy ce tace mu tafi jibi. Yace a'a kibari sai
ana gobe suna kije. Kafin lokacin ma na samu
wasu kudi da nike sa rai. Sai na sai maki kayan
barka zanen maman da kayan baby. Bishira ta ce
gaskia gobe zamu tafi, In ka sayi kayan barkar ka
aika dasu can wurin mummy yan tafiya Ranar
suna su kai mata. Abba yace nifa ban amince da
tafiyar nan gobe ba. Ban yarda ba. Bishira ta ce
ba wai ina neman yardarka bane, ina fada maka
umurnin da mummy ta bani ne, ko ka mance
mahaifiyata ce? Mamakinta ya cika abba, yace
mahaifiyarki ita zata baki izinin tafiya ko ni?
Umurnina da nata yanzu wanene...? Bishira ta
katseshi kada kayi ganganci hada kanka da
mahaifiyata, ita ta haifeni ta raineni har ka ganni
kace kana sona Sannan ka dinga kokarin
kwatanta kanka da ita? An fada maka kowa
baisan darajar mahaifiyarsa ba irinka? Abba ya
mike ni ne bansan darajar mahaifiyata ba? Tayi
shiru yace nagode Kuma suna na hanashi ma
gaba daya. Zan gani Kuma Bishira ta ce zako ka

gani.ls / ZURFIN CIKI book 4 part 19
ZURFIN CIKI book 4 part 19
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:14
Duk ummi tana jiyo su amman bata fito ba, tana
ta mamakin yarda bishira batasan darajar
aurenta ba, bare tasan girman miji. Ranar da
zasu tafi kuwa ko a jikinta ta dibi tsummanta ta
nufi gidan su, Duk ta fadama mummy yarda
sukayi. Mummy tace kinman dai dai talakan
banza shine zai hada kanshi dani, tafiya zakiyi in
yaso in kika dawo ya ce baya auren. Abba ya
dawo ya samu dakinta a rufe, ummi na daka
sakwara a kofar dakinta yace ina bishira? Ummi
tace ina ga ta fita, don ina daki bansan fitarta ba.
Ya daga waya ya kira aunty yace bishira tazo?
Aunty tace bata fada maka zasu tafi abuja bane,
Abba yace ta fadaman amman nace a'a sai ana
gobe suna zataje, ya kwashe komai ya fadama
aunty. Aunty tace kayi hnkr don allah idan ta
dawo da kaina zan hadata da daddyn mu, Abba
yace kiyi hnkr aunty na gaji da halin bishira inga
wannan karo gwara kowa ya huta ni da ita. Aunty
tace kayi hnkr Abba yace sai anjima ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login