Showing 27001 words to 30000 words out of 30182 words

Chapter 10 - ZURFIN CIKI Book 3 end by halima Abdullahi K Mashi .pdf

tare dariko hannunta, tunanin me ki ke
yi? Takalle shi, halin rayuwa nake tunani, yace
yanzun umma ta kira ni jiya sun je gidan su
bishira wai yau zata dawo. Ummi ta taba baki,
Allah yakawo ta lpy. Ya ce ni ban soba gsky. Sbd
ke ummi tadafa kirji, sbd ni? Ni ya abba, kada
kasa duniya ta zage ni, Tare fa nasameku? Yace
to ni dai kada kiga kamar da son raina, tace don
Allah ya Abba kabar zancen nan. Kaje kagyar
mata dakunanta don su kamal bazasu iya ba,
yanufi gurinsu ganin kamar ya damu yasa itama
taje tasa musu hannu don dai ya saki ranshi, sun
gyara tsaf ummi ta goge sannan ta rufe dakin.

Har magriba bishira bata ji an ce za'a maida
taba, sai ta dauki wayar kanwarta ta kira shi wai
yazo don Allah yadauketa. Tsakanin mata da miji
sai Allah, nan ya tausaya mata yace zaizo, kafin
ya isa sai daya sai mata waya irin dai ta hannun
ummi. Har cikin gidan ya shiga suka gaisa da
babanta, yayi murna sosai yayi tawa Abba
godiya, tare da ba shi hakuri yace yasan yanda ta
horu zai gata canza da yardar Allah. Yasa aka
turo ta yayi mata nasiha, sannan ya gargadeta da
cewa inhar ta bari mijinta yakawa kararta zatayi
mamakin abinda zai mata. Tace, insha Allahu
baza ta kara ba, yakawo kudi yaba Abba, da kyar
ya amsa ita kuma ya bata wasu zannuwa acikin
leda, yace su raba da abokiya zamanta. Taje tayi
wa hajiya zainu sallama suka tafi, tamkar
baquwa haka ta koma, sai kace basu taba zaman
aure da Abba ba, nauyinsa take ji. Suna tafe ya
ciro waya ya miqa mata, tasa hannu ta amsa
yace taki ce, tayi ta godiya yace ba komai.
Sallamarsu tasa gaban ummi faduwa, ta dake ta
fito ta amsa, wani kishi ya tasho mata amma
saita danne. Ta kalli bishira tare dayi mata sannu
dazuwa, ta amsa tana kallon ummi tayi kyau
tagoge daga ka ganta kaga wayayya 'yar gatan
miji. Ta dauko makullin dakin ta ba bishira, abba
kuma ya nufi dakin ummi. Bishira ta dinga kallon
yanda abba ya gyara gidan yaja gini ta gefen
ummi yayi mata falo da kicin, sannan tsakar
gidan an gyare shi da tiles. Haka bandakin su
yagyara shi, nan dai bishira ta shiga dakinta ta
zauna bakin gado tana yi wa allah godiya tare
dayi wa kanta alkawarin har abada bazata ta
kara yin yaji ko ta janyo abinda zaisa mijinta ya
sake ta ba. Ummi tana kan gado tana karanta
wani littafi yazo ya zauna bakin gadon bata ko
kalle shi ba don haushi take ji. Sai take ganin
kamar rawar kai yake yi da dawowar bishiran,
kuma tuntuni yana zuwa gurin ta ya boye mata.
Yace madam ina son in yi magana da ku ne ke da
bishira, ummi tace ina jin ka, yace can zaki zo
muje. Tace, gsky nagaji, kayi maganar da safe.
Yagama gano kishi ne ke damunta, don haka yayi

murmushi yace yanda kikace hakan za'ayi. Ya
fita kamar minti 30 yasake shigowa ya aje mata
leda tare da cewa saida safe aciki tace Allah
yabamu alheri. Yana tafiya taje ta banko kofarta,
yau kam bacci ya qi idanun ummi sbd tayi sabon
bacci a haqarqarin Abba. Dukkan filolinta ta rasa
wanda zai maye mata madadin haqarqarin
mijinta, ynzun yancan da wata tasan yanda yake
wannan rawar jikin ynzun ya manta da batunta.
Tarasa me yake mata dadi, littafin datake
karantawa kuwa sam bata fahimtar abinda ke
ciki. Hka ta dinga zubda hawaye har nisan dare,
ganin bata da wata mafita, tashi tayi ta bude kofa
lokacin 2 saura taje tayo alwala tazo ta kama
nafila. Abba jin bude kofarta ne yasa shi leqowa
ta window aranshi yaji tausayinta don yasan bata
iya bacci sai ajikinshi, ita bata san ya leqo ba
don ko hanyar dakin bata ishe ta kallo ba. Yakalli
bishira wadda bacci yayi gaba da ita ya tausaya
mata sosai yanda tayi tarawar jiki alokacin
auratayyarsu dazun. Yadauko wayarshi yarubuta
ma ummi sako. KI KWANTA KIYI BACCI BABY,
TARE DA QISIMA CEWA KINA LAFE
AMAKWANCINKI (WATO JIKINA) INA CIKE DA
KEWAR LEBUNANKI. Tana sallah taji shigowar
saqo amma bata yi ko marmarin dubawa ba, haka
tai sallah har zuwa lokacin da bacci yasoma
fizgarta. Tayi adduo'o'i sannan ta kwanta, saida
asubahi ne datayi sallah sannan ta karanta, dan
tsaki taja tare da cewa, Karya kawai, kishi yasa
ta fadin haka don tasan Abba sosai baya boye
mata komai ynzun. Sai dai abinda yasake qular
da ita da asubahin nan yanda tana fita shi kuma
ya fito wanka, duk da tasan dole wani abu yafaru
tsakaninshi damatarsa, amma sai taga tamkar da
gayya ya tsaya don tafito taganshi. Tna idar da
sallah ta dora ruwa akicin dinta, tadafa ruwan tea
taje kicin din bishira tadauko flask tazo ta wanke
ta zuba musu ruwan zafi taje kofar bishira tayi
sallama bishiran ce ta bude ummi tamiqa mata
tare da cewa an tashi lpy? Cikin sakin fuska tace,
lpy lau, nagode. Ummi ta ce ba komai takoma
dakinta ta kulle kofarta don yau bata da darasin

safe. Abba ma yau bada wuri zai fita ba, don
haka yadan samu baccin safe sai 8 yayi wanka
ya karya, sannan yanufi dakin ummi. Kofarta tana
rufe, ya kwankwasa ta share sai can dai dataji
yaqi tafiya sannan tazo tabude. Takalle shiya yi
kyau cikin kananan kaya, ta kauda kai tare da
cewa, an tashi lpy? Yace lpy lau, kin karya? Tace,
um'um sai anjima, zata rufe kofar yace,
makaranta fa? Tace sai karfe 2 nake da darasi.
Ta maida kofar ta rufe, yayi dan murmushin
takaici sannan yafita. Kwananshi 2 dakin bishira
yayi niyyar dawowa dakin ummi, don ya kosa
yadawo ya lallasheta bazai iya daukar wannan
shariyar da take mishiba. Tsakaninta da bishira
lpy lau amma shi sai tana wani share shi. part 33 the end
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:45
Ya shigo da zumudi zai nufi dakinta, tamiqe cikin
fara'a daga wanke-wanken da take yi ta amshi
ledar hannunsa da jakar laptop ta nufi dakin
bishira. Shida bishira suka bita da kallo, ganin
zata shiga bishira tace ummi yau ai dakinki yake.
Ummi tace injiwa? Anty bishara ai kullum ke ce
dashi har sai kin rama duk kwanakin da kika
dauka agida. Kinga kenan kusan wata goma sha
daya kenan. Abba cikin sauri yace ke
mahaukaciya ce? Ina ki kasamo wannan fatawar?
Ta kalle shi, sannan tashiga dakin ta ajiye ta fito
taqara kallonshi gurin malamai, yace to ban
yarda ba, don haka zanci gaba dayi muku kwana
bibbiyunku, ummi tace to ni na yafe mata nawa
kwanakin bishira tace nagode ummi. Haushi ya
cika Abba, amma shi bazai dauki wannan horon
da ummi take shirin yi masa ba. Yadawo dakin
bishira a fili yafurta kema saina baki haushi zakiyi
dakin sanin wannan furucin. Sharewa yayi yaci
gaba da kwana dakin bishira tare da nuna kulawa
ga bishiran. Ummi ta jure duk da duk daren Allah
sai taci kuka ta gode Allah, sannan tashiga zargin
cewa shi ma ya Abban dama can yana son
tarewa dakin bishira, inba haka bame zaisa yayi
saurin yarda kuma yayi ta nuna mata soyayya?
Ganin ummi tana yi tamkar bata damu ba yasa
shi qa rajin haushi, yadawo da yamma suna

zaune kowa A qofarshi. Ummi tayi kwalliya cikin
qananan kaya, bishira kuma tana sanye da leshi,
karatun littafi bishiran keyi ita kuma ummi tana
yin gyaran qumbunanta. Bawai suna wata hira
bane amma suna kula juna sosai musamman
bishira tana son su saba da ummi. Ummin ce
bata cika son fitowa ba, bishira ta tashi ta masa
sannu dazuwa tare da amsar kayan hannunsa
don yanzun tana koyi da ummi gurin kyautatawa,
ummi ta kalle shi sannu dazuwa, ya amsa da
yauwa baby. Yakalli bishira sweety zanyi wanka,
tace to, takai masa ruwa yashiga dakinta, sai
tazo tace masa takai nan kuma yajanyo bishira
jikinshi. Ba wai yana da bukata bane, amma don
ya shaqar da ummi sai ya banko kofar, qaran
kofar ne yasa ummi kallon gurin dakin. Ta duqar
dakai taci gaba da abinda take yi, kusan minti
arba'in suka fito, Abba ya matsawa bishira wai
suyi wanka tare, tace ni bazan iya ba akwai ummi
dama da dare ne inajin kunya. Kuma kada taga
kamar cin fuska ne, yace kenan don kada ki bata
mata rai ni mijinki bazaki faranta min ba ko? Dole
ta bishi suka shiga bayi. Baqin ciki yasa ummi
tashi tashige daki, kuka sosai tayi daga nan bata
fito ba sai magriba, tanayin alwala tarufo kofa,
washegari ma qin bude qofar tayi daga alwalar
asubahi. Abba yayi ta raba ido ya ganta amma
bata fito ba, yasan fushi take, ya kira wayarta
taqi dagowa yayi mata saqo cewa in zata
makaranta tafito inkuma sai darana ta bude ta
amshi kudin mota. Tana gama karantawa tayi
wuri da wayar ba tare data bashi amsa ba, haka
ya tafi. Bishira ta qwanqwasa ma ummi ta bude
suka gaisa, tace naga baki fito bane ina fata lpy?
Tace lpy lau bacci ne, tace yau baza kije
makaranta bane? Ummi tace, zanje sai sha biyu.
Bishira tace kinji dadinki ni gashi nan ina tayi
masa zancen karatun amma ya share ni, ummi
tace inkin matsa zai yarda, tace ko za ki dan sa
min baki? Ummi ta riqe baki, ni a wa? Ke da yake
hannunki ai ke ce zai saurara, ni kin zo ne ma ki
zage ni. Bishira tace wane irin zagi? Ni dama ki
amshi mijinki ummi don gangar jikinshi ce kawai

agurina, amma ruhinsa yana gurinki. Ummi ta ce,
ngd da zagi, bishira ta ce zancan gsky ne ba
wani zagi. Haka suka yi ta rayuwa cikin kwanakin
ummi kam har rama tayi shima Abba ya rage
walwala don wanda yasan kan kula da shi
kamarta. Yayi missing din abincinta. Amma ya
gaji bazai jure ba. Ya tuna bishira tace masa zata
ta yini gidan ummanshi. Don haka yana gama
muhimman abubuwan da zai yi agurin aikin
yanufi gida. Ummi tana shirin tafiya makaranta ta
dauko jakarta sai kurum taga mutum kamar an
jeho shi. Ta daure fuska tamkar bata taba dariya
ba, yace ummi nagaji kin ji ko, na gaji da wannan
horon naki. Laifin me nayi miki? In don na dawo
da bishira ne sai in saketa, duk ba kece kika
takura min sai na dawo da ita ba? Ummi tace, ni
karka doran jakar tsaba kasa kaji su bini, ka saki
matarka sbd ni? Ba ruwana. Yace, to ki dawo
yanda kike, kuma ki janye batunki na wai kin
haqura dani, niban haqura ba. Ke ma kuma nasan
dole ki kasa kanki, ummi ta ce ni ban damu ba,
ya ce qarya ne gashi nan duk kin rame? Ya
canza daga fada zuwa lallashi, ummi don Allah
na roqeki mu koma kamar da, haba bebyna. Ya
lalubo hannunta ta qwace, don Allah ka tafi kada
bishira ta dawo ta same ka anan ta zargi wani
abu. Haushi yakamashi sosai, ya daga murya da
qarfi, kin san Allah ummi zan hadaki da umma, ta
nufi hanya fita, nikaga kada kasa ni yi latti don
lokaci yayi nisa. Ya ficiko ta ta dawo ba zaki
makarantar ba, ke an ma daina karatun tunda yafi
ni. Ta zubar da jakar da hijabi ta nufi gado shi
kuma ya fita cikin zafin rai, gidan su umma yaje.
Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
Abba? Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
Tace, kyale ta muje dakin babanku. Abba ya fada
ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
Banda shashancin ta da ita kadai take son
azauna? Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane

kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina? Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita. Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan. Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada. Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya. Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina? Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita. Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya? To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita. Ta jima tana bata shawara kafin
Abba yadawo suka nufi gida. Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
aranar. ** ** ** ** Kwanci tashi asarar mai rai,
shekara ta zagayo lokacin bishira da tsohon ciki,
Abba nason yara don muhibba taqi dawowa tafi
son umma dole suka haqura suka bar mata. Ta
haifi 'yarta budurwa tubarkalla ranar suna ta ci
sunan sahura inda suka sa mata walida. Ummi
nason yara, don haka in tana gida to tana manne
da walida, Abba yana damuwa da rashin samun
cikin ummi, wanda ita ummin ta barma Allah
komai. Shekaru uku sun sake biyo baya, lokacin
Bishira ta sake haihuwar habiba takwara Abba
yayi wa ummi. Tsohuwa an qara tsufa, 'yan
rigingimu sun qaru tace ita Abba yama takwara
amma bata son ya duke ta irin yanda yayi wa
ummi. Abba kullum qara son ummi yake, umma
ta matsa masa sai da yayi qoqari ya sai fili rabin
filoti tace kuma a rage ciye ciyen dadin nan agina

shì. Haka kuwa ya gina flat mai daki hudu, daya
ummi daya bishira, sai nashi sannan na yara.
Yayi qoqari gurin gyaran falon ita kuma ummi ya
canza mata kayan daki don bishira an canza
mata daza su tashi agidan su. Yace tabishi bashi
in ya samu zai bata kudi amadadin kayan daya
saima ummi, tace ta yafe. Ummi dake karantar
(BUSSINESS) har ta hada (H.N.D) dinta kuma
tayi bautar qasa. Abba dai yace baza'ayi aiki ba
amma ya yarda tayi kasuwanci, Alhaji babba ne
ya bata jari inda take saro kaya zannuwa, lesuna,
takalma zuwa jakunkuna. Abin ya amsheta don
har kayan aure tana hadawa, tana yin saqo irin
su kwatano da chaina, india, pakistan ko dubai,
ta hanyar wani wan kawarta. Haka kawai ummi
ta samu kanta da zaban abinci, yawan bacci
kasala da dai sauransu, sam bata san
takamaiman lokacin al'adarta ba. Don bata wani
lissafi in yazo shi kenan in bai zo ba bata damu
ba tama cire ranta daga batun ciki. Abba ya kalli
nonuwanta, baby kwanan nan kirjinki ya cika
sosai, gashi kinyi haske ko kin canza mai ne?
Tace yaya yaushe kazama likita? Yace, ummi kin
fa canza shirya muje asibiti, ta ce ya Abba don
Allah ka bar ni nagaji dazuwa asibiti. Yace, to ni
zan je inya tambaya game da yanda ki ka canza.
Cikin jin haushi tace sai ka dawo. Ga yara
atsakar gida sun ishe mu, yace ni naki nake
qawar in gani nasan addu'ar da nike yi bazata
fadi kara banza ba, sannan ga qoqarin danake yi,
shiru ta masa. Dagaske yake yi yaje yayi wa likita
bayani, yace yadai kawo fitsarinta. Sai da suka yi
tsiya da qyar bishira ta lallasheta ta yarda ta
bada fitsarin. Rungume likitan yaya lokacin da
yake fada masa ciki ne in dai har fitsarinta ne.
Afalo gaban bishira da yara abba ya rungume
ummi yana murna, ji tayi tamkar tsokana amma
ganin ya zauna yana ta buga waya yanata
yadawa ta amince cewa gske ne. Don haka ta
tashi ta shiga dakinta tayi alwala tazo tayi nafila
raka'a 2 cikin kuku take godewa Allah tare da
addu'ar ya raba lpy. Ya bata mai albarka.
Tsohuwa ma kuka ta saka lokacin da labarin ya

riske su. Ummi taga gata musamman daya
kasance cikin yazo da kumburi tayi sumtum. Duk
kowa ya tsorata sbd tunanin ko hawan jininta ne
ya tashi. ALLAH cikin Ikonshi data tashi haihuwa
saita santalo danta cikin gajeriyar nakuda, sak da
abba kwabo da kwabo. Rungume ummi abba yayi
don murna, sunan alhaji babba ya sake maida wa
kuma walid din dai suke kiranshi. Watan yaron
bakwai ummi ta sake rasa kanta, kuka wiwi ta
dinga yi shiko abba murna kamar yayi rawa.
Tasake samun da namiji inda yaci sunan alhaji
karami suka sa masa hibban. Haka suka ci gaba
da rayuwa cikin haquri da juna, tsakanin bishira
da ummi, bama irin bishira saboda abba baya iya
boye son ummi. Kan 'ya'yansu ahade ba kya
gane bambanci, bishira ta gane umma uwa ce
guda har da rabi, don haka hatta shawara saitaje
gurin umma kuma ko sabani suka samu da abba
gurin umma take zuwa. Ita kuma umma ta dauke
ta babu bambanci da ummi, don bata taba fada
ma ummi sirrin bishira ba. Sahura yanzun ta
yarda umma da alhaji sune rufin asirinsu, kuma
gatan Abba, bashi ma da yayi aure gidan dasu
ummi suka tashi nan ya zauna. Dangin bishira
yanzun sunga bishira ta samu natsuwa sun
sulhunta. Abba agurin aikinshi yana ta samun ci
gaba, lamuran sai godiya. Ummi tashafa addu'ar
da takeyi sannan tamiqe tana linke dardumar tace
kallon me ka ishe ni dashi ne ya Abba, yace ina
kallo ne na kusan samun da na uku

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login