Showing 3001 words to 6000 words out of 21888 words
Chapter 2 - MUGUN MIJI BOOK COMPLETE by Hamida Sunusi Ahmad.docx
dinga amfani da gas ɗinta,cikin sauri ta zuba waken a tukunya ta zuba ruwa ta saka gishiri kaɗan ta jefa kanwa ta rufe. Waje ta koma ta shiga kitchen ɗinta ta ɗakko wani ragowar barkonon da take da shi da maggi biyu da ya rage sai uban gishiri da ya siyo leda baƙa guda dan ganin arharsa. Ɗiba ta yi ta hau dakawa,sai da ya daku ya yi luƙui sannan ta kwashe. Ci gaba da aikace-aikace ta yi har waken ya dahu ya yi laushi tuɓus ya farfashe. Manja ta soya da albasar Barirah sannan ta samu mazubi mai kyau da take zuba masa abinci a ciki ta kai kitchen ɗinta ta rufe. Godiya ta leƙa ta yi wa Barirah wadda idan da sabo ta saba,shi yasa kawai bata amsa ta ba sai ta tambaye ta ko akwai wani abu da take so? Girgiza kai Fauziyyah ta yi tare da cewa.
"Bana buƙatar komai Aunty na gode Allah Ya jiƙan magabata."
"Amin Fauziyyah."
Cikin gaggawa Fauziyya ta shiga ɗakinta ta cire kayanta ta fito da wanda Abbas ya cire kafin ya fita,wanki ta tsugunna ta yi ta ɗauraye su ta shanya,ta na gamawa ta ɗebi ruwa ba tare da ta koma ta sanya hijabin da zai rufe mata jiki ba ta faɗa wanka. Ta jima tana dirzar fatarta kafin ta fito. Ruwan dake jikinta ne ya bawa zanin jikinta damar mannewa a manyan mazaunanta da ke ɗauke da cinyoyi manya,gashin kanta mai yalwar tsawo da cika ta ɗaure shi a bayanta har ruwa ya taɓa shi yana ɗiga,wasu daga cikin gashin nata ne suka manne a dokin wuyanta da gefen fuskarta,farar fatarta mai ɗaukan hankali sai sheƙi take yi,gashin fuskarta duk ya kwanta gwanin burge mai kallo. A haka ta duƙa ta yi alwala sannan ta miƙe dan komawa ɗaki. Kamar daga sama aka wurgo su babu sallama sai hayaniya da darerekunsu. Wata iriyar faɗuwa gaban Fauziyyah ya yi,nan take ta gane wautar da ta tafka na rashin sanya hijabi dan suturce jikinta. Nasihar da Barirah ke yawan yi mata ce ta faɗo mata a rai.
'Fauziyyah ina mamakin yanda kike zama ki saki jikin ki a waje,bayan kin san kina da sura mai ɗaukan hankalin mace ƴar'uwa ki ma ballantana namiji wanda dama mace ce abokiyar jin daɗin rayuwarsa. Ko baki san cewa duk shaƙuwa da zaman da mukai dake ba be kamata ace Shehu na ganin jikin ki ba? Kar ki ɗauka wai kishi nake yi da ke,ah ah gaskiya nake faɗa miki. Matsalar mu hausawa muna ɗaukan zama babu hijabi har wani wanda ba muharramin mu ba ya ga surar jikin mu ba a bakin komai ba,musamman yaran maƙota da mijin maƙota,sai mu dinga ganin ai an saba,ko kuma haya muke yi to ya zamu yi ai dole a gauraye.'
A nutse Fauziyyah ta ce.
'Aunty shi ne ke hana ni saka hijabi ko mayafi,wai a cewarsa yana alfahari da kyauna,yana so duniya ta san wace iriyar mace ya aura.'
'Lallai kuwa zai kai ki wuta idan baki gyara ba,domin za a wayi gari tin kina son suturce jikin ki da kan ki,kema zaki saba da zama babu suturar arziƙi.'
Lallai wannan lokacin Barirah ke jiyewa Fauziyyah zuwansa,gashi har ta saba da rashin rufe jikinta. Sauri ta sanya za ta gudu ɗaki don ta rufe jikinta. Abbas ya dubi abokansa ya ga yanda suke bin mazaunan Fauziyyah da kallo cike da kwaɗayi da burgewa. Murmushin jin daɗi ya yi sannan ya haɗe fuska ya kalle ta,cike da isa da taƙama ya ce.
"Ki na saka ɗaya ƙafar a ɗaki zaki gamu da ni. Oya maza wuce ki ɗakko waccan tabarmar ki shimfiɗa mana sannan ki kawo wa mutane abinci."
Babu yanda ta iya haka ta juya kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki gudun kar ta yi dogon motsi jikinta ya juya. Sai dai duk da yanda take taka tsantsan hakan bai hana jikin nata juyawa ba,ganin yanda take tafiya bata kaɗa jikinta yanda ta saba ne ya sanya Abbas sake daka mata tsawa ya na faɗin.
"Dalla Malama ki kama jiki ki ɗakkowa mutane wajen zama,shashasha kawai wadda bata san yanda za ta tarbi miji ba idan ya dawo daga wahalar nema mata abinda za ta ci."
Cikin hanzari ta wuce ta ɗakko tabarmar da ta ji jiki,sai dai a wanke take tsaf babu datti,ta shimfiɗa musu. Juyawar nan da za ta yi ta shiga ɗaki zaninta ya kusan kuncewa,da sauri ta kama zanin ta faɗa ɗaki,ta na jin Abbas na masifa ya na faɗin.
"To yanzu Fauziyyah abincin ma sai na roƙa ki kawo mana? Kin san Allah ki dena saka ni yawan magana bana so,idan kuma kika bari na sake yi miki magana na lahira sai ya fiki jin daɗi."
Wani irin dogon tsaki Barirah ta ja a daidai lokacin da take fitowa daga ɗakinta za ta yi alwala,ido suka haɗa da Abbas da abokansa ta kuwa daka musu harara tare da faɗin.
"Me na ci ban bawa mutum ba ake ƙure ni da mugun kallo? Allah dai ya kai mutum lahirar nan ya banbance mana jin daɗin duniyar da na ƙiyama,aikin banza kawai,namiji har namiji amma basirarsa ta kare wajen musgunawa mace mai rauni."
Kallon Abbas abokansa suka yi,wani da ake kira da Salman ne ya ce.
"Tab ! Lallai matar nan ta ci ta ƙoshi,haya fa take a gidanka amma take iya faɗa maka maganganu yanda ranta ke so baka yanka musu tikitin barin gidanka ba."
Abbas bai ce komai ba har sai da Barirah ta shige banɗaki sannan ya yi ƙasa da murya ya ce.
"Idan na kore su ai kaina na cuta,ni kaɗai na san irin amfanin da zaman su yake yi min a cikin gidan nan. Sannan kuma wannan matar da kake gani ta riga ta shanye mijin,kana taɓa ta ko ka faɗa mata baƙar magana ubanka zai ci,ka dai ganta daf da ƙasa ba ta da wani kyan arziƙi,to a wajensa Fauziyyahta mummuna ce."
Nan da nan suka hau musanta kalamansa akan Fauziyyah suka ɗora da yabon shape ɗinta da surar ta tare da muryarta,Fauziyya na ɗaki ta na saka wata jemammiyar doguwar rigarta da ta ji jiki tin ta lefen ta,gashi yanzu auren su ya doshi shekara uku da rabi, ɗankwalin rigar ta ɗaura tare da rufe gashin kanta ta can ƙarshe,hakan sai ya bawa gaban kan nata bayyana kamar tana sane ta yi hakan. Takaicin hirar ta da Abbas yake yi wa abokansa ce ta sanya ta zama a bakin gado ta zabga tagumi,me yasa Abbas yake yi mata haka? Me yasa ba ya iya riƙe sirrin auratayyar su har sai ya sanar da abokansa hankalinsa ke kwanciya? Me yasa kuma baya tashi yabon ta sai abokan sun zo gidan? Meye amfanin yabon da yake yi mata a wajen mutane amma ita ko sau ɗaya bai taɓa yaba ƙoƙarinta ko bajintar da ta yi masa ba? Kiran sunanta da ta jiyo Abbas ya yi a ƙufule ne ya dawo da ita hayyacinta ta miƙe da sauri ta nufi kitchen. A jikinta take jin yanda idanuwansu ke kallon saƙo da lungu na jikinta. Ƙwalla ce ta taru a idanunta,a haka ta duƙa ta ɗakko abincin ta ɗora a babban faranti ta zuba ruwan randa a jug dan tini ya siyar mata da fridge da deep freezer ɗinta manya,wai babu wajen ajiye su,duk lokacin da suka yi gidan da ya fi wannan girma zai siya mata.
Cikin takunta mai cike da natsuwa ta ƙarasa gaban su ta durƙusa ta ajiye abincin,gaishe su ta yi kanta a ƙasa suka amsa sannan ta dafa gini ta miƙe ta koma ɗaki. Ta na shiga Rabi'u ya ce.
"A gaskiya Abbas duk cikin mu kai kaɗai ne ka yi dacen macen nuna wa duniya ba ma sa'a ba kaɗai,ka ga mace kamar ka sace ta ka gudu?."
Dariya suka saka Abbas kuwa ya na jin kansa kamar ya fashe dan girma,Salman ne ya ce.
"Allah sarki Babangida,yanzu da yana nan fa da ya ce,wannan abun da kuke yi haramun ne,Allah ya haramta,kai kuma ka zauna kamar mara kishin iyalinsa wasu na yabon matarka,ni duk wanda ya yaba surar mata ta ba sai na zare takobi na fille wa jahili kai ba."
Dariya suka bushe da ita suka tafa,cikin shaƙiyanci Abbas ya ce.
"Ahhh shikenan Babangida ya tafi,ta wanke ta bashi ya kurɓe."
Salman yana dariya ya hau daidaita fuskarsa ya na kwaikwayar Babangida da baya wajen ya ce.
"Ah ka manta ni na sha abuna a haka? Ai bata wanke ba ta sirka da wani abu, concentrate na sha. Ku fa gani kuke yi yiwa matayen ku mugun hali da musgunawa shi ne yake riƙe muku su ko? Ku sani soyayya ce ke riƙe da su kawai da biyayyar aure,ina jiye muku lokacin da zaku kai su bango su juyo kan ku da tasu kalar azabar ba za ku ji daɗi ba."
Dariya suka sake bushewa da ita,cikin isa da izza Abbas ya ce.
"Ni mace ta isa ta juya ni? Kuna gani fa ana zaune wannan ƙwailar tasa za ta kira shi a waya,jiki na rawa yake tafiya,ni yanzu da nake da mace kamar Fauziyya ta isa ma ta min haka? Kun dai ganta kun shaida yanda take da kyau da duk wani abu da namiji zai nema a wajen mace,amma bata isa ina faɗa tana faɗa ba,ballantana mu yi sa'insa ko ta saɓa umarnina."
Dariya suka kece da ita Rabi'u ya daki kafaɗarsa ya ce.
"Shegen sama,ai nake faɗa maka abokina kai kam ka gama dacewa a duniya,saura ƙiyamar ka kawai. Ka samu mai siffofin hurul'ini tin a duniya."
Buɗe kwanon abincin Abbas ya yi da niyyar su ci idanuwansa suka sauka akan dafaffen waken da ya ji manja da yaji,nan take yawun bakin su ya tsinke,kasancewar abincin manja ya gaji haka. Sai dai girman kai da mugunta irin ta Abbas ta sanya shi rufe kwanon ya na muzurai,sai da ya haɗiye yawun da ya cika masa baki ya daidaita natsuwarsa sannan ya ce........
[9/12, 6:22 PM] HAERMEEEBRAERH ✍️✨: MUGUN MIJI.
RUBUTAWA HAMIDAH SANUSI AHMAD HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 3.
"Ke zo nan!"
Jiki na rawa Fauziyyah ta miƙe za ta fita,ta na ayyanawa a ranta.
'Na shiga uku ni Fauziyyah me kuma na yi?'
Mamakin yanda har ta ji kiransa ta amsa ne ya kama Salman,cikin yin ƙasa da murya ya ce.
"Wai kana nufin wannan kiran da ka yi mata har ta ji ta amsa kuma ta na nan tafe? Gaskiya abokina kai bala'i ne."
Murmushin mugunta Abbas ya saki sannan ya ce.
"Kar ma ta amsa mana. Ai matsawar ina cikin gidan nan to fa kunnuwanta da zuciyarta a buɗe suke,ta yanda ko da motsi na yi ta san me nake buƙata kafin na furta,kuskure ɗaya za ta yi wajen ƙin fahimtar magana ko motsina jikin jakar ya faɗa mata."
Kalmar jaka da ya kira ta da shi a gaban abokansa ce ta daki zuciyarta,cikin ƙunar rai ta durƙusa a gabansa cike da ladabi ta ce.
"My king gani. Ku na buƙatar wani abun ne?"
Haɗe rai Abbas ya yi ya nuna Fauziyyah da yatsansa manuni, cike da wulaƙanci da izza da isa ya ce mata.
"Ke dan Uban ki wace iriyar shashasha ce? Yanzu ace na fita rana da zafi inuwa da damina na nemo abinda za a ci a gidan nan,amma na kawo baƙina ki haɗa mu da zallan dafaffen wake har da wani manja da yaji a ciki? To ina laifin ma ki dafa wake da shinkafa?"
Zuciyarta na tuƙuƙin baƙin cikin zagar mata mahaifi da ya yi a gaban abokansa,ta daure tare da jurewa kar ya gano halin da take ciki ta ja wa kanta mari ko jibgar wulaƙanci ta ce.
"My king ka yi haƙuri don Allah, nima shinkafa da waken na yi niyyar dafawa sai kuma na tarar da shinkafar ta ƙare shi yasa na yi amfani da iya abinda muke da shi kawai na dafa dan kar ka dawo babu abinci."
Cike da ɓacin ran tona masa asirin bashi da ƙwayar shinkafa a gidansa da ta yi gaban mutanen da yake nuna wa shi wani ne, ya daka mata tsawa tare da faɗin.
"Dalla malama tashi ki bani waje! Daƙiƙiya kawai. Kin duba buhun da na kawo ne jiya? Ki na nan kina jan jiki kamar akan ki aka fara ɗaukan ciki baki san ma akwai abinci a gidan ba. Bari mu gama zan shigo ne mu gauraya da ke. Ware ki bawa mutane waje."
Duk rugugin faɗan da yake yi bai dame ta ba da fari,saboda hankalinta ya yi nisa wajen tunanin yaushe ya shiga da buhu gidan? A ina kuma ya ajiye buhun? To ko dai a store ya ajiye bai sanar da ita ba? Ta na tafe tana tunani ta furta.
"Kai gaskiya ban ga wani buhu ba,saboda yana shigowa gidan na je na tarbe shi kamar yanda na saba yi kullum,da hannuna na karɓi jakarsa na ajiye a inda na saba rataye masa,to wanne buhu yake nufi?"
A bakin gado ta zauna tare da zabga tagumi. Ƙwaƙwalwarta ce ta tina mata kalamansa da ya ce.
'Bari mu gama zan shigo ne mu gauraya.'
Hankalinta ne ya yi mummunan tashi,dan kuwa ta san yau ɗin Allah ne kawai zai ƙwace ta a hannun Abbas. Wasu jijiyoyi ne raɗa-raɗa suka firfito a gaban goshinta,hancinta kuwa har wata zufa yake tsattsafarwa,idanuwanta sun kaɗa sun yi jawur saboda tashin hankali. Ta na nan zaune ta ji fitar su suna sake zuga shi akan ya ci gaba da riƙe wuta,domin kuwa kyawawan mata irin Fauziyyah idan suka samu waje juya miji suke yi,wataƙila ma albashinsa ita ce za ta dinga amshewa sai abinda ta bashi na kashewa a ciki. Idan kuwa ya kuskura ya bari hakan ta kasance,to fa babu shi babu ci gaba da more ƙuruciyarsa da ƴan shila,guzumayen ma ba kula shi za su yi ba. Wata iriyar dariya suka sanya suka tafa,shi kuwa gogan cikin haɗe girar sama da ta ƙasa ya ce.
"A da ne kafin mu yi aure take da wannan farin jinin. A yanzu kuwa ko me sharar kasuwa sai dai ya yi manage da ita,saboda ta zamo marar amfani."
Wasu irin zafafan hawaye ne suka fara gudun tsere a kuncin Fauziyyah da ke sauraron duk wata kalma dake fitowa daga bakin masoyinta,wanda ya kusa rasa ransa saboda tsoro da fargabar rasa ta da ya kusan yi a baya,namijin da ya sadaukar da jin daɗin sa saboda ya mallake ta,shin da gaske ne bata da wani amfani ko a wajen mai sharar kasuwa? Shin da gaske ne babu namijin da za ta burge ballantana har a so ta? Ashe shi yasa Abbas ɗinta abun ƙaunarta ya sauya daga masoyinta ya koma maƙiyinta? Lallai rashin gyara masifa ne,to amma ai laifinsa ne ta lalace har ta zamo marar amfanin da yake yawan kiranta. Tini ya dena sauke duk wani haƙƙinta da ya rataya a wuyansa. Turare wannan shi kaɗai yake siyawa kansa ya ɓoye,ko za ta yi warin bunsuru ne sai dai ta yi,amma bata isa taɓawa ba.Sutura kuwa kamar zata kashe Abbas masu kyau da tsada yake siya,takalman sa kaf babu ƙasa da na dubu goma,amma ita tin na lefe take ta murza ko na sallah baya yi mata ballantana idan ya ɗinka nasa ya tuna da ita. Sabulun wanka yake siyawa kansa mai kyau da tsada,ita kuma sai dai ta yi da na wanki,idan ya ƙare ta yi da omo,idan babu omo ta yi da zallan ruwa,shi yasa lokuta da dama ko ta yi wanka da ta yi aiki kaɗan sai ta fara warin hammata. Man shafawarsa na musamman ne,amma ita ko basilin be siya mata ba,tin mayukan lefenta da suka ƙare be sake sai mata mai ba balle hoda,shi yasa ko tsinke babu a saman mirror ɗinta da ya wuce kwalli da brush ɗin da take taje girar ta da shi. Idan tana son shafa mai sai dai idan ta faki ido ta tatse na leda da ta kan adana idan ta juye man. Lokuta ƙalilan ne take samu Barirah ta sammata mai a duk lokacin da ta sai me kyau na gyaran fata. Ranar da Mahaifiyar Abbas ta kawo mata basilin kuwa ririta shi ta dinga yi ta na adanawa,har sai da ya shekara be ƙare ba. Murmushi ta yi a lokacin da ta tina da mahaifiyarsa,mace ce itanmai mutunci da karamci,takaicin Abbas shi ne ya yi sanadiyyar da ta kamu da mummunan hawan jini. Yawan zuwa gidan ta tarar da Fauziyyah a cikin mawuyacin hali har itama nata ciwon ya tashi ne,ya sanya danginta suka bata shawarar ta rage zuwa gidan nasa,idan yaso duk sanda ta so ganin Fauziyyar ta dinga saka shi yana kai mata ita su gaisa,shi kuma ta dage da yi masa addu'a da fatan shiriya,watarana komai zai zamo labari. Wannan shawarar ce ta sa sai su shafe wata ɗaya zuwa biyu basu haɗu ba,wani sa'in ma har sukan kai wata uku Fauziyyah bata ga surukar tata ba. Sai dai shi yana zuwa kullum yana gaida ita,kasancewar wajen da yake koyarwa babu nisa sosai da gidan nasu.
Zumbur ta miƙe tsaye tare da binsa cikin ɗaki,saboda yanda ya fizgi hannunta na hagu ko tausayin tulelen cikin dake jikinta bai yi ba. Jikinta ne ya ɗauki rawa suna zuwa ƙofar bedroom ɗin su ta riƙe gini ta na yarfe hannunta na dama ta ce.
"My king don Allah ka tausaya min,ka ga halin da nake ciki. Ka yi haƙuri ka yafe min duk wani laifi da na yi maka,na yi alƙawari ba zan sake ba."
Mugun kallon da ya zuba mata da shanyayyun idanuwansa ne suka sanya ta haɗiye wani mugun yawu mai bala'in kauri,busassun laɓɓanta ta lashe ta ɗaga ƙafa da ƙyar ta bi bayansa zuciyarta na lugude kamar ana dakan sakwara.
A zafafe ya yarfe hannunta ya koma saman makeken gadon su mai tsananin kyau da tsada ya zauna. Huci yake yi kamar wani kumurcin maciji. Murya a shaƙe kamar ta ragon layyan da ya ci kuka ya gaji ya ce mata.
"Tuɓe."
Hawayen da suka maƙale suka ƙi fita ne saboda tashin hankali,suka samu damar