Showing 3001 words to 6000 words out of 29277 words

Chapter 2 - Mugunta 1 Complete Hausa Novels By Khairat.txt

KHAIRAT   

13 Mar 2026

11

dabbobin inna ladiyo ta kalle ta sama da kasa sannan tace "ga surfe nan kwano 3 kiyi sauri kiyi musu zasu dawo yau su amsa". Da "toh" AYAMAN ta amsa mata kafin ta kalli gefen kwanon kosan dake ajiye har ya fara bushewa,inna ladiyo tace "wannan kosan sai kin gama surfen dawar nan sannan Zaki ci" kin jima na gaya miki.

Daukar surfen tayi zata fara har ta fara debo ruwa daga cikin randar su taji inna ladiyo na cewa"wannan ruwan bana surfe bane na amfanin gida ne Dan haka kije ki debo Wani"
"Toh" AYAMAN ta fada tana daukar bokitin ta fita daga gidan,"saura ki tsaya yawon iskancin ki kar kiyi sauri ki debo ruwan".
AYAMAN dai fita tayi ta kama hanyar da zata sada ta da borehole din garin,ta tarar da borehole din ba mutane Dan haka tayi sauri ta dibi ruwan ta kama hanyar gidan,tana cikin tafiya taji muryar Anas,
Anas wani saurayi ne da yake tausayin AYAMAN matuka,saboda irin halin da take ciki, "ahh yau ko nema na ba kiyi ba AYAMAN? Idrees ya fada yana murmushi.
Murmushi AYAMAN tayi Mai kafin tace "Ina wuni". "lapiya kalau AYAMAN" ya gida? Idrees ya amsa mata gaisuwar tata, "lapiya kalau alhamdlh" AYAMAN ta fada tana kokarin wucewa kar inna ladiyo ta ga ta Dade, Anas ne yace "AYAMAN ya maganar mu ta ranar nan? Kina so na?
Rasa me AYAMAN zata fada tayi kawai tayi sauri ta wuce tana murmushi,shima murmushin yayi kafin ya wuce.
Inta ce Bata son idrees toh wallahi tayi Karya,Dan Anas ya cika namiji,ka hankali da nutsuwa ga Kuma neman na kanshi,a haka tayi ta tunanin Anas har ta qarasa gida.

"Assalamualaikum "AYAMAN tayi sallama,shiga cikin gidan tayi Amma Bata tarar da kowa ba a tsakar gidan ajiye ruwan tayi sannan ta leka dakin inna ladiyo ta tarar ba kowa Dan haka tayi sauri ta debi ruwa tayi wanka da tokar da ta Tara ta shiga dakin ta shirya sannan ta fara surfen Wanda sai da ya dauke ta awa 4 ba tsayawa sannan ta kammala.

Ruwa ta Sha, sannan tayi alwala tayi sallah, karar da cikin ta yake mata ne yasa tai saurin fita zuwa tsakar gidan ta dauko busheshen kosan ta zauna ta fara ci, ta cinye Ta sha ruwa ta gode wa Allah,ta zauna tana tunanin rayuwar ta....




Love you all 😘 ❤️


Khairat 🖤 🖤 🖊️ 🖊️ 🖊️https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*



*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*

https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8






*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️







😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈




Written

By

Khairat 🖤🖤🖤




Na sadaukar da wannan shafin zuwa ga babbar yayata, happy birthday my dearest sister ❤️ ❤️ 😘




BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM



Page 9-10


Ruwa ta Sha sannan ta yi alwala ta yi sallah, ƙarar da cikinta yake ma ta ne ya sa tai saurin fita zuwa tsakar gidan ta dauko busheshen kosan ta zauna ta fara ci har ta cinye.

Ta sha ruwa ta gode wa Allah ta zauna ta fara tunanin rayuwar ta..


Anan muka tsaya yanzu zamu cigaba....



Tuna wa ta yi da rayuwar da sukai ita da innarta da babanta. Sannan kuma tana mamakin halayya irin ta inna ladiyo.

Tana mamakin wai aminiyar innar ta ce ta ke Bata irin wannan azabar,kuma mahaifinta yana kallo ba tare da yace komai ba.

Tana nan zaune ta ji kiran sallar laasar, tashi ta yi ta gabatar da sallar ta tunda tana da alwala,sannan ta Kai kukan ta ga Allah mabuwayi.


Karar bige kwanuka da ake yi a tsakar gidan ne yasa ta tashi daga lazumin da ta ke yi ta leqa ta yagallallan labilan dake jikin kofar dakin.
Yunusa ta hango a tsakar gidan a halin maye yana ta tambele, yana magagi irin na yan giya.
Tuno abinda ya faru ranar nan ta fara yi, "dimm" taji zuciyar ta ta buga,fara faɗan sunan Allah ta yi a cikin zuciyarta cike da firgici.
" Kehh! Shegggiiiyyar yarrriiinnnnyaa." Yunusa ya faɗa cikin muryar maye, "Kin zata bannn gannkii baaannneee! Hhhhh. " ya sheqe da wata irin dariyar ƴan duniya.
Ayaman tana daki ta yi tsuru-tsuru,ta ji shigowar mutum dakin, kukan da take riqewa ne ya kufce mata, "Wayyyyooo, dan girman Allah kayi hakuri, ka sani fah idan babu wanda yake kallon ka ka sani Allah yana kallon ka kuma akwai ranar hisabi ." Ayaman ta fada cikin muryar kuka.
Sannan ta cigaba da fadin" kada kayi sanadiyyar lalata rayuwar marainiyar Allah, wacce Bata da kowa sai Allah."
Ganin duk wannan jawabin ba jinta yake ba, sai dai ma kuma matsowa da yake, damkar kasar dakin ta yi ta watsa mai a Ido sannan ta hankaɗe shi ta fice daga ɗakin.
Tsakar gidan ta fita tana Neman abin da zata kare kanta, murhun da suke girki da shi ta dauko, yana fitowa ta daidaici wurin goshinsa sannan ta maka mai wannan murhun.
Da gudu ta zura ta fice daga gidan, bata tsaya ko ina ba sai gidansu tsahare.
Tana shiga ta tarar da tsahare tana tankade garin tuwo, ganin a yanayin da Ayaman ta shigo ko ɗan kwali Babu a kanta yasa ta kama Ayaman suka zura zuwa cikin ɗakin tsahare suka rufo kofar.






********************************





*LADIYO da DELU*


Zaune suke gaban bokan kan tsauni sun rusuna kamar masu neman yafiya, " Na gaya miki ba abunda zamu iya yiwa yarinyar nan,saboda akwai wani babban kariya a tattare da ita." bokan kan tsauni ya fada yana kallon inna ladiyo.
Sannan ya cigaba da fadin,sai dai akwai hanya daya,matso kiji, inna ladiyo ta matsa kusa da shi tana kara kunnanta kusa da bakinshi.
"Toh shikenan fatan dai ba matsala." , Ladiyo ta fada.

"Idan kinga baza ki iya ba ki barshi." boka ya fada yana zazzare idanu.
" A'a zanyi boka ." inna Ladiyo ta fada tana mai ƙara russunar da kai kasa.
" Ke kuma." boka ya juya yana kallon Delu, mece matsalar ki?"

"Na gaishe ka ɗan gidan uwar kowa,bokan da yake ɗaya tamkar dubu."inna delu ta cigaba da yi ma boka kirari har sai da ya dakatar da ita.
" Dama akan maganar mijina ne, Ina son a mallaka min shi ya zama babu me iko da shi sai ni."
Delu ta numfasa sannan ta cigaba da cewa, "Sai kuma maganar auren diyata , a taimaka boka." , inna delu ta gama fada tana ƙara russunar da kai.
" Akan mijin ki, yau da dare misalin karfe uku na dare kije maqabartar dan dolo, akwai sabon kabari da yau aka binne gawar, mutane ma zasu ke su ajiye Wani kullin magani a cikin kabarin, ki je ki dauko maganin daga cikin kabarin ki barbada shi a kan shimfidar ku ke da mijin ki yau da daddare kuma ki tabbatar Kun kwanta a Kai, sannan Kuma kiyi tsarki da shi , ba yannan ki sa a ruwan wankan mijin ki, sannan Kuma kiyi amafani da kwalli da Kuma turaren da na baki kwanaki, sannan Kuma ki tabbatar kin gama komai kafin giftawar alfijir" bokan kan tsauni ya gama fada yana kallon inna delu.
Ya numfasa ya cigaba da fadin, "batun diyar ki kuma akwai layar da zan baki ki Saka akan hanyar da mutane ke wucewa,daga nan samari zasu yi ta zuwa" boka ya fada yana kallon inna delu wacce tuni ta fara washe dashashun hakoran ta.
" Ku tashiiii ku bani guri la'anannun Allah,tsinannanu" boka ya fada yana kallon su, zumbur suka mike suka kama hanyar fita, kafin su gama fita ya ce " ku kawo min ladan aiki na ranar lahadi da misalin karfe Sha biyu na dare " , " toohh boka",mun gode a Mika mana sako gurin uwarkowa" inna delu da ladiyo suka hada bakin wurin fada sannan suka fice daga kogon" .

Suna fita daga cikin kogon suka dauki kayan su suka Saka, saboda dama dokar bokan kan tsauni ce cewar ba'a shigar Mai da kaya cikin kogon, suna saukowa daga kan tsaunin Dan kogon Yana Saman tsaunin.
Suna ta tafiya su biyu a cikin dajin ga dare Dan a lokacin kusan karfe Sha biyu na dare,ga Kuma sanyin da ake busawa a garin.
Har suka shigo cikin garin suna ta firar su, " delu tace ay ladiyo Muna gama aiwatar da aikin nan sai yadda nayi da malam" ta karasa fada tana washe baki , "toh kafinnan muje gidanki mu huta kafin lokacin yayi mu tafi maqabartar,ko ya kika gani"? Inna ladiyo ta fada tana kallon delu.
" Yayi Hakan ma da na gaji wlh" delu ta fada kafin suka cigaba da tafiyar su har gidan delu.



BAYAN AWA BIYU DA RABI

Delu da ladiyo.



Sun fito daga gidan delu sun fara tafiya, hanyar maqabarta suka nufa.
Isar su ke da wuya suka durfafa akan sabon kabarin dake farko farkon maqabartar, wuqa delu ta fito da daga jikin ta, ta fara haqa kasar kabarin, ladiyo na gefe tana haska mata hade da kallon delun.
Wani hayaki Mai ban tsoro da kauri ne ya fito daga kabarin Wanda yasa suka toshe hancin su.
Wani qullin magani ne ya fado daga cikin kabarin ya fada hannun delu, tashi su Kayi zasu tafi, yayin da kasar kabarin ta koma yadda take kamar ba'a taba bude wa ba.
Sauri suka yi suka fita daga maqabartar zuciyar delu fess, a hanya suka tsaya suka binne abin da boka ya basu, wacce hanyar zuwa kasuwar garin ce
A marrarrabar hanya suka rabu inda ladiyo ta kama hanyar gidan ta ita Kuma delu tayi ta ta hanyar.


LADIYO


Tana Isa gida ta tura kyauren kofar Wanda ba'a rufe ba saboda mutanen garin kowa yasan kowa ne ba Wanda zai shiga gidan Wani yayi sata.
A tsakar gidan tayi kichibis da yunusa kwance jikin jini, sakamakon wata yakai tsakiya shiyasa take iya ganin sa Dan gari yayi haske, razana tayi da ganin shi a Hakan, sai da ta debo ruwa ta watsa mai taga ya farka sannan hankalin ta ya kwanta.
Ruwa ta dafa Mai zafi ta taimaka mai yayi wanka ya gasa jikin shi Kuma ta wanke Mai ciwon sannan ta fito daga bandakin, dakinshi dake sauron gidan ta kaishi ta kwantar sannan ta koma tsakar gidan ta zauna.
Bata Ankara ba tana ta tunanin waye yayi ma yunusa wannan abin sai ji tayi an kira sallar asuba, tsaki taja kafin ta miqe ta nufi dakin AYAMAN domin tashin ta ta fara bauta.
Tana kutsa Kai cikin dakin da ruwa a hannun ta, ta ga ba kowa a cikin dakin, ta duba ko Ina Bata ga kowa ba sannan ta fito tsakar gidan tana mamakin Ina AYAMAN taje.....





DELU


Tun bayan rabuwar su da ladiyo a kan hanya ta nufi gidan ta, tana shiga ta dauki maganin tayi amfani da shi hade da turaren Dan kwallin sai da safe, ruwa ta tafasa ta barbada maganin a ciki ta Kai bayi.
Dakin mijin nata ta nufa,tashin shi ta fara yi har sai da ya Farka, " wai ke delu meye haka ne? Saboda rashin ...... Sai Kuma yayi shiru sakamakon Jin Wani luuuu a kansa da yayi , jansa tai zuwa dakin kafin ta rufo kofar tana tuna gargadin boka na kar ta sake asuba tayi Bata aiwatar da abinda ya sa suba....







Nima anan zan dakata sai mun hadu a shafi na gaba...... Nagode ❤️😘



https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB

*(Posting room)*






*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇*



https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8



*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️






😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈


Written



By



Khairat 🖤🖤🖤





Wannan page ɗin ma sadaukar da shi zuwa ma karanta littafin MUGUNTA da masu comment, ina godiya I love you lodi lodi🙈❤️‍🩹💋♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️.





BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM




Page 11-12





Bayan wayewar gari




* LADIYO *


Tun bayan fitowar ta daga ɗakin Ayaman ta shiga dakinta cike da mamakin inda Ayaman ta tafi, "Ko ba komai dole ta dawo gidan ay." inna Ladiyo ta faɗa tana tashin malam isyaku cike da masifa, " Toh asararrare sai ka tashi asuba ta yi, ko so kake a sake ma wani daren?,kai da ba aikin fari kake yi ba bare baki shine har ka samu damar shan bacci haka." ta karasa faɗa tana kallon malam isyaku.
Tashi malam isyaku ya yi saboda kansa da yaji ya fara Sara masa, salati ya yi sannan ya miqe ya fita daga dakin ya bar Ladiyo tana ta sababi.
Malam isyaku yana tafe yana tunanin yadda akai Ladiyo take fada masa magana baya daukan mataki a kan ta, sai dai koma meye ya barma Allah dan a gareshi yake kai kukansa.





* DELU *

"Delu! Delu! Delu! Ke ki tashi mana lokacin sallah ya yi,malam surajo mijin delu ya faɗa yana tashin ta daga bacci.
" Malam ga ruwa a bayi na aje ma fah, da shi kayi wanka dai koh?" Delu ta tambaye shi tana mitsika idanu irin na wanda ya tashi daga bacci.
"Ehh naga da dumi shiyasa nayi amfani dashi, ki tashi fah." ya gama faɗa yana fita daga dakin.
Delu kuwa wani farinciki ne ya cika ta saboda ganin aikin su ya fara aiki dan malam surajo ko da wasa baya shigowa dakinta, wai shi ne yau har da tashin ta daga bacci.

Fita tsakar gidan ta yi ta wanke fuskarta ta dau tsintsiya ta fara shara dan sallar asuba ba wani damun ta tayi ba.






*AYAMAN*

Tun bayan shigar su ɗakin tsahare, ta zauna ta fara maida numfashi sannan ta labarta ma tsahare abinda ya faru.
Tsahare sakin baki tayi tana kallon Ayaman"Toh yanzu yana gidan ne?"
"Eh Yana chan."

"Amma dai Ayaman kinyi min daidai, yanzu Ladiyo ta gane ba tsoro kike ji ba." Tsahare ta faɗa tana jan Ayaman zuwa tsakar gidan.

"Taho muje in karasa aikina, ba kowa a gidan." taja Ayaman suka fita, suka cigaba da girkin wanda tuwo ne na masara da miyar busheshen kuɓewa wanda ta ji daddawa da sauran kayan kanshi.

"Wai gidan ba kowa ne" Ayaman ta tambaya yayin da suke wanke kwanikan da suka yi amfani da shi.
"Ehh duk basa nan, sun tafi biki, ni ce kawai a gidan."

Haka suka cigaba da aikin su har suka kammala gab da lokacin da ake kiran sallar magriba. Sallah suka yi suka ci abincin da suka dafa har suka kammala.

Mahaifiyar tsahare na dawowa , tsahare ta labarta mata abin da ya faru tsakanin Ayaman da Yunusa.
"Kai jama'a, umma ta faɗa (mahaifiyar tsahare) yanzu shi yunusa har lalacewar tasa takai haka?"Gaskiya Allah ya kaimu gobe muje gurin maigari ya dawo da ke hannun mu tunda abu yaqi ci yaqi cinyewa, Ladiyon ba imani ba ga ƴaƴanta marasa ji kuma baza ta tsawatar musu ba."

"Badai a gidana ba." mahaifin tsahare ya faɗa yana ƙarasa shigowa cikin gidan, haka kawai, yarinya ba dangin ku ba kun bi so kuke ku liƙa mana ita, yarinyar da ta qi auruwa? Salan ta zo gidana ta shafama yayana baqin jini, toh wallahi baku Isa ba."
Ya numfasa ya cigaba da cewa "Yau ne kawai zan barta ta kwanan mun a gida amma zuwa gobe zata tafi."

Jiki a sanyaye tsahare ta kalli mahaifin nata tace "Dan Allah baba, wlh Ayaman tana shan wuya gurin Ladiyo kuma naga aure ay lokaci ne in yazo zata yi." Tsahare ta gama faɗa kamar zata yi kuka.

Ɗaki umman su tsahare ta umarce su su shiga, Tsahare ta ja Ayaman suka shige ciki.

Suna shiga dakin, Ayaman tace "Da kin barni na tafi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login