Showing 9001 words to 12000 words out of 29277 words
matsalar ku.", ta cigaba da baƙaƙen maganganun ta.
Addah asiyah ce ta tashi cikin fushi ta sabi jakar ta da takalmi zata fice addah suwaiba ta dakatar da ita.
"Wlh Yaya ki barni na tafi kar ayi abin kunya." addah Asiyah ta karasa fada cikin wata irin murya ta fushi.
"Munga Zaki ma karshen fushi, yarinya ce dai ba za'a bada ba tana nan gidan ubanta." ladiyo ta fada cikin izgili.
Shiru addah Asiyah ta yi ta tsaya suna bama malam isyaku baki amma biriss yaqi karshe ma ficewa ya yi daga gidan bisa umarnin ladiyo.
Tashi suka yi da niyyar tafiya gida dan ba gari daya suke da garin su ladiyo ba.
Tashin su ke da wuya ladiyo ta sheqe da wata munafukar dariya, tace "Allah ya raka taki gona." tana wani watsa yatsu a iska kamar ana kora awaki.
Addah Asiyah ce ta juyo ta mata magana wadda ta sa ladiyo hankada asiyah kusa da bakin rijiya.
"Dama haka nake so." ladiyo ta fada a zuciyar ta.
Addah Asiyah kuwa ta bige da bakin rijiyar, addah sadiyah karamar kanwar inna ta ce ta Kai ma ladiyo duka ta kufce.
Kafin kace me gidan malam isyaku ya kacame da fada, ta ko'ina, Dan ladiyo dama Masha Allah, akwai jibgegen jiki, ga addah asiyah ma mai karfin hali.
Kaf cikin ƴan uwan mahaifiyar tawa addah suwaiba ce kawai ke gefe riqe da kanta da aka buga ma karfe.
Ni kam da ban wuce shekara 10 ba na tsaya tsuru-tsuru Ina kallon wannan tashin hankali.
Malam isyaku ne ya shigo da fadawan Maigari aka tattara mutanen aka kai su gaban maigari, bayan bayanai da yawa maigari ya zartar da hukuncin su addah Asiyah ne marasa gaskiya tunda har gida suka je.
Sannan batun Ayaman tana nan gidan ubanta ba inda zata tunda Yana da halin riqe ta, kuma haka addini ya tabbatar.
Bayan an dawo daga wurin maigari ne su addah Asiyah suka kama hanyar gida ba tare da sun kalli ko inda Ayaman take ba, Amma a zuciyoyin su tausayin Ayaman da kuma alhinin rashin ƴar uwar su ne ya dawo musu sabo.
"Ayaman! Ayaman! Ina kike ne?"
Firgigit AYAMAN ta yi daga duniyar tunanin data Lula .
"Na'am "
ta amsa kiran ladiyon tana fitowa daga ɗakin.
"Ungo abincin rana ne Maza ki cinye."
Ladiyo ta fada tana miqa mata kular abinci hade da lemon kwalba.
"Toh, nagode." Ayaman ta fada cike da mamaki qarara a fuskar ta .
Ladiyo ta lura da mamakin nata ne yasa tace "ko baki yafe min bane Ayaman?" Ta ƙarasa fada cike da makirci.
"A'a ba haka bane inna na hakura."
"Yawwa diyar albarka nagode."
Tashi Ayaman ta yi ta shiga dakin ta, yayin da ladiyo ta bita da kallon tsana ta ja tsaki kasa-kasa.
AYAMAN na shiga dakin ta , ta zauna tana ta mamakin halin Ladiyo, dazu fah ta gama hantarar ta ita ce yanzu har da abinci,
"Allah ya kyauta" ta fada tana daɗa jinjina lamarin.
Bude kwanon ta yi taga shinkafa da miya ne har da salak a kai, mayar da murfin ta yi ta ajiye kwanon gefe dan har ga Allah tana tsoron cin abincin nan duba da daga hannun wacce ya fito.
********************************
*DELU*
Ta bangaren delu kam likafa sai cigaba take dan yanzu har ta kai Mariya kullum tana kofar gida da wani saurayin an zo zance.
Haka ma malam surajo ya yi wani kala da shi duk ya firgice, banda umarnin delu ba abinda yake bi, sai hidima yake mata ita da diyar ta.
Yanzun ma zaune suke a tsakar gidan suna shan iska,Dan cikin ya yi zafi da yawa.
Mariya ce ta fito daga daki tana fadin, inna wai Ina abincin ne? Cike da muryar shagwaba.
"Laaa malam, waken tun dazu bai kammala dahuwa bane?" Delu ta fada tana kallon mijin nata.
"Na manta ne, Amma nasan yanzu ya yi kam." malan surajo ya karasa fada cikin sauri dan baya son fadan delu.
"Shi ne kazo nan ka rashe, ka saki baki kana surutu , Amma dai anyi lusari wlh." delu ta karasa fada tana riqe haba.
Ta koma kan Mariya tace "yi hakuri 'yar mama, yanxu abincin zai kammala, kinji."
"Yawwa inna na manta ban gaya miki ba, su ladiyo dazu aka kaisu fadar maigari akan wannan shegiyar Ayaman din."
" Ke habaa! " Delu ta fada tana bude baki kamar taga wani abin mamaki.
"Wlh fah, dazu da iliya yaxo yake fada min."
"Kuma banji maganar ba." delu ta fada, sannan ta cigaba da fadin.
"Wannan iliyan bana son alaqar ki da shi wlh, dan ba wani abin arziki yake tsinana miki ba."
"Toh shikenan." Mariya ta fada.
"Wai inna alhaji gabatari ne? kwana biyu Bai shigo ba.
" Wlh ban San masa ba, Amma qila yau yazo."
"Toh shikenan. "
Sai mun hadu a next page, thanks love you all 😘 ❤️......
Khairat 🖤🖤✍️✍️
https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈 MUGUNTA 😈😈😈
By
Khairat 🖤✍️
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 17-18
Hira delu da diyarta suka shiga yi,har malam Surajo ya kammala girkin ya miko musu.
Shinkafar da ya dafa ta chabe duk ta yi ruwa ta yi kamar tuwo, fuskarsa cike da tsoro kamar wanda ke gaban Zaki, ya rusuna ya aje shinkafar hade da kallon ladiyo.
" Har ka gam... " Bata karasa maganar ba ta kalli inda shinkafar ta ke.
" La'ilaha illallah, abinda ka girka kenan, lallai ma malan." delu ta numfasa sannan ta cigaba da fadin "haka ma jiya ka yi mana wannan iskancin, wai meye a kanka ne? Tunanin uban me kake?". Ta ƙarasa fada kamar zata kaiwa malam surajo duka.
"Hehehehe" mariya dake zaune ta sheqe da dariya, "wato ada in ni ce nayi wannan girkin ay duka da zagi ba wanda baka min baba, amma yau wai kaine da girki, waii giwa ta fadi, hhhhh." Mariya ta ƙarashe da dariya.
Umarni delu ta yi ma malan Surajo akan ya zubar da shinkafar ya ɗebo wata sabuwa ya dafa.
Ta bangaren malam Surajo kuwa, ya rasa me ke mai daɗi, wani ciwon kai na azaba yake yi, ga shi ya rame ya kanjame tamkar wanda ya yi cuta.
Yana mamakin yadda Mariya ta gayamai magana har ya hakura ya yi shiru, dan ba damar ramawa, koma dai mene ya san duk inda aka je aka dawo dole ya bi umarnin delu.
"Baza ka tashi bane." delu ta faɗa a ɗan tsawace.
Zumbur ya miƙe ya nufi madafar tasu, takaici cike a ransa ya dauko wata shinkafar ya wanke ya dafa.
Yana girkin yana jiyo hayaniyar delu,
"Saura kuma ka kuma lalata shinkafar, wallahi kaji na rantse kayi ta dafa sabuwa kenan." Delu ta fadi cike da daga murya wanda mutumin dake waje zai iya jiyo ta.
Cigaba da girkin sa ya yi har ya kammala, "alhamdulillah ." ya faɗa ganin shinkafar bata chabe ba.
"Assalamu alaikum. "Muryar Ladiyo ta karade gidan .
"Waalaikumus salaam ƙawar arziki, yanzu nake son zuwa gidan naki."
Ladiyo ta watsa ma ta wani kallo, sannan tace "dama kin samu duniya ba dole ki sha re ni ba".
"Wallahi ba haka bane, ƙawas." delun ta faɗa tana wani fari da idanu.
"Waya ga fara, hhhh." ladiyo ta faɗa sannan ta cigaba.
"Ni ba wannan ba ma, kinsan gobe zamu koma wurin bokan....." .
Bata karasa ba delu ta yi azamar rufe ma ta baki, alama ta yi mata da ta yi shiru.
Janta ta yi zuwa dakinta, matsar da tulin kayan dake kan gadon tayi sannan suka zauna.
"Mene? Naga kin jayo ni daki."
"Zaki ɓallo min ruwa, malam fa yana nan."
"Dan malam na nan shi ne kika wani jayo ni, mchteeww." ta karasa da jan wani uban tsaki.
"Ladiyo kar yaji fa aikin ya lalace."
"Yanzu dai ba wannan ba kin shirya koma wa wurin bokan kan tudu?" Ladiyo ta katse maganar.
"Ehhh, ina abubuwan da ya buƙata?" Delu ta tambaya.
"Ni kinsan aiki na daban, dan haka tsakani na da shi ne, sannan kuma wannan yarinyar kin san har gaban maigari ta kaimu Ni da malam?"
"Hmmm", delu ta ja numfashi sannan ta cigaba da fadin "ay dazu mariya ke gaya min, amma kwa in haka ne Ayaman ta fara sanin kanta".
"Ke dai bari delu, yanzu jiran lokaci nake ƙanƙani, na fara musguna ma ta wanda ya fi na da .
"Haka nake so muniya ta. " hannu suka tafawa sukayi sannan suka cigaba da hirar har malam surajo ya kammala girkin ya kawo musu.
Ladiyo dai tayi dariyar ta har ta gode Allah, sannan ta chachakali abincin.
Sai wurin magriba ta fito daga gidan delu, akan alƙawarin gobe zasu koma kogon boka.
*Ayaman*
A bangaren Ayaman kam tun lokacin da Ladiyo ta kawo ma ta abincin nan ta kasa ci, sai tunani da ta ke ta fama da, da kuncin rai.
Da ta gaji da tunanin, ta miƙe ta fita zuwa gidan su tsahare, ta yi rashin sa'a tsaharen bata nan, dan an sa ranar auren ta da Umar dan ƙanin baban ta, dan haka ta koma gidan babbar yayar ta domin horon aure.
Abinci babar su tsahare ta zuba ma ta, godiya ta yi,ta hau cin abincin su na ɗan taɓa hira.
Bayan wani lokaci ta tashi ta nufi gidan, Anas ta tarar yana kofar gidan da niyyar aika yaro yayi kiran ta.
"Assalamu alaikum." ta faɗa cikin sassanyar muryarta.
"Waalaikumus salaam ." Anas ya amsa ma ta cikin murmushi.
"Ya gidan?, naji abinda ya faru,me yasa kika kai su baba gaban maigari?"
"Lpy kalau, wallahi yaya(dama haka ta ke kiran Anas), ni ma ban so ba , tsahare ce ta bani shawarar hakan, duba da yanda inna ke azabtar da ni".
Ta ƙarasa maganar kamar za ta yi kuka.
"Toh meye kuma na kuka, shikenan na bar maganar. "
Shiru ta yi bata amsa masa ba.
"Amma ba'a son kai iyaye kara, saboda darajar da Allah ya yi musu, ko ba komai inna Ladiyo ay ta haife ki, dan Allah kar na ƙara ji". Ya karasa da alamar jan kunne.
"In sha Allah, yaya" ta amsa mai.
Hirar su suka cigaba da yi irin ta masoya har ladiyo ta ƙaraso, sakin baki tayi tana kallon su, ko me yazo mata a rai kuma ta saki wani murmushi.
"Ahh ah , su Ayaman ne anan, sannun ku toh." ta faɗa tana washe baki hade da russunar da kai kamar mutuniyar arziki.
"Inna Ina wuni." Anas ya gaishe ta cike da ladabi.
"Lafiya kalau ɗan albarka, ya mutanen gidan?"
"Alhamdulillah inna ya gida ya yau?"
"Wallahi qalau."
"Toh Ma sha Allah."
"A gaida mutanen gidan. " Ladiyo ta faɗa tana wucewa.
Har ta je bakin kofa kuma, "Ayaman ki shigo da shi ciki mana."
Ayaman dake tsaye tana kallon dramar ladiyo, ta amsa ma ta da "toh".
Kallon Anas ta yi ta kalli kofar da Ladiyo ta shige ciki, tace "tabb".
Sallama sukayi, Anas ya wuce ita kuma ta shige gida.
Tana shiga ta ɗauki buta ta shige banɗaki, tana fitowa ta daura alwala, ta nufi daki dan gabatar da sallar magriba.
Ladiyo ce ta shigo dakin ta tarar da Ayaman kan zanin da ta ke sallah.
"In kin idar da sallah ga garin tuwo nan ki tuƙa mana da miyar kuka."
"Toh inna." ta amsa ma ta sannan ta bita suka fita tare.
Garin ta fara tankade wa sannan ta daura ruwan a kan murhun.
A ƙasa da awa ɗaya ta kammala girkin kasancewar da iska a garin.
Tana gamawa ta wanke kwanonin ta tattare murhun wuri ɗaya.
Ladiyo ce ta fito daga ɗakin ta, "yawwa, sannu ƴar albarka".
"Yawwa inna".
Kwano ta dauko ta bawa Ayaman din ta zuba nata har da man shanu da yajin daddawa mai matukar kamshi .
A tsakar gidan ta shimfida tabarma ta yi zamanta ga hasken watan da ya haskaka ko ina tarrr kamar rana.
Iskar dake kadawa hade da kamshin abincin, da kuma hasken watan ya bada wani yanayi na daban, tunanin rayuwar su ta baya ta fara.
Kwance ta ke a kan cinyar innar ta tana shafa mata kai, yanayin yayi dai-dai da wanda take ciki yanzu, ta tsuniya ta ke bata a lokacin.
Abban ta ne ya shigo da sallama, sannu da zuwa sukayi mai, bayan ya nitsu innar ta gabatar da abincin dare wanda
tuwon masara ne da miyar kuka.
Tsire da fura abbanta ya fito da, daga jakarsa. Bayan sun kammala cin abincin ne innar ta ta dauko furar tana damawa suna taɓa hira har ta kammala suka cinye kayan su...
Firgigit ta dawo daga tunanin, hawaye taji yana sauka daga idanun ta, kallon tuwon ta yi, ji tayi gaba daya ya fitar mata daga rai.
Rufe abincin ta yi ta kai ɗaki ko dan da safe, alwalar bacci ta ɗauro, kichibis ta yi da Ladiyo tana fitowa daga ɗakinta, sallama ladiyo tayi mata. Ita kam tana ta mamakin ladiyo da dabi'ar ta ta ke.
Daki ta shige ta yi shafa'i da wutiri sannan ta yi addu'arta ta kwanta don bacci......
Ladiyo kam sai da ta raba dare tana tunani da kuma jiran shigowar Nabila.
Sai wurin sha biyu na dare sannan Nabila ta shigo gidan, da gasashiyar kaza, zama sukai suka tadar wa kazar har sai da suka cinye sannan sukai kwanciyar su...
Love you all 😘 ❤️ ❤️
Khairat ✍️✍️✍️🖤https://chat.whatsapp.com/IiFZaLvHaXWJSlqsXgayfB
*(Posting room)*
*My WhatsApp group comment section 👇👇👇👇👇👇*
https://chat.whatsapp.com/EF8H5r2xZU81B9Fj9qafY8
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
😈😈😈*MUGUNTA*😈😈😈
By
Khairat ✍️🖤
BISMILLAHIR RAHMNIR RAHIM
Page 19-20
Sai wurin sha biyu na dare Nabila ta shigo gidan,da gasashiyar kaza, zama sukayi ta re da cinye kazar,sannan suka mai da haƙarƙari suka kwanta.
*5 star hotel*
Hausawa suka ce dare mahutar bawa, amma a wannan wurin hakan ya bambanta.
Hotel ne na manyan mutane, iya tsaruwa wurin ya tsaru, amma kash! Ba abinda ake aikatawa a wannan wurin sai alfasha da saɓawa Allah (wa'iyazubillah).
Babban hall ne dake cikin hotel din, fitilu sun haskaka wurin sai ya yi kamar rana ce ba dare ba, cikin hall din kuwa fitilu ne masu mabanbantan kaloli wanda ya haɗa da jar kala, kore, shudi(blue), da sauransu.
Waƙa ce ke tashi a wurin, wanda tun daga harabar hotel din ake jiyo wa, samari da ƴanmata ne chakude a wurin kowa da abinda yake .
Wasu na zaune a kujerun sofa din dake wurin su na shaye-shaye, yayin da wasu ke tsaye suna kwasar rawa, wasu ko na abinda bai kamata ba.
Wani kyakkyawan saurayi ne ke zaune a ɗaya daga kujerun sofar dake cikin hall din, ya sha giya ya yi tatil, ga matan banza zagaye da shi, surutan banza yake ta yi wanda ke nuna a bige yake.
Wata matashiyar budurwa dake ta tiƙar rawa tun dazu ce ta taho zuwa inda yake, kallon matan da suka zagaye shi tayi sannan ta watsa musu kallon banza.
"Dallah ku tashi ku bani wuri, sai kace mayu kun zo kun sa shi a gaba." ta karashe maganar cikin yatsina fuska gami da kallon banza.
Sumsum suka tashi daga inda yake, dan sunsan halin Nafee.
Amrah ce kaɗai ta zauna saboda sun saba faɗa da Nafee.
"Baki ji me nace ba?" Nafee ta tambayi Amrah hade da ƙare ma ta kallo.
"Ehhh, bazan tashi ba, in ubanki ne wanda bamu san asalin sa ba, ya sayi kujerar sai ki tashe ni." Amrah ta gaya ma ta tana kauda kai gefe.
"Kut....... Nafee ta auno wata uwar ashariya ta danna wa amrah, sannan ta chakumo wuyanta, tai ma ta wata irin shaƙa wanda da ƙyar amrah ke numfashi.
Da yake mutanen banza ne a wurin, ba wanda ya yi yunƙurin raba su faɗan, sai ma waya da suka ciro suna