Showing 24001 words to 27000 words out of 33116 words

Chapter 9 - DAFIN SO Document Complete By maji dadin kainuwa.txt

tayi har k'asa tace "Ina kwana Inna, an tashi lpy "kafin ta amsa Sulaiman dake parlo zaune yace "Momy ke nake jira ".cikin sauri ta ture Momy ta shigo parlon tace "yauni Uwani naga bala'i wato Sule iskancin ka ya wuce wuri kai baka gaishe ni ba, kuma baza ka bari Uwar ka ta gaishe ni ba, to kayi kad'an ae Uban ka Abdullahi ya duka har k'asa ya gaishe ni, D'an iska kawai, to ma wai gidan uban wa zaku je da sanyin safiyar nan? "
hade fuska Sulaiman yayi yace "ki na da matsala da wannan ne, ko aeken mu kika yi ne? "
Kafin ta basa amsa ya dauki hijab din Momy dake kusa da shi yaja hannun ta suka fita, a gate ya saka mata Hijab din har k'asa mai hannu sosai ta yi mata kyau, jin Inna na shirin fito wa yasa ya saka Momy mota ya ja su ka bar gidan a tamanin.
"tsohwan munafiki wallahi zaku dawo ku same ni harda Uwar ka dake goya maka baya duk zanyi maganinku, bazaku daura mun hawan jini ba, kai wallahi Sule ya cuce ni, Abdullahi ya haifo abunda yafi karfin sa ".
A mota Momy tace "wai Sulaiman baza ka daina wa Inna haka ba bana jin dad'i"
"kiyi hakuri, amman abun ta yawa yake yi, ki barni da ita kawai "tunda ya fadi haka har suka iso gidan da zasu je be kuma cewa komai ba. Har cikin Gate din gidan mai gadi ya bude masu suka shiga, tun da su ka fito mota idonsa ya sauka akan na Arif da sauri ya iso wurin sa ya rungume sa don sarai ya gane sa "ur welcome Uncle "ya fad'a sannan yace wa Momy "Good morning ","Morning too "jin wani irin son yaron tayi a ran ta.
"ina twin naka? ",dariya Arif yayi yace "gashi yana kallon ka, ae haka yake shi ",Kama hannun yaron yayi suka isa inda Anif yake shima ya rike hannun sa, amman ko kadan yaki ce masa komai tun daga gaisuwa.
"kaje ka cewa Ammi tayi baki a waje, and what's ur name ".
Zaro ido Arif yayi yace "jiya bana fada maka ba "
"ae bana iya banban ce ku ne friend ".
Dariya kawai yayi yace "I'm Arif ,bara na fada mata "be jira amsa ba yayi ciki da gudu, ba jimawa ya dawo ya samu ya sab'a Anif a kafada yace "she say u can come in "shi yayi masu jagora har dakin Ammi suka zauna parlo suna jiran fitowar ta.
Majidadi✍🏻
Stylish Star ✨✨




*Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…*
*____________________________________*


*πŸŒˆπŸ‡°AINUWA πŸ‡ΌRITER'S✍🏼*
*πŸ‡¦SSOCIATION🀝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*


πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡
*DAFIN SO*
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


Story and writing by
*Maryam Ismail*


*MAJI DAD'IN KAINUWA CE* ✍🏻


facebook
Maryam ismail(maji dadi)
Inster
maryam maji dad'i


Page 107 to 108


Cike da fara'a ta Kara so parlon, dogon hijab ne jikin ta ita ma "sannun ku da zuwa "abunda ta fada kenan ta na zama kusa da Ammi.
"ina kwana, mun same ku lafiya? "Momy ta fad'a
"lafiya qlau Alhmdllh"kallon ta sosai Ammi keyi sannan ta kuma yin murmushi tace "Momyn Maryama ko ?"
Dariya kawai Momy tayi, "Anif kaje kace Aunty ta kawo wa bak'i abun sha "
"aeko da kin barshi daga gida muke yanzu "cewar Momy
"haba dai"
Sai lokacin Sulaiman yace "ina kwana Hajiya "
Murmushi ta fad'ad'a don tsab ta gane sa,tace"lafiya qlau yaron kirki"bude d'akin da aka yi ne ya maida hankalin su a Door din, wani irin yanayi Momy ta tsinci kan ta ciki, tun daga k'asa take kallon matashi yar budurwar har zuwa sama hannun ta rike da tray har ta ajiye sa k'asa bata dago fuskar ta ba, Momy kam tuni ta gama gane wacece kallon ta takeyi hawaye na ambaliya akan fuskar ta, wani irin yanayi take ji muryar ta na sarke wa tace "Janna "
Das das haka gaban Janna ya bada sauti kafin ta dago idon ta ya cika da ruwan hawaye kasa furta komai tayi lokacin da idanuwan su ya sarke da na juna, da gudu ta isa wurin Momy ta fad'a a jikin ta tare da fashewa da matsanan cin kuka har kyarma kyarma takeyi a hankali tace "Momy na "tattara yaran Sulaiman yayi suka fita daga dakin baya so su fahimci wani abu akai, a kofar fita yaci karo da Faruq "ga Appie na "Anif ya fad'a yana kokarin sauka daga jikin Sulaiman, sauke shi yayi da sauri suka rungume sa suna murnar ganin sa, hannu ya ba Sulaiman suka gaisa yace "ina kwana, sannu da zuwa "
"lafiya qalau Omar, mun sameku lafiya? ",murmushi yayi yace "Alhmdllh, muje daki na ko "be musa masa ba suka nufi dakin sa, a compound Arif yaga yara na ball wurin su yayi da gudu, Anif zai rufa masa baya Faruq ya rike sa da sauri yace "Why always that Ahmad, kada kayi gudu ko ball pls "
Murmushi kawai yayi yace "to Appie zan kalla ne kawai "be jira me zai ce ba ya yi gaba abun sa, sannan suka ida sa dakin nasa, drinks ya basa masu sanyi ya karba malt kawai yace "this will be ok, thank u ",fira suka fara sama sama sannan Sulaiman yace "pls a ina kuka hadu da wancan uwar rawar kan? "
"Adamawa "ya basa amsa, zaro ido Sulaiman yayi yace "ur joking Man, ita fa y'ar Abuja ne, infact bata tab'a zuwa Adamawa bafa ".
Murmushi Faruq yayi yace "to this time taje ae "nan ya kwashe labarin haduwar sa da Janna ya fada masa da irin wahalan da tasha kafin tabar garin, jinji na kai kawai Sulaiman yayi yace"mun gode Captain Faruq da ace ana samun muta ne irin ku da anji dad'i sosai a rayuwa, Allah yabar zumunci "
Da Ameen kawai ya amsa suka ci gaba da fira kamar Sun sa ba.
B'angaren su Momy suma abunda ya faru kenan tallabar fuskar Jannat Momy tayi da dukkan hannayen ta tace "Ashe zan ga wannan rana?, Janna ina ki ka tafi ki ka bar maman ki da kewar ki?, waya fada maki ana fushi da gida?, kullun Maman ki addu'ar ta ta sake ganin ki ko da sau daya a rayuwar ta"Sosai ta rike hannun Momy cikin na ta tace "Momy na daina, ki yafe mun, ba fushi na yi daku ba, kullun ina tunanin ku, ina gudun Abba ya tsine mun ne, ko ya sakeki Momy ".
"dana rasaki Jannat ki fada wani hali gara na bar aure na don na tallafi rayuwar ki, Jannat ina cikin da kika fita dashi?, ki fad'a mun waye ya maki ciki? "
Hawaye ne suka soma zubo mata ta kasa cewa komai, Ammi tace "yaran da suka fita anan Ahmad da Faruq sune abunda Maryama ta haifa, rabon su ne ya gifta da kaddarar ta, kinga Maryama yanzu ba lokacin kuka bane ya zama dole mahaifan ki su san komai, boyon da kike masu ne yasa kuka shiga wannan halin na yanzu ba dogon bayani yanzu kin ga illar k'awa ,ba ko wacce kawa ake bawa amana ba, maza ki share hawayan ki kibawa mahaifiyar ki labarin abunda ya faru dake, in dai na isa da ke "
"Ammi kin isa da ni, a rayuwa kinmun abunda bazan iya rama maki ba, ina maki kallo tamkar mahaifiya ta, kin so ni lokacin da na rasa gata kowa ya guje ni ,umarni gare ki kawai nake buka ta don na tabbatar maki kin isa dani ".
labari taba Momy tun daga haduwar ta Ashman da Ahmad har zuwa ranar data bar gida da abunda Madinat tayi mata babu abunda ta boye mata.
"ban taba tunanin na haifi jarumar y'a ba sai yau, kin sha wahala a rayuwar ki, Allah yayi maki albarka, Allah ya tsare mun ke, duk in da Ahmad yake dole zamu ne mesa ,tun da shi dama yana son yaran sa, yanzu dole ki wanke kanki a gaban Kakar da y'an uwan ki wanda kowa ke maki kallon karuwa "gyada kai kawai tayi tace "To Momy ".
"Maman Faruq na gode kwarai na gode Allah ya saka da alkhairi, kin mun abunda har na koma ga mahalicci bazan taba mantawa dake ba, bana da abunda zan iya biyan ki dashi sai dai addu'a, wanda ba don ke ba bansan wannne hali y'ata zata fada ba, sai dai ina neman alfarma ki ara mun y'ar taki tamun kwanaki kafin ku tashi wucewa, don bazan ce ta dawo gare ni ba ".Momy ta fada.
murmushi Ammi tayi tace "ki godewa Allah, kuma d'a duk na kowa ne, baka san wazai rik'a kaba, ba damuwa amman kuje da Faruq yaga gidan sai ya kaini Insha Allah idan nayi waya da Abban su, amman dai zaki mun wayau ki dauke mun mazaje gaskiya "
Dariya duka suka saka tace "wa ni dai In ba cefa ne fasa auran zanyi gaskiya "duka Suka Kara saka dariya.
"to Maryama kije ki kama yaran kuje, sai nazo insha Allah, kiwa Yayan ku magana ".
Da to ta amsa ta fito ta kira su Arif, cijewa yayi yace "Aunty ina zaki je damu? bayan ball nake yi"
Wani wawan kallo ta jefa masa tace "ban sani ba, kuma karka wuto ka kwana anan ".jan hannun Anif tayi a hanya taci karo dasu Ammi harda su Faruq an Kira su, marairaice fuska tayi tace "Ammi ban yiwa Ibtihal sallama ba fa "
Kallon ta kawai tayi tace "nace kawai ki tafi, mazo daga baya, kinsan basu san komai game dake ba, kinsan yanzu idan kika je gida sulhu zaku je ko ".
Bata kuma cewa komai ba sukayi sallama ita da Momy sai boy's din ta ne baya sai Faruq da Sulaiman a gaba suka dauki hanyar gida. Sai da Ammi taga tafiyar su sannan ta koma dakin ta twin's na nan a zaune "Ammi ina Auntyn Twin's?"
"na siyar da ita, ko zama banyi ba kin jefe ni da tambaya ".
Kasa da kai Ibtihal tayi tana murmushi tace "kiyi hakuri na damu ne da ban gan ta ba "
"ok taje gida ,baki tashi bacci bane time din ba"
"Momy wanne gida? "
"gidan iyayen ta mana, na gaji da tambayar nan Ibtihal ".
"kice ta dai je kauye dubo gyatumi,Allah yasa ka da ta dawo wallahi, a haka zata kare dai da ganta li "Ibtisam ta fada tana yatsine fuska.
"tashi barmun daki, har abada bazaki taba hankali ba kedai,Allah ya shirye ki"Ammi ta fada.
Mikewa Ibtisam tayi tana turan baki tabar dakin.


Suna isa a parking lot Sulaiman yayi parking, sai da kowa ya fita a motar ita tana zaune, kallon ta Momy tayi, tayi mata murmushi tace "feel free y'ar lalen Abba muje ".
Zaro ido tayi sai kuma hawaye a sannu ta safko kafar ta cikin gidan wanda tayi tsawan shekaru ba ta cikin sa, yana nan yacce yake sai dai gyararraki da fenti wanda duk basu ta sani ba ,ji tayi wani irin sanyin farin ciki na ratsa ta, kafin suka shiga aena hin main parlo na gidan, Faruq yasha mamaki da ganin girman gidan da tsabar dukiyar da aka narka ciki a ranshi yace ashe y'ar mai kudi ne ita, dafe kirji Inna tayi tace "na shiga ukku yau naga abunda ya ishe ni be ishi Allah ba, wa nake gani kamar Janna, kin gama yawo Kin dawo, abunda bazai yiwu ba kenan "jin hargowar Inna yasa y'an gidan fitowa harda Abba aka soma kallon kallo.
(gaskiya bana jin dadi, kun daina comments a book din nan, bana gane ko sakon na isowa gare ku, idan bakwa so saiku fada na daina wahala kawai, ta hanyar comment ne zansan me nakeyi)
Allah ka gafartawa iyayen mu, kayi mana kyakyawan karshe
maryam majidadi✍🏻
stylish star✨✨




*Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…*
*____________________________________*


*πŸŒˆπŸ‡°AINUWA πŸ‡ΌRITER'S✍🏼*
*πŸ‡¦SSOCIATION🀝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*


πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡
*DAFIN SO*
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


Story and writing by
*Maryam Ismail*


*MAJI DAD'IN KAINUWA CE* ✍🏻


facebook
Maryam ismail(maji dadi)
Inster
maryam maji dad'i


Page 109 to 110


"ka wani yi mun tsaye a kai Abu, shin zuba mata ido zakayi tana kallon ka?, da idanuwan ta kamar na mayu, maza tabar gidan nan wallahi "Inna ta kare tana kumfar baki.
Kamar muna fuka haka Janna ta taka kafan ta zuwa gaban Abba da niyar ta duk'a, saurin rike ta yayi kafin ta kai k'asa, hawayen da take makalewa ne suka gangaro mata ta rungume sa tace "Abba nayi kewar ka, don Allah Abba ka yafe mun bazan kuma ba, Abba wallahi ba'a sani na nayi ba "
"kaji iskan cin banza ki Kai kanki ga k'ato kuma kice baki san anyi ba, yau naga abunda ya ishe ,wallahi yarin yar nan Abu ka haifa wa kanka fiti na, ta iya tsara labari da shegiyar karya "Inna ta fad'a
D'ago kan ta yayi yana murmushi yace "ni ban rike ki ba arai Mamana, fushin zuciya ne kawai, amman ya akai haka ta faru?, nasan ba halinki bane Mamana, ina kika je? bayan Kin tafi "
Wani mugun kallo Inna tawa Momy tace "ae hankalin ki ya kwan ta Kin kawo mana anno ba a cikin gida, Allah dai ya sakawa d'ana wallahi ae akwai hisabi dai, a dai rika tunawa da Allah Indo "
Momy bata ce komai ba, ta Kama hannun yaran takai gaban Abba tace "ga rabon daya samu, kayi hakuri Allah dai ya rubuta dole sai yaran Sun zo ta haka "
Sakin Jannat yayi ya rungume yaran yana jin tsananin kaunar su har a ransa, kallon Jannat Anif yayi yace "Aunty who is this Man ".
Sulaiman yayi murmushi yace "is ur Granfa, ur Momys Father "
Waro ido Anif yayi yace "No, but what about Abban Adamawa?
Murmushi Faruq yayi yace "bana son tamabaya shima Baban ta ne, wannan ma Baban ta ne, baban Abuja".
Washe hakora Arif yayi yace" kamar mu ga Appien Adamawa ga Appien Abuja ".
"muje mu zauna"Sulaiman ya fad'a ,Sawam ya kallah yace "ka kaiwa Sadiya yaran nan ".
Da sauri Inna ta jawo yaran jikin ta ta rike tace "yau naga bala'i saboda shegen hassada sai kasa a fitar dasu banga jikoki na na, wallahi Sule Allah zai saka mun duk abunda kake yimun, kuma ba su zuwa wallahi "
Ta gefan ido ya maka mata uwar harara, yayin da Sawam ke boye dariyar data taho masa
"kawa uwarka Aisha dariya gata nan "
Bata an kara ba taji ya janye hannun yaran yayi waje yace "yaran da kike aeban tawa ne zan baki "
"ka kama kanka Sawam bana son sakarci "Abba ya fada. Dakin Aunty Sadiya yakai yaran yace "uwar Humaira ga yaran Jannat fa ,zasu zauna nan suna magana a parlon ne "
"to Masha Allah yaran harsun girma haka, what's ur names boy's "
"am Arif, my Twin Anif "Arif ya bata amsa, labari suka ci gaba da bata iri iri tana shan dariya ga Humaira ma ta sake jiki sai wasa suke yi, banda Anif dake gefe yana kallon cartoon.


Zaune suke duka a parlo, suna sauraran ta, tana basu labarin yacce ta zauna da taje Adamawa, sosai suka tausaya mata, Abba yayi dana sani sosai, Inna hawaye ta matse tace "haka kawai da raina an cuci y'ata, ka kore ta Abubakar, bancin da Allah yasa ta hadu da yaron nan na kirki daya kake gani mezai faru da ita, Allah ya maka albarka yaro, kai d'an arziki ne, ka kaini gidan ku dan Allah nawa iyayenka godiya ".jinji na kai faruq yayi lallai lamarin tsohuwar nan akwai tsufa a ciki


*******
"ka tabbata Baba mai gadi, Jannat na cikin gidan nan "Madina ta fada tana nishi da kyar ga y'arta jaye a hannun ta


"eh ae tunda kika sakani aeki nake maki, suna ciki ki shiga "godiya tayi masa sannan ta shiga cikin gidan bakin ta dauke da sallama ,kowa kallon sa ya koma gare ta, bata zarce ko ina ba sai gaban Jannat tuni hawaye Sun malaye fuskar ta tace "dan Allah maryama ki yafe mun, wallahi sharrin shaidan ne da son abun duniya, gashi komai ya dawo kai na, dan girman Allah ki yafe mun "
"ta yafe maki uban me, me ?kuma ya hadaku ?,daga gani kin zalin ce ta da yawa wallahi shiyasa kika marairai ce haka "Inna ta fada
"kinga dai na kukan nan haka Madina ki fada mana me yake faruwa ne ?"
share idon ta tayi ta basu kabarin duk irin abubuwan da suka yiwa Jannat sannan tace "nasan ban cancanci yafiya ba, amman don Allah ki daure ki yafe mun dan nasan hakkin ki ne ke bina, kuma ni tawa tazo karshe ga y'ata Lamrat dana haifa y'ar Alhaji sabo ce kuma yace bazai Karba ba "
Salati Inna ta Saki tace "makira Allah ya isa wallahi, Allah ya sakawa jika ta, ni dai nasan bana da jinin karuwai, ashe sharrin ki ne, ae hisabi sai dai gaban Allah kuma".
Share hawaye Jannat tayi tace "kada ki damu Madina, na yafe maki, nima ina neman Allah ya yafe mani laifin dana masa.
Sosai taji dadin maganan Jannat tace "nayi maki alkawari zanje gidan su Ahmad suma na roki gafarar su, ko don na samu rahamar ubangiji.
Inna hararan Madinat kawai takeyi barin ma da taji Jannat ta yafe mata kuma ta dauki Lamrat.
Maryam majidadi✍🏻
Stylish star ✨




[6/30, 1:03 PM] Maryam Maji Dad'i: *Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…*
*____________________________________*


*πŸŒˆπŸ‡°AINUWA πŸ‡ΌRITER'S✍🏼*
*πŸ‡¦SSOCIATION🀝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*


πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡
*DAFIN SO*
πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡


Story and writing by
*Maryam Ismail*


*MAJI DAD'IN KAINUWA CE* ✍🏻


facebook
Maryam ismail(maji dadi)
Inster
maryam maji dad'i


Last page
πŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”š


Inna harare kawai takeyi,ta rasa meke mata dadi dan tsabar haushi da "ni dai ba ruwa na, gara ma ki sakar masu d'iya, kije ki jajubowa kanki masifa da wannan shegen ciwan sai tsami sukeyi, Allah dai ya saka wa jika ta ni dai, dan dai ba yafewa mukayi ba ".


Abba kallon Inna kawai yakeyi shi yama rasa me zaiyi, kullun abunta kara gaba yakeyi.


Sallama tayi masu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login