Showing 27001 words to 30000 words out of 32103 words

Chapter 10 - Sanadin Boko Book 1 Complete Document by Halima I Mashi .txt

musu dry. Don ni nasha
alwashin namiji ya gama ganin hakorina. Mun je kasuwa,
duk abn da zamu bukata gurin walima mun sayi, don
Walima kadai zamu yi kayatacciya, sai dai ta ce, Sagir za
suyi (Dinner) kuma za su yi (Pink & blue day). Kullum
rokona take in je har dai na amsa mata zani. hakan ya
tilasta min siyan shadda kamfala (pink) mai ratsin
bulu,yayin da Shadad na dinka masa(blue) din shadda,
atamfar walima kuwa Rahma da kanta ta sai min.,
Bikinmu yayi kyau, komai a gidana aka yi duk da cewa
ina zuwa gurin aiki da mkrnt, kin yi wa Manaja mgn nayi
don ba zan sake yi mishi wani zance ba, ko neman wani
abu. Ranar daurin aure kam ban je makarantaba, kuma
banje aikin ba, saboda aubuwan sun kwa6e min.
Malamai sun halarci walima, sun kuma yi nasiha akan
mahimmancin yin aure tare da falalar da ke tare dashi.
Sun ja hanklin iyayen yara masu cewa su dole sai
'ya'yansu sunyi boko mai zurfi, ko sai sun kama aikin
kafin suyi aure. da cewa wannan ba koyarwa addinin
Musulunci ba ce. Suka ce, ita mace babu abinda yafi
daraja da mutunci a gare ta irin aure. Sun ce boko ba ya
hana aure, kamar yanda aure baya hana boko. In
'ya'yanku suka lalace saboda kun hana su aure sai boko,
hakika laifin zai fi ta'allaqa a kanku iyaye., Nasihar da
suke yi ta sani shiga dogon tunanin, ni kaina misalice
SANADIN BOKO gani yau na zama 'yar kaina, domin da
ace ban ce bokoba nabi zancan mahaifina nayi auran da
yaso, da yanzun ina tare da dangina da ban kashe auran
iyayena ba, da ban haifi shege ba, da maxa ba su dinga
latsa ni suna son mu lalace ba. Ban san hawaye na
sauka daga idanuna ba, sai dai hannun Rahma naji a
kumatuna tana share min tare da yi min rada a kunne.
Haba Hafsa cikin fa taro ki ke, ya ya za ki ba mutane
damar yin tunanin ke wacece? Please ki share don Allah.
Walima ta tashi lfy, na ce da Rahma bari na leka shop,
kin san ban dauki uxiri ba, ta ce min ba damuwa. Naje na
samu su Ishak, ya ce nasan kuna biki shi yasa ban tashi
ba, na fada mawa manaja cewa zan zauna madadin ki
har ku gama biki, ya kuma san auran Rahma ne shi yasa
bai ce komai ba.Ya kara da cewa, ki koma har sai kun
gama ki mata fatan alheri, mun so muzo daurin aure
amma kin san Manaja. Na ce na gode, ya ce a'a ba
komai, wata rana irin haka zata iya faruwa da mu, na
dawo nake fada ma Rahma ta ce, Ishak da Musa suna da
kirki sosai, dn dai kin kasa Fahimtarsu ne. Na ce, Ba zai
sa don sun kar6ar min aiki in sakar musu fuska ba,
gaisuwa kawai ke hada mu ko da, kuma ita zan ci gaba
da yi kadai. Anje anyo ma Rahma danki(jere) an zo ana
ta lbrn kyan gidan an ce ango ma ya zuba labulaye da
kayan wuta, Sai an kai Amarya sannnan za'ayi sauran
shagalgulan da ango suka shirya, wai ba a son mutane
suyi yawa, sai ka nuna pass sannan zaka shiga. Da muka
kai amarya unguwar Sharada, gidan kam ko ni ya min
sosai, taso in kwana na ce mata ta min hakur sai gobe in
mun hadu gurin (pink & blue day' . Ta ce don
girman Allah kada ki ki zuwa, na ce kin sanni Rahma in
har na ce zan yi abu bana fasawa, ta ce shi kenan, ki
gaida min Shadad. Na tafi ina hawayen rabuwa da
Rahma, don ita wani bangare ne na farin cikina. Gidan
su Maman Rahma naje na dauko Shadad, jikinshi naji da
dumi, ina zuwa gida na bashi (paracetamol) Na kwantar
da shi. Sannan na shiga gyaran gida. Ina zuwa na samu
ma yayi bacci, nayi Shafa'i da wutiru nima na kwanta.
Cikin dare na farka don yin nafila kamar yanda na saba,
sai dai kawai naji jikin yaro sharkaf da zazzabi. Na cire
masa riga na dunga goge masa jiki da ruwa mai sanyi.
Sanna na kara bashi magani, kafin safe Allah ya
taimakeni jikin yayi sauki. Sai dai yan rigin gimun da
yake yi na shiga gidan su Rahama muka gaisa da su
mama, ina zama
Kiran Rahama na shugowa, ina ji dama nasan ita ce, dan
bani da number kowa a cikin zumu dina na daga ina
cewa hajiya kenan, amarsu ta ango. Ta katseni da cewa,
ba wata hajiyarki, shine ko ki kirani da safe ko? Nace shi
kenan sai na hau doka maki kira da safe kisa angonki ya
ji haushi na. Tace wane ango? Kin san Allah ba nan ya
kwana ba, tare da su hadiza kawaye na muka kwana, ba
ke kinki ba? Nace ai gara da na dawo, dan na sami
shadad da zazzabi haka muka kwana. Amma yanzu
Alhamdu lilahi. Tace to Allah ya kara sauki. Tace don
Allah ina sa ido gurin programme din nan, wlh in baki
zoba bikin zai baci, don kina da muhinmanci matuka a
gurin. Nace to zan kokarta duk da shadad nata yan
rigingimu, kin sanshi in baya jin dadi sai yayi ta rigima,
tace yaro kenan Allah dai ya kara sauki,nace amin, yace
kizo da wuri dai. Sai da na fara yima shadad wanka,
sannan na shiga na fito naga gari ya soma hadari, nayi
alawala dan yin sallar la‘asar, haka kawai yau naji ina
sha‘awar shafe shafe a fuskata. Na fito da kayan shafa
da rahama ta di bar min na lefenta, har da jaka da
takalmi da mayafi ta bani duk pink, tun asali ni mai son
yin kyale kyale ce, halin da na tsinci kaina ne yasa na
daina, nafi minti 30 ina kyalekyale a fiska ta. Na dinga
kalon kaina a madubi nasan nayi kyau sosai, har shadad
yana kallo na, nace nayi kyau? Ya daga kai ina kulle gida
rahama na kira na, na daga tace aminiyata ki tai makeni
kada kisa naji kunya, wlh guri yayi guri amma ke kadai
muke jira da wani abokin sagir da ya sauka daga
adamawa state, anje daukoshi daga filin jirgin don Allah
kiyi sauri. Nace to zubaina ganin zuwa amma fa garin
akwai hadari, Allah yasa in sami abin hawa da wuri.
Tsaye nake a bakin titi duk wani dan a daidaitan da yazo
yana dauke da mutane, masu son banza watan yan rage
ma mata hanya suna tsayawa Amma ni ko kallon su
bana yi. Wata jibgegiyar jeep ta zo ta gifta, sai kuma ta
dan dawo.sai tin inda nake ta tsaya, gilashin motar ya
sauka a hankali,naga mai tukin saurayine yana sanye da
shadda yar gaske blue mai duhu, hularshi itama blue ce,
amma kalar sararin samaniya. Ta gefen ido na kaleshi,
sannan na dauke kaina. Yace, yan mata ina zaton guri
daya zamuje in na lura da shigar da ke jikin ki ko? Na
kaleshi nace ba dole hakan ta kasance. Yace, yace ki
shugo muje kinga hadari. Nace kuje na gode. Glashin
baya ya sauka, naji saukar galas din ne da wani sauti da
yayi, amma ban waiga ba, saima na dan kara taku biyu
ta baya na. Muryar da naji ne tamkar in waiga, amma sai
na dake yace shugo mana ga hadari nason zubo da ruwa
gaki da yaro. Na dubeshi dan son in tuna inda na san
wanan muryar, kyawunshi yasa nayi saurin kauda kaina,
tare da cewa kuje ni ba zan shiga ba.daga cikin motar
naji wani yana cewa don Allah mutafi amma za a
taimaka mata tana yiwa mutane yanga,da sauri na
kallesu cikin bacin rai, idanuna har kan kancewa sukayi
don ta kaici, cikin kalon hadarin kaji nace taimako? Ce
muku nayi ina neman taimako? Na dan duka tare da leka
motar, kai me fadin taimakon nan kasani bana neman
taimakon wani abin halita sai ma halincci, ni ban tsai da
ku ba. Na kara rike hannun shadad da kyau, na soma
tafiya dai dai da ruwan ya kece, kamar da bakin kwarya,
ba tsanmani sai naga kofar ta wangale na bakin kofar ya
sauko kafa tare da sauko hannu ya dauki shadad zuwa
cikin motar, a gigice na dubesu yace ki shigo in kuma ba
zaki shigoba ki samemu a can. Amma shi kam ruwa ba
zai dake shi ba. Bani da zabi, tunda sun daukar min yaro
dole na shiga. Gashi bana son dukan ruwan, don haka sai
na shiga. Shadad na ciyar mutimin da muryarshi ke sani
faduwar gaba, kamar na taba jinta ada innaso in tuna
inda nasan muryar ko mai irinta. Muryar ta sake katseni
da tunanin da nake yi, yace ma shadad boy ya sunanka?
A zatona shadad ba zai yi masa magana ba, saboda shi
yaro ne mara son ma gana, musanman in bai san mutun
ba, sai naji yace shadad. Mutumin ya mai maita sunan
shadad, sunanka yayi dadi, to wanan fa? Ya nunani ya
sunanta? Shadad ya kalle ni, na zabga mashi harara,
amma ga al‘ajabi na sai yaron nan ya kauda kai yace
anty. Mutumin yace to kana zuwa makaranta? Yace eh
al‘iman sunan makarantar mu, kuma muna yin (A B C D)
har da(1234). Na rike baki inata al‘ajabin yaron nan,
tunda nake dashi ban taba jin yana rarata surutu haka ba,
harda kin kalona shida ko abu aka bashi da ya kali
fuskata zai gane, in ina nufin ya karba ko karya karba
amma sam ya ki kallona tunda ya gane ina hararan shi.
Mutumin yace gud, kana yin kokari? Yace eh mana, har
ma naci number one, aka min kyautar books. Anty na
kullun tana koya min karatu, da su home work harda ma
islamiyya, ban san sanda nace shut up stupit boy!
Mutumin ya kalle ni, shikuma shadad ya kwanta lakwas a
jikin mutumin. Ya tsorata dan bana mashi tsawa, ko
yawan zaginsa. Na daga can gefen yace. Ke! Wai wane
irin hayaki kanki ya keyi? Ko kuwa ance maki wani kyau
ne dake? Ko ance miki sonki ake yi? Ko kuwa burgewa
ce wannan masife masifen da kike yi. Nace kai saurareni
bana son shishshigi da katsalandan cikin lamari na, nayi
magana da kai? Ko nace ka kalle ni ne bare ka tan tance
kyauna?gani na kayi a filin gasar kyau? Balle kace nace
ina da kyau ne? Masifa kuma dole ku jita tunda ku ka
nace sai kun dauko ni, haka nan bana bukatar burge
kowa cikinku na fison in burge kaina. Don haka yi ta
kanka dan dukanku bakwa gaba na, zaiyi magana mai
dauke da shadad ya daga masa hannu alamun yayi
shuru. Shi kuma yaci gaba da shafa kan shadad wanda
yayi kwance a jikinsa. Wayata ta shiga ruri, ban ko kula
ba dan nasan rahama ce, sai yi take tana katsewa, ana 5
din na daga a kufule, don itama haushinta nakeji ba don
bukin ta bane wa za ya hadani da wayanan gardawan.




Mukhtar Ismail Muhammad
WhatsApp: 08161892123


Sanadin Boko 1-09
Posted by Mukhtar Ismail Muhammad
On
www.arewarulers.com.ng


Under: SANADIN BOKO
Don itama haushinta nakeji ba don bukin ta bane wa za
ya hadani da wayanan gardawan. Cikin fada nace wai
meye ne kika dame ni da kira, ina hanya in kuma zaki
matsa min sai na juya gida abina. Tace mai da wukar
Allah ya baki hakuri, da ma ruwan da ake shekawa ne
nace bari naji ko kin koma gida ne saboda ruwan sai
direban su sagir yazo ya daukeki. Nace na hutar dashi,
gani nan zuwa na kashe wayata tare da tsaki.Harabar
hotal dam yake da jama‘a, ko ince motoci jama‘a sun
cika holl din suna tsayawa na kama kofar zan buduwa.
Ashe daga gaba ne direbab zai bude mu. Yana budewa
na fita, sanan na nufi ciki mai surutun tsiya nan shadad
ba tare da na kalesu ba na nufi wata yar baranda ina ta
yi mashi fadan irin surutun da ya dinga tsugawa acikin
motar, sai ya bale mun da kuka yana fadin.uncle! Uncle!!
Nace yi min shuru ko in mareka, sarkin shishigi, bai daina
kukan ba, na na ciro wayata na kira rahama gani nan fa
ba zan iya shiga ba, mutane sunyi yawa. Ta ce mun
ganki kin tsaya ga Aisha nan tazo zata taho dakegurin
mu tare zamu shiga. Nice a gefen amarya sauran
kawaye suna bayan mu,haka nan ango da abokan shi
suna biye da mu, ina reke da hanum shadad, wanda har
lokacin bai daina gunjin kuka ba, muka shiga. Kidan da
ke tashi kamar zai fasa kwanya yasa naji tamkar in bar
gurin kai tsaye. Wani mai dauke da abin magana yace,
ango da amarya sun shigo, kowa da amininshi zai zauna,
sagir ya zauna gefen shi wanan mutumin, ni kuma ina
gefen Rahama tare da shadad
ta dube ni, mutuniyata wa ya taba ki ne, naga fuskarki ta
kasa boye fushinki, nace uhm! Ke dai bari, abokanan
muijinki ne wlh, sai kuma shadad yaron nan ya kular dani
yau. Tace to dan saki fuskar mana saboda guri ya
kayatu, kisan fushinki zaisa gurin ya dishe. Na harareta
tare da dan murmushi, tace ko kefa. Sagir yace ranki
yadade, ya gajiya? Na nace tana gurinku ya jama‘a?
Yace gasu muna tare nace Allah yasa alheri, da ganan
na maida hankalina gun mai abin magana, yace za mu
kira baban bako kuma baban abokin ango don yayi mana
jawabin maraba tare da dan fada mana wanene sagir.
Sai dai kafin nan babar kawar amarya hajiya hafsat sai
ta bude mana taro da adu‘a, na kali rahama tace please,
tashi kawai. Na mike cikin natsuwa na isa gurin na
amshi abin maganar. Shadad yazo ya rikeni yana kuka,
sai wai abokin ango ya taso ya daukeshi. Bayan n gama
adu‘a na dora da karanbanin nawa, ina bawa jama‘ar da
ke gurin nan shawar kada suyi liki, almubazaranci ne ga
duk mai sha‘awar ya burge ango da amarya su dan ka
musu a hanun su, amma ba dole bane kuyi yanda
nace,sha wara ce. Na koma na zauna, bayan sun bini da
tafi. Shiko da zaije yin jawabin maraba tare da shadad
yaje yana rike da hanunshi. Cikin jawabin ne naji yana
jaddada maganata cewa abinda na fada yayi kyau, don
haka ba‘a son liki, duk wanda zai lika yazo ya ba ango ko
amarya a hannusu. Wanan ma yasa aka kashe rawa da
za‘ayi, rahama ta dinga yi min dariya wai a gaisheni da
karfin hali har ta sanima na dinga dariyar. Sagir cewa
yayi nazo na hanasu rawa, to wane rawa zasuyi ba liki?
Nace tai makonku nayi ai rawa haramun ce ko? Haka
aka ta gabatar da abubuwan da za ayi har lokacin da
akayi sanarwar ango da amarya tare da da masu tayasu
zama dan dibar abinda suke son ci da kansu,
kasancewar dibi da kanka ne za ayi a gurin. Muka hadu
muka jeru amarya tana biye da ango yayinda ni kuma
nake biye da abokin nashi, shi kuma yana dauke da
shadad a kafada tamkar wani danshi. Ango yasa abida
yake so sai fruit ya ce ko zaki tai maka min? Inji abokin
ango tamkar ince a'a amma sai nace me zan sa maka?
Ganin yana sabe da shadad yace ki samin ko menene,
zan ci. A raina nace kaji dashi, ba tare da tsayawa tunani
ba ko mai hanu na yakai shi nake zuba masa, sai da na
shake plate din sannan na bi bayanshi da plate 2. A
gabanshi na dire tare da samashi cokali, na koma ma
zaunina. Sai kurum naji sarkin surutun nan wato mai rike
da abin magana yana cewa, kai gaskiya ango da amarya
kun burge ni, kun zauna da aminan ku kuma mata da miji
har da dansu, to yace ke amarya yaya bakiyi koyi da
kawarki ba kema ki zuba ma ango da kanki? Kai abokin
angon nafa yi maka murna, matar kada kayi mata
kishiya, dubi yanda ta cika maka plate da kaji da kifi kila
abinda ka fi so kenan, wanan ya nuna ko a gida ba a
barinka da yunwa. Sai kurum naji gurin ya dau tafi. Da
sauri na dubi plate din, lallai kam kaji ne da kifi, sai dan
cosilo a gefe, na dubi fuskarshi yana dan murmushi.
Rahama da sagir kuma dariya naga suna ta shekawa nan
take na hade rai tare da kin kai komai bakina. Shiko
shadad sai uban cin naman nan yake yi, shi da mutimin
tuni gurin ya rikice da ciye ciye kowa na diba da
kansaRahama tace to kici mana,nace mata ke ni nama
koshi, ba yan haka ma ni ba zan iya cin komai a taron
nan ba, kowa yana kallona. Haka nan bayan an tashi duk
na matsu naje gida domin magariba ta yi, ina so inyi
sallah sai dai tun da muka fito banga shadad ba, ban ga
mutumin nan ba. Nace rahama ina suke? Tace suna
cikin jama‘a in dan jira. Can nesa na hango wani shago
naje na siyo ruwan naira 10 nayi alwala, nasami gefe
dama da hijabina a jaka, nayi sallah ta. Rahama tazo
tana ce min sun dawo? Nace ke zan tam baya, ina
mijinki? Kune kuka sanshi ku zaku nemo shi. Takira sagir
tace sun ko dawo? Hafsat tana son zuwa gida. Yace a'a
na kira wayarshi kuma a kashe, tace a a to ina ya shiga?
Kai kana inane? Yace gani nan kusa da shago ina kallon
ku ai. Muka nufi girin ango, hankalina ya tashi da rahama
take fada min wai wayanshi a kashe.rahama ta dubi
angon ta tace, ba kace min bako ne ba? Yace eh amma
kano ba bakuwa bace a gurinshi. Ki kwantar da
hankalinki, yauwa gasu nan zuwa ma, duk muka kai
duban mu gurin shi. Yana rike da hanunshi, shi kuma
yana reke da leda. Suna tafe suna yan zan tukansu har
suka isko mu, nace kai ka cika shegen yawo, ina kaje?
Na finciko shi yace anty munje masalaci ne da uncle, ba
kin ce mun wai in dinga sallah a farkon lokacinta ba?
Nace naji ni dan Allah wuce muje na dubi rahama sai
watarana, tace dinner din fa, anjuma karfe 10 naja tsaki
ke kinsan ba zan iya wanan galafirin ba, gara ke sai dai
nazoo. Sagir yace ki bari a kaiki don Allah, gari yayi
sanyi ga duhu, nace nagode, sai anjima nayi gaba.Wani
daga cikin abokan da suke tsaye wanda har dashi muka
shigo motar nan da zamu zo, ya dubi rahama yace kai
wanan kawar taki ta cika masifa, ita ba kyau ba rahama
tace a a kada ka zagar mun kawa masa‘udu, hafsat bata
da masifa,tana da kirki sosai na jima banga mace mai
saukin kan hafsat ba, ita dai abu 3 ta tsana a rayuwarta,
inko mutun ya kiyaye ba mai jin su. Ni da ita bamu taba
yin fada ba koda munyi sai dai ni ni na ta sababi na
amma bata biye min. abubakar lamido yace yanzu kai
kaga masifarta? Ya dubi masa‘udu masa‘udu yace au
yanzu duk abinda take maka baka gani ba? Yace ni kam
me tamin? Bata min komai ba, duk abubuwan da takeyi
sun matukar burgeni. Ya dubi rahama, ni kam in tambaye
ki? Rahama tace ina jin ka, yace amma dai ba matar
aure bace ko? Rahma tace a a daga nan bai sake
magana ba. Duk abubuwan da Abubakar Lamido ke gani
daga hafsat bai taba ganin wani aibunta ba, tunani 1 ya
dameshi, ina ya santa? Shi dai yasan cewa koda a hanya
ne ya taba ganin ta. Anashi ganin Hafsat ta san
mutuncin kanta shiyasa take wanan dabi‘un. Acikin
masauki ya kasa zaune da tsaye, baisan meyasa ya
damu kanshi da dabi‘un hafsat ba, bai taba ganin mace
da ta burge shi irin ta. Yasan daga ganin halayenta za
asha wuya kafin a samu soyayyar ta, duk da bashi da
tabacin sonta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login