Showing 9001 words to 12000 words out of 32103 words

Chapter 4 - Sanadin Boko Book 1 Complete Document by Halima I Mashi .txt

media,yayi murmushi, to ni zan wuce, ina
kayanki? Sai lokacn na tuna da tirena da kudina cikin
ledar gwangwani, na ce to sai gobe. Na tafi ina
waiwayanshi, ina cewa kai,wannan mu2min dan gayu
ne,ga kamshin turare yana yi. Ranar Litinin tsawo naga
ta min,yau kam d murna na iso,na nutsu ban yi wasa
ba,saboda wata zuciyar da ke ce min in ya ki zuwa fa,
ga shi na zo da sabon littafina, ba karamin damuwa
nayi ba da na ga lkcn tafiyarmu yayi ban gan shi ba.
Ina kulle gwangwanaye sai gashi, na ce hr na cire rai,
ya ce ai zan zo, na ciro littafi na ba shi, tare da cewa
wannan takardar ta isa? Ya ce eh, na ce na gode, na
mika mishi gyada tare da cewa na rage mishi ne. Ya ce
ya gode ya tafi. kai, kuruci dangin hauka, nifa
tsakanina da Allah na yarda suke buga kudi. Daga
ranar ban kuma ganin shi ba, Kusan sati 2 hr na soma
tunanin ya gudune da kudina kun ji shirme. Wata ranar
Jumma'a ranar za a yi wa dalibai hutu hr cikin
Makaranta muka shiga muna ta ciniki,mun saida mun
fito sai na hango shi tsaye gurin zaman mu. Da sauri
na isa gurin shi, me bugakudi......


Mukhtar Ismail Muhammad
WhatsApp: 08161892123




Sanadin Boko 1-04
Posted by Mukhtar Ismail Muhammad
On
www.arewarulers.com.ng


Under: SANADIN BOKO
@* NA
Maryam Abdullahi K/Mashi
"Da sauri na isa gurin shi, me buga kudi ina ka tafi na
daina ganinka? Ya ce aikin kudin ki ne ya 6oye ni, na ce
Allahu! Har ina cewa ka gudu. Ya yi dry, na gudu da
kudin ki ki ke zato Na ce eh, nima ina dry. Ya ce kai kina
da bn dry, to ga kudinki,amma muje gidan ku na bawa
iyayenki kada wani ya bi ki ya kwace. Cikin murna na ce
to daga nan ma in sun gan ka sun fi yarda. Na kama
hanya a kafa ya ce ga mota can zo muje, in kin san
hanya direbn mu sai ya kai mu, ba tare da wata shakka
ba na ce to. Sam na manta da su Sa'a, sai da zamu
shiga motar naji muryarsu,suna cewa ke Hafsatu ki ka
sani ko dan yankan kai ne? Na dube shi, shima ya ji
amma sai yayi tamkar bai ji ba, na ce ba wani dan
yankan kai na shiga motar da dan tirena, shima ya shiga
ya ce kawarki fa,shawara suka baki nace tame? Yace
kin san ni ko dan yankan kai ne? Duk da gabana ya fadi
amma sai na dake nace, bakayi kama dasu ba yace suna
da kama ne? Nace oho amma kai bashi bane yace, dama
sunanki hafsatu? Nace eh abakin su sa‘a kaji ko da suka
kirani dazu ko? Yace eh nace yan bakin ciki ne, dan fa
nace masu kana buga kudi sai suka ce mun karya ne, kai
malamin makaran tane. Yace gaske ne ni malamin
makaranta ne, amma daga yau na gama nace, duk da
kudin da kuke bugawa basu ishe ka ba sai kayi koyarwa?
Yayi dariya yace bautar kasa aka turoni daga jahar mu.
Nace bautar kasa kuma? Yace kema watarana zakiyi in
dai kikayi karatun da kike fadi, gwamnati zakiyi wa aiki
na wata tara ko shekara.
Ban gane nufinshi ba amma nace Allah yasa naga
lokacin.
Da gudu na shiga cikin gidan mu ina cewa inna fito kiga
mai buga kudi ya bugo min inna ta saka hijab ta fito tana
cewa ni ban gane wanan shirmen naki ba, ina mai buga
kudin? Wannan yarinya da wautar tsiya kike inna tayi
turus lokacin da tayi arba da rantsatsiyar motar tace
hafsatu aina kika jajibo wadan nan...? Cak! Maganar ta
tsaya lokacin da saurayin ya bude motar ya fito
kyawunshi yasa inna tunain ko aljani na janyo, ta soma
karanta (ayatul kursiyu) zata juya gida na rike mata
hannu. Inna dan Allah ki tsaya mana zo muje gurin su
tace a a hafsatu muje ciki bana tsamanin wadannan
bil‘adama ne nifa nasan banda aljan ke ina kika isa kiga
mai buga kudi, sai dai in jabun kudi. Saurayin yatako har
gaban inna ya dan rusuna ya gaishe ta, ta amsa tana
dan dari dari, nace to wanan ce inna ta sai ka bata
kudina inna tayi ta maza tace samari daga ina? Ni fa ban
fahimci surkulen da yarinyar nan take yi min ba? Yayi
mur mushi ya dube ni jeki kawo min ruwa nasha, da gudu
nayi ciki ban saurari inna ba da takecewa in dibi na baba
yafi sanyi
ina tafiya ya dubi inna yace mama zolayarta nake yi, ni
dan bautar kasa ne an turo ni daga Adamawa state, ina
koyarwa a makaranantar da take zuwa talla. Yawan
wasanta ke burgeni har na shiga sabagarta, sai kuma na
fiskanci cewa tana son karatu amma rashin hali ya hana
hakan. Dan ta fada mun tana talla ne dan kawai ta tara
kudin makaranta. To ni nazo ne in ba damuwa zan
taimaka mata don ni daga yau in sha Allahu na bar
kaduna kenan, don na gama abin da ya kawo ni, dai dai
nan na taho da ruwa na ce masa gashi. Inna tace mika
mashi yace a a dama basha zanyi ba bakiga na sha ruwa
a mota ba? Nace eh yace to maida. Yaci gaba da cewa
dama nawa ne kudin nata? Tace ni ban tambayi nata ba
amma lokacin na wanta inaga dubu uku muka kashe? Ina
ga ba zai wuce hakan ba. Ya ciro yan daurin nera goma
gama guda uku sababbi fil ya mika mata ga wanan
mama dan Allah ku biya mata kudin makaranta, ku cika
burinta har tazama abin alfahari nan gaba. Allah ne kadai
ya san al‘ummar da zasu anfaneta. Innarmu jiki yana bari
ta amshi kudi tana ta zubo mashi godiya ma, sai daka
tsale nake tamkar yarinya karama, ina cewa shi kenan na
huta talla. Innarmu ta harareni tana cewa to kiyi mashi
godiya mana, nace na gode yayi murmushi ya tafi yana
daga mun hannu nima haka. Sai dai kash nayi mantuwa
ban tambayi sunan shi ba, a lokacin ban damu in san
sunan shi ba muka nufi cikin gida da murna innarmu bata
da rufi, don haka a tsakar gida ta fada musu cewa wani
bawan Allah ya taimaka min da kudin makaranta. Wasu
suka taya mu murna ciki harda babarmu, wasu kuwa sun
nuna bakin cikinsu a fili don Ade ina bayi naji tana cewa,
maman abba yau kinji matar nan mu zata rainamawa
hankali ta dai tura yarinyar ta maula. Maman abba tace
ai shegen son kudi irin na maman hafsatu ya isa, ace
mata sai rashin godiya Allah duk fa kokarin mujinta ta
raina. Daga can asabe ta sako baki shi wannan mujin
nata ai tuni ta gama dashi katsinawa kuma da shegen
asiri? Dubi fa fada irin na mutumin nan sai da tasha
karfin shi ga kishiya kuma sai yan da akayi da ita Ade ta
ce, ayi dai mu gani, kina nan yarinyar zata janyo mata
abin kunya, Maman Abba ta ce ta dage sai yarinya tayi
boko, za su ga boko ai. Na fito cikin takaici ina kallon su,
sai nan da nan suka canza mgn. Asabe ce suna ta zagin
ki,wai kina asiri ke Bakatsina,wai zan ja miki abin kunya.
Inna tana da fada, balle in an ta6o ta, ta fita da sauri
Yayana Umar ya hau ni da fada,wai don ubana ni
mahaukaciya ce da zan fada mata, na ce ka ji gulmar da
suke yi ne? Hayaniyarsu ce ta fito da mu, Umar ya je
yana cewa, Inna ta bari ta dawo daki, nan dai haka gidan
kan rikice wani lkcn. Musamman in ana fada kan yara, ko
gulma. Innarmu tana da fada kowa a gidan yana shakkar
ta6o ta. Bayan komai ya lafa, muna daki ta ce "Hafsatu
kin dai ji da kunanki, ina so ki baiwa mara da kunya, ki
kare min mutuncinki, kiyi karatunki ki zama abn sha'awa
da kwatance na ce to Inna. Cikin kwazo na soma
karatuna, kudin dan gayu mai buha kudi ya bugo min sun
taimaka min kwarai. Inna tayi musu kyakykyawan
adani,sun ishe ni har zuwa lkcn da na gama JS 3, lkcn
shekaruna 14 girma ya soma zuwa min 'yan alamu sun
bayyana. Na kan ji mutane suna cewa, wai ban cika kyau
a fuska ba, sai dai jiki. Yawan fadin ina da diri shi ne ya
sani jin cewa ni mace ce musamman in nayi kwalliya.
Wata safiyar Jumma' naje fitsari sai naga jini, cikin
fargaba nazo har da hawaye nake fada wa Inna. Ta ce,
Hafsatu girma ne ya kama ki yau nawa ga watan bature?
Na ce 7. Ta ce to duk 7 ga wata za ki ga wannan jinin.
Ta iya yiwuwa yazo kafin 7, ko bayan 7, amma duk wata
dai za ki gan shi. In kuma ba ki gan shi ba hakan na
nufin kina da ciki. "Na zaro ido ta ce ai ba a samun ciki
haka sai in kin kasance me wasan banza da MazaNa
sauke ajiyan zuciya,don nasan bana yi. Na ce ni dama
ba ruwana da maza, ta ce na sani, amma ki kara.sannan
ki kara sa tsoron Allahn ki cikin zcyrki. Daga yau din nan
an bude miki fayil dinki, duk aikin alkairi ki ko akasin
haka za a rubuta miki, don haka sai ki kula, ki kuma san
me ki ke ciki. Tun daga wannan lkcn nasa ma raina
tsoron maza, nake kuma duba duk wani aiki da zan yi
zunubi zai ja min ko lada.
Marubuciyar tace'Yan uwa mata zan dan mana wani tuni
nan gurin, mu nutsur da 'ya'yanmu muyi musu bayani
mai kyau tare da nutsa tsoron Allah cikn zukatansu, lkcn
da suka samy kan su a irin wannan yanayin na
balaga.....Allah yayimana jagora
Ba zan manta da Jumma'ar ba, misalin 4 da mintina na
yamma gari yayi sanyi La'asar, nayi kwalliyata da riga
da wandon pakistan da Inna ta sai min a gurin wata
mai gwanjo. Kore ne kalar lemun tsami da gyalanshi,
Sakina kanwata yarinyar Baba kishiyar Innarmu ta ce "
Yaya Hafsatu zan biki." Na ce, zo muje gidan kanwar
Innarmu zan je Hayin Malam Bello na kai mata kudin
dashin sabulu da suke yi. Ko can gidan matan gidan
suna ta yaba yanda kayan suka yi min kyau.Dai-dai kan
layin Biliya wasu matasan samari suna tsaye jikin
mashin, kallo daya na musu na dauke kaina ban kuma
kawo komai a raina game da su ba. Sai naji takun
tafiya, ana cewa 'yanmata ji mana,maza sun sha yi min
haka bana tsayawa, don Innarmu ta fada min karatu
basa haduwa da soyayya, kada na sake na kula kowa.
Ya zagayo ta gabana Beby saurare ni mana. Na' kalli
fuskarshi,sai zcyta ta buga, ina son mu2m mai kyau,
daga ganin shi dan gidan 'yan gayu ne. Na harde
hannuwana a kirjina, ya sake dubana daga sama kuwa
gsa kasa, "Wow! Ya sunanki?" na ce "Hafsatu." Ya ce
"Nice name, Hafsy ina ne gidanku?" Kawai sai na samu
kaina da yi masa kwantance, can kasa muke Abuja
Road, layi na shida marar kwalta, kana zuwa layin ka
ce ina ne gidan yawa za a nuna maka. Ya dan yi shiru
don ya fahamice a geto take amma sai yace zan zo
anjima ko gobe zan samu ganinki? Nace eh yace to sai
kin ganni na tafi ina wai wayanshi sakina tace yaya
hafsat mijinki ne? Cikin yar dariya nace eh mijinane
wasa ne ya ruda ni na kasa sukuni, tare da boyiwa
innarmu don kada ta hanani fita, sai dai har tara banji
ance ana kiran hafsa ba,har fita nayi gurin bakin titi ina
tunanin wai ko yazo bai gane layin ba na dawo daf da
zan shiga gida na ganshi tsaye kofar gidan mu. Wani
sanyi naji acikin zuciyata, sai na soma tunanin zan jene
na ce mashi gani ko ko ce mashi zanyi ni kake nema?
Sai na yanke shawarar na bi ta gabanshi, har na daga
labulen buhun da yake kofar gidadanmu zan shiga, sai
naji yace hafsy sai na tsaya tare da sauke a jiyar
zuciya, sannan na wai wayo na tako cikin irin tafiyar da
ban taba sanin na iyata ba. Duk da yake dare ne a kwai
kwan lantarki a kofar gidan, yace nafi minti 5 ina jiranki
nace ina yini? Yace lfy da farko dai sunana munnir jafar
dalibi ne a (A B U) zariya ina shekara ta 2. Sanan
muna zaune ne a nan makarfi road son munnir ya kara
shiga ta, don a rayuwa ta inaso in auri miji dan boko
nace ni kuma na gama js3, yace me ya hanaki cigaba?
yanayin garin ne. Haka muka ta fira sam bansan dare
yayi ba har 10 ta gota ba sai da naji karan raidiyon
baban mu ya nufo gida. Ya tsaya tare da cewa wacece
nan? Ke hafsatu me kikeyi haryanzu? Na dubi munir
nace ga baba na. Ya cire hular kansa hana sallah yace
ina yini baba? Ya dubeshi lfy lau zo ki shige muje, nace
to sai anjuma yace zan zo gobe nace to. Tun kafin
mushiga daki baba yake min fada tare da tambayata
wanene wannan yaron ya dame kugu? Nace dazum ne
muka hadu dashi. Hayaniyar shi ne ta tashi inna daga
dan baccin da ta soma, tana tam bayarshi lfy malam
kake fada da tsohon daran? Yace amma dai ke
sakaryar uwace, 10 ta wuce yarinyarki tana can tana
zance da wani kato ke kuma kin hamgame baki kina
bacci Inna tace hafstu na can tayi baci tuni dakin
babarsu, ba ita kagani ba ita da bata fita zance ma
yace to ga tanan ma bare ki karyata ni. Inna tace hafsa
zance kika fita? Ya mukayi da ke? Baba yace ni dai
tashi ya turo mun iyayensa dama ni burina in aurar da
ita. Inma shi bayi zaiyi ba akwai mutane da dama sun
min magana. Inna tace je ki kwanta itama ta maida kai
ta kwanta alamun zancen baba bai shigeta ba. Da safe
ta tsareni da son jin wajen wa na fita? Nace inna wlh
jiya ne fa da kika aikeni ya ganni shine yazo. Tace
amma nace maki ki fita hanyar samari ko? Kin san
babanki matsawar zaki rinka tsayawa zance kina son
karatun nan zaki barshi ko nace inna naga shi wannan
yana son karatun, don su gidansu yan boko ne. Maman
shi da baban shi duka aikin gwamnati sukeyi yace min
jami‘a yake yi (A B U) zariya tace to ni dai banaso
kurinka tsayawa nace yama ce zai bani kudi nacigaba
da karatu na. Inna tace to indai ko haka ne sai dai
kitafi makarantar kwana, saboda kin san babanku sarai.
Koda munnir yazo washegari, haka na zauna na fada
mashi komai dangane da ma haifina game da kin boko.
Yace taf kice cutarki zaiyi? Tun kina karama zai
kasheki da aure ai gaskiyar innarki ne kada ki yarda.
Nace kudine matsalar mu sai dai in shiga ta kwana
yace haka ne, yace zan baki kudi bari dad dinmu zai
bani kudi in yadawo tafiya. Nayi ta masa godiya yace a
a shidai abinda zanyi mishi kada in saurari kowa kuma
na saki jikina dashi, nace kada yaji komai cikin sati 1
na gama yarda munir na sona, nima kara sonsa nake
duk zuwa yakan zo min da wani abu, turare ko dan
zobe ko dan wani abun kwalama. Bana manta ranar
lahadin da yazo min sallama zai koma makaranta ya
kuma bani kudi naira dubu 20 har kuka nayi mashi dan
bana so rabuwa dashi. Ranar shida abokin sa sukazo
wai shi faisal, kawai sai naji munnir ya rumgume ni,
wani abu naji tun daga tafin kafata har tsakiyar
kaina,shiko sai cewa yake inyi shuru in daina kuka
hannun shi kuma na zaga sassan jiki na, fadan inna ya
fado min cikin rai inda take cewa. In kula da kaina
wasan banza da namiji zai iya sawa in sami ciki, nayi
sauri na janye jiki na daga gareshi, yasa hannu yana
share min hawaye muka yi ban kwana na shiga gida.
Suna tafiya faisal yace munir dagaske kana son
yarinyar an? Munir yace da dai nazo na dan kwashi rabo
nane, sai kuma na gane yariyar ba yar hannu bace.
Sannan kuma nasamu kaina da sonta na gaske faisal
yace ka dai san dadinka ba zai barka ka auri yar geto
ba ko? Yace kai nif zan zaba da kaina ba zan yarda ace
min naje ga yar wani ba. Nikam ina shiga gida muka
soma murna da inna, nan muka shiga tsara yanda
zamuyi wa baba bayanin munir. Washegari inajin inna
tana cewa baba wai kananta da yayansu sunce ta kaini
zasu nemmar min makarantar kwana. Baba yace a a
shifa bai yarda ba, tace yayi hakuri kwana nawane zan
gama? Baba yace nifa ba kin karatun nake ba, nafiso
tayishi a can dakinta inaso kisani har in yarinya ta
soma tsayawa da saurayi mafi kyawu shine ayi mata
aure. Inna tace za ayimata malam, wannan yaro da ka
ganta dashi shene yake son auranta na lura itama tana
sonshi yace to ba sai ya turo magabatan shi ba muyi
zancen manya! Inna tace yo shima ai karatun yake sai
ya gama itama ta gama kafin nan. Shuru yayi bai sake
tankawa ba shurun ba yana nufin ya yarda bane,
shurunsa yana nufin mukarata can shi ba ruwansa.
Kwana 2 tsakani muka shirya ni da inna muka nufi
manunfashi kananta kawu sha‘iabu da kawu bashir
harda wanta kawu kabiru sun sunji dadi sun kuma tsaya
har saida nasamu shiga ss1. Haka baba ya hakura ya
zuba muna ido, na cigaba da karatu cikin nasara da
kwazo, yan gidanmu kam da makota sai gulma da
tsegumi, ba mu damu ba. Fatan inna shine inzama abin
kwatance nan gaba.
A duk lokacin da nazo hutu munnir nazuwa, haka duk
lokacin ziyarar dalibai in yana da sarari yakan zo.
Hidimar karatuna shi yake yinta haka nan duk wani
kaya na yan mata shi ne yake siyan min, wanan shine
yasa na kara sake wa dashi. Matsalata dashi son taba
jiki na, kawai lokacin da wani hawaye yayi min wai in
bishi muje dakin wani abokin shi, niko nace a a muji
tsoron Allah ba don son da nake yiwa munnir ba a tuni
na hakura dashi. Cikin haka na gama karatuna na
secondary. Na dubi likitar idanuna suna zubar da
hawaye nace, anty ko lokacin da na gama karatu na
baba ko gai suwa nayi baya amsawa, kannena yaran
kishiyar mama na guda 2 ya musu aure. Sannan
karatuna kafin na tahoshi sai da ta kai yace in har wani
abu ya biyo baya abakin auran innata, sannan in nemi
uba..... Kuka ya kwace min mai karfi, ina fadin na shiga
ukuna zan kashe auran iyaye da kaina. Munir ya cuceni
fyade yayi min anty ki taimaka ki cere cikin nan. Yan
gidanmu da yan unguwarmu duk dariya zasuyi mana.
Kalo kawai likitar keyi cikin tausayi har nayi kukana mai
isata na gama ba wanda ya bani hakuri. Daga ita har
asabe tace to, ke hafsat ki koma makaranta gobe kizo,
keko asabe ki kwana nan nace anty don Allah nima zan
kwana nan din, ko naje makarantar ba zan iya komai
ba, tace shikenan. Ta mike sannan ta nuna mana wani
daki, ku shiga nan kuyi sallah da komai a ciki. Ba tare
da ta jira amsa ba ta nufi dakin ta, kaiwa da kawowa
kurum take yi. Ta ina zata bullowa wayanan yara? Sam
bazata cire cikin ba, bazata kuma bari suje su cire su
zubar ba. Ta lura Asabe tafi saukin kai don haka da ita
zata fara. Yanda naga rana haka na ga dare, alwaula
kawai nayi na yi nafila. Daga bisani na koma istigifari,
washegari bayan ta lalabemu mun karya, sai ta bamu
wasu magun guna tace kada in damu in koma
makaranta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login