Showing 30001 words to 32103 words out of 32103 words
Chapter 11 - Sanadin Boko Book 1 Complete Document by Halima I Mashi .txt
yake ko burgeshi take. Ya dai san ko ma
dai menene ya damu da ita. Kafin kwana 3 ya damu da
son sanin wacece ita? Alwashi ya sha ma kansa ba zai
bar kano ba har sai yasamu cikaken labarinta, wanda
yasan gurin rahama ne kadai zai san haka, haka a rana
ta 4 ya kira sagir yace gashi nan zuwa, zaya ci dinner
tare dasu. Duk da tulin kayan da aka tara a gaban shi na
lashe-lashe da tande-tande, sam basu dameshi ba, ya
dubi sagir cikin hausarshi na fulanin yola ya ce, nikam ka
bani dama inyiwa amaryarka wasu tanbayoyi game da
kawarta nan sagir yace wace ba dai hafsatba? Bai san
da lilin fadiwar gaban da yaji ba, haka nan bai san
lokacin da kalma ta fito daga bakinshi ba, tana da miji
ko? Ya tsare sagir da idanun shi masu kama da na
mata.Sagir ya ce bata da miji, amma fandarrarun
halayenta ne zasu gundire ka, yace bana zaton haka,
yanzu dai nafi so ka min izinin zantawa da matarka,
yace to ya kirata tazo ta zauna tare da cewa ba dai har
ka gama cin abincin ba?Yace ai kafin abincin ya samu
shiga nikam sai naji batun kawarkinnan hafsa. Rahama
ta dubeshi da sauri tace me kake son sani game da ita?
Yace unguwarsu da kuma dan lbr ta haka rahama tace
unguwarmu daya, sannan ita daliba ce a Poly yanzu haka
tana HND dinta ne. Iyayanta fa mutanen kirki ne?
Rahama ta danyi din sanan tace eh yace ta taba aure
ne? Kuma shadad dan tane? Nan take zufa ta karyo
mata, amma bata da amsar da ta wuce eh ya jijiga kai,
dama nayi zaton danta ne duk da batayi kama dashi ba
sun rabu da mijinta ne ko ya rasu ne? Nanma tace eh,
yace Allah sarki inaga shiyasa bata son hulda da maza,
dama ance mace in mujinta ya rasu kafin ta manta da
wuya. Iyayan ta din sunan layinku? Rahama tace eh, a a
karatu tazo suna kaduna. Gurin aikinmu daya ne super
market ne, yace to zan iya samun number dinta?
Rahama tace wai gaskiya yallabai sai dai kayi hakuri, in
na baka number ta zai iya zama sanadin rabuwar mu
kwata-kwata. Ya dan yi shuru yana nazari, Rahama tace
duk yanda kake tunanin hafsat ta wuce nan. Yace amma
ina zaton bakinki naji yana fadin tana da saukin kai da
dadin zama, kuma bata da fada? Rahma tace gurinmu
mata ba, amma game da maza sam bata da sauki, ta
tsani namiji ta kijinin ace anason ta sanan bata son
taimako daga namiji, ko wannen abu 3nnan ba taso.
Yace to me tafi so? Rahama tace abinda tafi so shine
kada kashiga harkarta, in kuma kashiga kayi tsananin
dace ta kula ka to kada ka tam bayeta ko wace irin
tanbaya, sannan kada kace kana sonta, ban san me
zakayi ba ta saki jiki da kai ba, don naga maza da yawa
wanda suka sota amma dole suka hakura rashin sakin
fuskarta yasa maza suna tsoranta. Da zaka hakura da ya
fi maka lada don ko taji hau shin abinda MC yace mata a
gurin bikinmu inda yace ku miji da mata ne. Abubakar
yace niko sai naso ace gaske naji dadi maganarsa.
Rahama ba zan iya hakura da hafsat ba don ina jin wani
abu game da ita wanda ban taba jinshi a wata yarinya ba
ina zaton shine so. Su Rahma suka sa dariya sagir ya
nisa yace lalle sonka din nan ya iya jan rigima ya fada
inda zaku sha wahala Abubakar yace sona yayi daidai
don yasan bama ra‘ayin mata marasa aji wadanda ke bin
maza da kansu suce suna so zanje in gwada sa‘a ta
kafin na bar kano zanga yada zamuyi. Sukace Allah ya
taimaka yace kasan ban sami daurin aure ba so bansan
gidansu rahama ba bare insan nasu hafsa din. Yace bari
inje in nuna maka daga nesa suka fita suna dariya ba
tare da yace komai ba shi tuni ya manta da menene a
gabanshi ko da sagir ya nuna mashi sai yace ba yanzu
zanje ba sai gobe da safe.
Ni kam tuna ranar da muka dawo daga bikin rahama
kulin shadad bashi da magana sai ta uncle dinshi tun ina
jin haushin shi ina mai fada har na dawo lallashinsa,
saboda har lokacin yana fama da zazzabi nakan
lallabashi da cewa kayi hakuri zai zo ya daukeka
ranar cikin dare har da cewa to anty kirashi a waya nace
to ka bari sai da safe yanzu yayi bacci, cikin kwana ukun
nan da kyar na samu ya manta da maganar uncle sai
jifa-jifa. Da safe yana sanye da kayan makaranta ni kuma
nayi shirin gurin aiki. Yau bani da lecture da safe don
haka gurin aiki zanje dama ka‘idar da manaja ya bani
kenan dan a daidaitanmu yana jira, shadad ya fita da
gudu ni kuma na kule dakin na fita. Ina rufe gida naji
muryar shadad yana cewa anty ga unclena anty na wai
wayo baya na datse kwado, ilai kuwa yana tsaye jikin
wata yar kyakyawar motar blue kiran kanfanin (toyota)
sanye da t-shirt da wando jeans baki, riga baka da ratsin
ja. Ta kalmin kafarshi baki ne sauciki. Na dauke fuskata
daga kalonshi bacin nayi fuskar shanu shadad wanda
tuni ya daneshi, murna yake yana cewa unclue kazone?
Da ma anty tace indaina kuka zakazo, takaici ya kamani.
Shi kuma sai ya dubeni anty antashi lfy? Ba tare da na
kaleshi ba nace kalau na daga labuln dan a daidaita na
shige. Sai naji yana cema dan a dai daitan, ungo nan
malam kaje sai bayan kwana 2 ka dawo tun da nazo ni
zan rinka kaisu kafin in tafi. Ya mika mushi yan dubu
dubu sababi fil guda 3 ya amsa yana cewa na gode
yalabai to sai zuwa yau she zan dawo yace nan da
kwana hudu haka nace sannu da karfin hali menene
gamina da kai? Da har zakaso ka min iko? Bai ce kala ba
ya juya. Na cema dan a daidaita sahu muje na leka
nacewa shadad zo mutafi ko nayi tafiyata. Mutumin ya
kaleni shima fuska a kame ki fito muje ban san sanda
nace to ubana! Sai kazo ka jani ya kara matsowa saitin
dan a daidaita yace ka sauketa katafi abinka. Sai kawai
mai a daidaita yace kiyi hakuri yar uwata, ki sauka ban
tankashi ba bankuma sauka ba,gani nayi zamuyi latti
nace yanxu kai malam haka zamuyi da kai? Duk tsawon
lokacin da muka dauka yau kace bazaka kaini ba? Yace
to Alhaji ne yace ki sauka ai, kuma ni bansan
dangantakarku ba kada in shiga hurumin da banawa ba.
Nace to bawata dan gantaka a tsakanin mu, asalima ni
ban sanshi ba da muna da alaka da baka gan shi ba ko
sau daya? Yace ki sauka mana nasan duk yanda akayi
kunsan juna. Ganin zai bata min lokaci sai na sauka na
dauki jakata nace shadad ya wuce muje, a mota yasaka
shi amma ya tada mota sukayi gaba. Na tare mai mashi
muna ciniki yazo yace mai mashi tafi abinka, in ka
dauketa zaka gamu da hukunci... kafin ya rufe baki yaja
mashin ya kara gaba. Na kaleshi nace me kake nufi
dani? Yace gurin aiki zan kaiki kawai,nace banaso dan
Allah kai mayene? Yace a'a ni ba maye bane, to bin me
kake min? Nifa ba yar iska bace. Yace nasani ai, to dan
Allah kafita hanyata, in kanawa darajar mahaifinka. Yace
don girman Allah ki shiga motar nan mu tafi, kada
shadad yayi latti, sannan inaso ki bani lokaci nazo mu
dan tautauna, nace bani da lokacin da zan iya baka, ka
fita harkata please, nacigaba da tafiya. Ranar dai a kasa
na tafi gurin aiki, shikuma sukayi wani guri shida shadad,
nasan sai dai suyi tambaya amma shadad ba zai iya
gane makarantar ba, ganin nakusa bansha wahalar hawa
abin hawa ba na karasa, takwas ta gota ina shiga ishak
yace yau bamakaranta kenan? Nace eh, gashi ma nayi
latti, musa yace manaja kuwa yazo yananan ya zagaya
ciki nasan sai yayi maki surutu, nace uhum sai dai yayi
tunda dai latti na riga nayi shi.Ina zama yana isowa, ban
ko kalleshi ba na jawo takarda dake kan teburina zan
fara duba abubuwan da suka fita da safen nan, sai ya
ce, "Kin san zaki zo da safe me yasa zakiyi latti?" Na ce,
"Abin hawa ne ban samu ba." Ya ce, "Amma ai ba'a
wahalar mai ko?" Na ce, "Kamar yaya?" Ya ce,
"Ballantana ki ce ana wuyar abin hawa." Na ce, "Akwai
abin hawa mana." Ya ce, "Baki da kudi ne?" A kagare na
ce, "Ina da shi." Ya ce, "Ok kin soma gajiya da aikin
kenan?" Na san shi sarai zai iya cewa ya koreni, kuma
dai Allah ya sani da aikin na dogara, don haka nace,
"Tunda ba halina bane lattin amin uzuri." Ishak yace ayi
mata hakuri Sir. Ya ce, "Kune kuka iya bada hakuri ita
bata iya ba ko? To ba zan mata uzuri ba, sai dai in
taimaka mata." Cikin sauri na ce, "Bana son taimakon
kowa sai na Allah, nace dai amin azuri." Ya ce, "To ki je
gida ki huta na sati 2 don ki koyi yadda zaki dinga zuwa
aiki." Muryarshi muka ji ya ce, "Uzuri za'a yi mata
manaja." Ya dubeni har na mike, "Koma ki zauna.
Manaja akwai uzuri a rayuwa, ko tana latti?" Ya ce, "A'a
ranka ya dade bata dai da mutuncine, in banda rainin
hankali tana fada min akwai abin hawa kuma tana da
kudi amma ta zo latti?" Ya ce, "Duk da haka ka mata
azuri da tace baka san dalilin ta ba, so tayi zamanta." Na
dube shi ina mamakin karfin halinsa, sai naga ya nufi
Ofishin manaja na ce kila ya san shi ne. Ni dai na zauna
na ci gaba da aikina. Ina jin Musa da Ishak suna mitar
rashin mutuncin shi.Abubakar ya dubi Manaja ya ce, "Ka
daina yiwa mutane haka, musamman na kasa da kai, a
rayuwa dole ne mutum ya dinga hakuri, yanzun kasan
uzurin da ya tare ta?" Manaja ya ce, "Yallabai yarinyar
nan bata da mutunci sam!" Ya ce, "Ko zan iya sanin
halayen ta marasa kyau?" Ya ce, "Na 1 bata da fara'a ga
kallon banza, kuma ta fi karfin kace zaka taimaka mata
sai ta hau bala'i, ina ce sakin fuska ma abu ne?" "Ni
kuma hakan ya birgeni." Abubakar ya katseshi, "Ban ga
laifinta ba, don ta kare mutuncin ta. Shi kenan sai ya
zama zubar da mutunci don bata saki fuska ba?" Manaja
ya yi 'yar dariya, "Yallabai yarinyar nan fa in ma sonta
kake ka hakura don ba zata baka hadin kai ba, in mata
kake so 'yan gayu isassu na debe kewa sai in kawo
maka su. A ina ka sauka?" Abubakar ya ce, "Na fada
maka ina son ta ne? Ko na fada maka ina son mata ne?
Inma matan nake so ai baka fini saninsu inda zan same
su ba, ina maka nasiha ne ka daina wulakanta na kasa
da kai, in dai suna yin abinda ya dace." Ya ce, "To zan
kula Yallabai -ya ci gaba da cewa- Ya hajiya? Ai mun yi
waya da ita jiya tace matake fada min kana Kano zaka
shigo ka duba abubuwan dake tafiya." Abubakar ya ce,
"Kwarai kuwa, bari in duba takardun. Fito min da su." Ya
jima sannan ya kammala ya fito, Manaja yana biye da
shi ya tsaya kusa da ni, "Ki yi hakuri kin ji ko?" Sannan
ya fita.Ni kam ban ko kallesu ba. Tunanina 1 ina ya kai
min yarona?
Lokacin tashina nayi na nufi Makarantar su Shadad na
dauke shi muka nufi gida. Tun akan hanya ya isheni da
labarin Uncle, Anty Uncle ya sai min ice-cream ya kai
min da muka yi break da su sweat, kuma ya tambayi
Auntynmu wai ina karatu? Ta ce mishi inayi sosai,
kuma ana lura dani wurin yin home work, yana ta jin
dadi. Na yi tsaki tare da cewa, "Yi min shiru." Da dare
ina Sallar Isha'i naji bugun gida, sai da na idar sannan
na nufi zauren nace wanene? Ba'ayi magana ba har
zan juya aka sake bugawa nace wanene wai? Yace
Abubakar ne. Na gane muryarshi amma sai nace, "Wa
kake nema?" Ya ce, "Shadad." Na yi shiru ina nazari,
hausawa sunce mai Da wawa, inna bar wannan
mutumin zaya fake da dana ya cutar da ni, gara in
masa rashin mutunci ko ya fita daga harkata. Na bude
kofar sannan na dogare bakin kofar, "Kai Malam! Ka
fita idona, ina ganin kimarka bana son ta kaimu ga
rabuwa fata-fata ni da kai, ina nufin in zabga maks
rashin mutunci, ka ja tsumman rayuwarka ka yi gaba,
ka fita harkar yarona, anzo za'a fake da yaro a cuceni."
Na ja tsaki tare da maida kofar garam na barshi tsaye
da leda shake da kaya.
Daga ranar ban kuma ganinshi ba, hakan ya min dadi
don haka na godewa Allah. Sai dai damuna da Shadad
keyi na kiran Uncle har da kuka. Kwana 8 bayan haka
ina ta kici-kicin girkin rana, yau lahadi sai da yamma
zan fita aiki. Tuwon shinkafa miyar alayyahu nake son
mana na gama kwashe tuwon cikin leda na zuba a kula
na samu Shadad yana home-work na ce, "Yauwa ka
zauna zanje kasuwa in dawo." Daman nakan barshi. Ya
ce, "To Anty." Ya tashi ya dauko kujerar da yake
takawa yasa sakata ta ciki.
Na nufi kasuwar don ba nisa sosai. Ban fi minti 30 ba
na dawo, sai dai me? Kofar gidan a bude, haka na nufin
Shadad ya cire sakata, a hanzarce na shiga. Takardun
shi suna gurin, takalminshi suna gurin. Kaf babu inda
ban dyba ba cikin gidan amma ban ganshi ba, da
hanzari na nufi makota duk da na san baya zuwa,,,,,
Me ke shirin faruwa da nine?
End of 1
Mukhtar Ismail Muhammad
WhatsApp: 08161892123
www.arewarulers.com.ng