Showing 21001 words to 24000 words out of 32103 words

Chapter 8 - Sanadin Boko Book 1 Complete Document by Halima I Mashi .txt

muje amin gwaji nayi fitsari na kawo. Nan take
sakamako ya fito baro baro ina da ciki nurse bata fada
muna ba, ta dai bamu sakamakon mu kaiwa likita.
Lokacin zuciyata ta gama bushewa, na mekawa Allah
komai. Mun shiga yana rubuta muna wani magani, sai da
ya gama sanan ya duba. Ya kali baba, tana da miji? Baba
yace a a likita yasake kalona, amma ke kinsan kina da
ciki? Wata muguwar faduwar gaba naji, tamkar yau
nasoma jin cewa inada cikin. Baba yace tanada ciki ko?
Yacigaba da rubuta wata ta karda yana cigaba da cewa
tana dauke da ciki. Abinda sakamako ya nuna kenan.
Amma kuje ayimata (scan) don kusan ko wata nawa ne
inna kawai na kallah wada ta kafa min idanu sun kada
sunyi jajajir,Baba ya ce a"a bama bukatar sai tayi
hoto,dama tabbacin cewa akwai cikin muke son sani,
tunda akwai shi kenan. Ya kalli Innarmu,bana bukatar sai
na sake tuna miki komai daga ke har ita. Ya fita abinshi.
Inna cikin kuka ta ce, Hafsa haka zaki min? Hafsa na
dace da wannan sakamakon? kin min adalci kenan? cikin
kuka nima na ce kiyi hakuri Inna, wlh fyade Munnir ya
min. Ta ce, karya ne, ki min shiru. Ta dubi Likitan da ya
zuba musu ido,don Allah Likita ka taimake ni ka cire
mata cikin nan. Da saurin Likitan ya mike tsaye cikin
murya mai karfi, fita anan domin nan ba asibitin zubar da
ciki ba ne. Muka fito muka nufo gida, Inna na fadin
Hafsa kin cuce ni kin kuma cuci kanki. kafin mu isa gida
tuni Baba yaje yayi fadan shi a tsakar gida kamar yanda
ya saba, muna isowa kowa sai kallonmu yake yi. Muna
shiga yazo ya ce ya va mu zuwa da safe mu fice,
yanzun ma don dare ne. Mutane na ta bashi hakuri,amma
ya ce to wane hakuri zai yi? Dan ya ce mata in haka ta
faru a bakin aurenta, kuma ta yarda. Ranar inna kasa
fadan nata tayi, duk da matan gidan da suka cika a kofar
dakinmu. Ni kaina kasa min fada tayi sai kuka da take
shara6awa. Mun kule can daki, can cikin sulusun dare
na tashi dan bacci taya dauki Inna na fice. Bayan na
kwashe duk wani abuna mai mahimmanci,
Baban titi na mika ina tafiya ba tare da tsoro ba. Daf! da
Asubahi naji wata mota suna cewa kano ne? na tsaida su
na shiga duk da cewa ba ni da ko sisi,saboda ragowar
kudina na mikawa Inna tun zuwa na, wato kudin wayata.
Sai da muka dau hanya suka ce dari biyar zan ba da, bn
yi mng ba, don haka sai suka zata na yarda ne. bakwai
da 'yan mintuna muka isa Gyadi-Gyadi, suka ce kudina,
na ce bani da kudi,don Allah su taimaka min. Nan
kwandastan ya hau ni da zagi, ni dai kallon shi nake yi.
Direbn ya ce, in je amma nan gaba in banda kudi in dinga
magana tun kafin na hau mota, don ba kowa zai iya
kyale ni ba. Na ce na gode.Sai lokacn kuma na soma
tunanin ina zan je? Wata zuciyar ta ce bakina karanta
littattafan su Anty Fauziya D. Sulaiman da su Anty
Sadiya ba? Ai suna fadin cewa in yara sun gudu su kan
je wani gidan a rike su a taimake su. To suma ai sa rike
ki in kin je ki zauna da sy za su fahimce matsalarki don
suna rubutu kan haka. Amma sai wata zuciyar tace, ki je
gurin Likita nan, ban san lkcn da na tsaida dan mashin
ba, na masa kwantace muka tafi. Ta fito kenan zata ofis
sai gani, ta ce a'a Hafsa ce .da safen nan? Na ce eh,
Anty ga shi ma bani da kudin da zan ba mai mashin din.
Ta zuge jakarta tana cewa, nawa ne? na ce,daga Gyadi-
Gyadu ne ba muyi ciniki ba, ta bashi dari biyu,naga dai
ya bata canji, amma bn san ko nawa ba ne, ta ce daga
ganin ki ba wata nasara amma shiga ciki. Sai da ta huta
bayan ta dawo sannan na fada mata komai, tace to ke
yanzun menene burinki? Na ce ni da zan samu wani dan
aiki in dauki nauyin kaina ba tare da na sake neman
taimakon kowane da naminji ba, zan so haka,amma da
wuya tunda takardun sakandire kawai gare ni, ta ce
amma bn san hikimar guje ma iyayenki da ki ka yi ba,
musamman mahaifiyarki wadda ta gwada miki kauna. Da
kin bita kun gudu tare ko kwa tsira tare. Na ce Aunty ina
tsananin jin kunyar mahaifiyata. Ba zan iya zama da ita
ba. A halin yanzun itama nasan ta dauki hanyar gidansu,
da wane ido zan kalle su? Ta ce to yanzu ina son ki
zauna nan mu ga yanda za"ayi. Ni da Asabe mun zama
'yan gidan Doctor Hindu, ita ke mana awo da komai,
magunguna duk ita ke ba mu. Cikin haka hr muka shiga
watan Haihuwarmu ko na ce haihuwar Asabe. Ta kawo
min kaya jarirai yayin da Asabe aka kawo mata daga
gidan su Yasir. Doctor ta ce, Kin gani kin hana mu dauki
mataki da kema yanzun dole su ringa yi miki komai. Na
ce, Bar su kawai Anty, Ni yanzun ba n da burin da ya
wuce in haihu lafiya, ina so in tsaya da kafafuna ko Allah
zai taimake ni in dawo da iyayena farin cikin su. Ina tuna
kannena, musamman Ummi, Nasan Baba kishiyar
Innarmu bata da mugunta, zata rike su amma nasan ba
za su yafe min ba, Matsawar suka ji cewa ni ce na
kashe auren uwarsu da ubansu. Doctor ta ce kada ki
damu, Insha Allahu za ki dawo musu da komai. Asabe ta
haihu'ya mace, kyakykyawa. Duk da 'yan gidan su Yasir
da shi kan shi ba su zo ba, amma sun aiko da komai
hatta ragon suna. Sannan suka ce ta sa ma 'yarta sunan
da take so. Doctor ce ta bada shawar a saka sunan
mahaifiya Yasir wato Maryam.A cewar Likitar, zai fi
girmama yarinyar duk lkcn data koma gare su. ...
A ganina matsalar Asabe mai sauki ce, don mahaifiyarta
har duba ta tazo sa6anin ni da ban san halin da nike ciki
ba? suma ba su san in da nike ba, Mai aikin Doctor ita
ce ke mata wanka., Kwanci tashi ni ma(E .D. D) na ya
cika har ya gota, amma shiru ba batun nakuda bare
haihuwa, Ranar Litinin tana min gwaji ko na ce awo, ta
ce yaran nan naki fa yayi girma da yawa ga shi kin kasa
kwantar da hankalinki jininki kullum kara hawa ya ke yi. ,
Yanzun ya wuce ka'ida ina miki tsoron afkawa cikin
matsala, kin kasa daukan kaddara. Kuka ya kwace min
Anty zan so in mutu a gurin haihuwa nan, shi ne kawai
burin zcyta. Likitar ta ce dama mun saba fada, duk lkcn
d zan miki awo,mugaye fatan d ki ke yiwa knki kuwa da
kina da kambun baka da yanzun kin lalace., Na ce Allah
isa tsakanina da Munnir Ta ce " Ameen. Amma yanzun
na fi so ki kwantar d hnklnk kin ji? Na ce to. Wasa- wasa
gani na kara sati 3 ta ce in na kara kwana 3 za a yi min
akin. Talata Doctor ta tafi wani taro a brnin Tarayya,
ranar ce kuma na soma nakudar Haihuwa. Haka na kwna
na yini, mai aiki tana kula dani, bayan magriba ta shigo
fada ta hau mu da shi me yasa b muje asibiti ba? Ni kam
na galabaita matuka,gado aka turo aka dauke ni, zuwa
cikin asibiti, amma haka na sake kwana dole ayi min aiki.
dn hk Likitar tasa a min shiri a sani a dakin tiyata.Tare
da taimakon wani Likitan suka yi nasarar ciro min katon
yaro namiji. Hakika na matukar shan wahala, kusan
kwana 3 ban sami kaina ba., Sai a rana na 4, din ranar
har na tashi an jingina min filo. Likitar ta kawo min
yaron. kai na kauda domin a ganina shi ne silan raba ni
da iyayena. Ban ta6a ganin fushin Likitar ba a iya
zamana a gidanta sai yau. Ta ce, Dauke shi ki ciro nono
ki bashi . Na fashe da kuka Anty ban yi aure ba kada ki
sa in ba shi nonona su fadi, ba zan ba shi ba. Ya ya
za'ayi ya raba ni da iyayena, na ci gaba da kuka, ta ce
ke rike shi kafin in zabga miki mari. Shi ina ruwan shi?
Shi ya samar da kan shi ko samar da shi ku ka yi? Don
me za ki ga laifin shi ? Da ba ku aikata abin da ku ka
aikta ba da Allah bai samar da shi cikin mahaifarki ba,
ganin irin kukan da nike yi yasa ta koma lallashina,
bayan na dauke shi. Babansa ya juya masa bya, kada
kema ki zama kin juya masa, Kina nufin ba za ki rungumi
kaddara ba? da lallashi ta shawo kaina na ciro nono yana
sha ina kuka. Satina daya na gargije, muka koma gida.,
Ba a yanka ragon suna ba, sai dai na ce ma Anty duk
sunan da ya dace ta sa mishi ta ce a sa mishi
SHADDAD. sunan wai yana mata dadi. Har ta kara da
cewa da Allah ya nufe ta da aure ya bata da sunan da
zata sa masa kenan, don haka yaro ya ci suna Shaddad.
A hankali na rinka jin kaunar yaron tana shigata, sai dai
kullum kamanninshi da Munnir kara bayyana take, ban
ta6a ganin da mai tsanabin kama da ubansa ba irin haka.
Zuwa yanzun zcyt ta dake,watanmun 3, Wata rana Doctor
Hindu ta zo mana da lbr mai dadi, wai ta samu miji,
tsohon ministan ilimi na kasa. Muka yi ta murna, ita kam
har da Azumi 2 don nuna godiya ga Ubangiji. Sati 4 aka
sa bikinta, mu ne har Katsina gidansu. 'Yan uwanta da
take bamu lbr duk mun gansu,ita ce ta dinka mana
ankon dinner. Ranar daurin aure da dare aka yu dinner.
Sam na kasa sakewa,saboda kallon da maza ke min, duk
da yaron da ke kafadata. Ni kuwa yanzu duk namiji da
zai kalle ni ko da bisa rashin sani ne ai bn da makiyi
kamar su. Mun sha biki,sannan muka dawo,mun samu
gidan yasha gyara,an zuba komai sabo,shi yana zaune a
Abuja da Iyalansa, amma ita zata zauna a gidanta
saboda aiki. Ada na cika wasa da tsokana ga son raha,
amma yanzu na koma miskila,masifaffiya, mara
fara'a.Bugu da kari yanzu ba ni da tsoro, musamman
akan namiji. Kwanci tashi hr Asabe ta yaye 'yarta, kuma
tuni an kaita gidan su Yasir. Bayan hukuma ta shiga
batun don kare lafiyar yarinyar. Sannan ta samu miji a
can kauyensu, mun je har can bikinta garin da aka kaita
ya dan fi kauyensu zama birni. Ni kam kullum cikin yiwa
Likita naci nake, ta samar min aiki ko na gida ne, ta ce
an gudu ba a tsira ba, dubi abin da ya faru da Asabe
sanadin aikin gida. Cikin satin da muka yi wannan
maganar tazo min da lbrn cewa ta samo min aiki a wani
Super market, amma da nisa tsakaninsu da unguwarmu.


Mukhtar Ismail Muhammad
WhatsApp: 08161892123


Sanadin Boko 1-7
Posted by Mukhtar Ismail Muhammad
On
www.arewarulers.com.ng


Under: SANADIN BOKO
Cikin satin da muka yi wannan maganar tazo min da lbrn
cewa ta samo min aiki a wani Super market, amma da
nisa tsakaninsu da unguwarmu.Na ce ba komai zan iya,
ba d jimawa ba na yaye Shadad, na ci gaba da zuwa
aikina, a wata dubu goma ake biyana. Shawara ta bani,
wai in bude (account) tunda bn rasa komau ba, hatta
sutura tana bani nata. Dan Adaidaita ta samo min duk
wata sai dai in biya shi, sauran na kai banki, Nayi-nayi ta
dinga cire wani abu a cikin albashina, amma sai ta ki ta
ce ita don Allah take zaune da ni,matsala daya a gurin
aikinmu ita ce manajanmu ba shi da mutunci.Farkon
zuwana ya yi ta shige min shi yana sona, ganin yanda na
birkice mishi sai ya sama min lfy, amma akwai zuga
rashin mutunci. In minti daya ka kara bisa karfe 8, to
zaya iya korarka, ban ta6a kai takwas ba tare da naje ba,
sbd ina matukar son aikina. Shadad yana da hkr yana
zaman shi gurin mai aiki. Cikin haka muka wayi gari cikin
farin ciki, Doctor ta samu juna biyu, Mijinta mu2m mai
mutunci da sanin ya kamata. Yayi murna, sai dai cikin
yazo mata da matsaloli masu dama, ko dn ta manyanta
ne? oho. Kwanci tashi ta shiga watan haihuwarta, mijin
ya ce ta shirya su tafi Abuja ta haihu a can, wani asibiti
na musamman. Sun tafi ko yaushe muna waya da ita,
maganarta daya kullum ita ce mu sa ta addu'a, sannan
ta ce min " Hafsa koda bn dawo ba kiyi kokari ke nemi
mahaifanki tare da neman yafiyarsu. Mummunan lbrn da
ba zamu ta6a mantawa da shi ba, musamman ni, shi ne
na rasuwar Doctor Hindu, nayi kuka tamkar raina zai fita.
Ta rasu bayan awa daya da haihuwarta, ta samu 'yan
tagwaye mace d namiji, Innalillahi wa inna ilaihin raji'un,
ko dangin Doctor basu kai ni jin mutuwarta ba, domin ni
ita ce dangina uwata kuma ubana. Can Abuja a kayi
jana'izarta, amma gidanmu ake zamn makoki, in da
dangin ta da na shi suka zo. Tun kafin bakwai na soma
tunanin gurin zuwa, don kan yanzun asirina ya tonu,
gatana ya fadi., A zaton danginta ni 'yar aiki ce, amma
dangin mijinta sun zaci ni 'yar uwarta ce, yaranta
tubarkalla, lafiyyu ana ta ji da su. Ranar 7 kuwa
subahanallah,tunda aka ce mu hada kayanmu za su rufe
gidan hankalina ya tashi, mai aiki kuwa dama daga
kauye take, bata samu matsala ba don ta riga ni tafiya.
Ga shi gobe zan koma aiki hutun da gurin aikina suka
bani a matsayin uwata ta rasu, kamar yanda na fada
musu. Rahma ce ta fado min a rai, yarinyar da muke aiki
shago daya da ita.Rahma tana da mutunci, bari in nemi
taimakonta. Na kira lmbrta t daga, na ce Rahma don
Allah ina nema wani agaji, ta ce na me? muryata ta
sarke, Rahma ina son dakin haya a unguwarku, zan
samu? Ta ce yau-yau din nan? Na ce eh, ta ce gskiya ba
za a samu ba, sai dai in an bincika a hnkl. Na ce na
shiga uku! Ta ce wai me yake faruwa? Na ce ba ni da
gurin kwana, ta ce, gidanku fa,? Na ce ba gidanmu ba
ne, kuma yau masu gidan zasu rufe gidansu, Ina da
matsala. Ta ce ok, yanzun kina ina? Na ce ina gidan ina
hada kayana, ta ce to za ki gane gidanmu? Na ce eh, ba
Tukuntawa ba? Ta ce eh, Mama tana nan sai kiyi mata
bayani kafin na dawo, na ce to na gode. Sun bani kayan
sawa nata da yawa, na nemo dan tasi ya dauke ni zuwa
Tukuntawa unguwar su Rahma, Mama da matar Yayan
Rahma ne kadai a gidan. Muka gaisa, Mama ta ce daga
ina? Sobada ganina da ta yi da kaya riki-riki na ce
sunana Hafsat gurin aikinmu daya Rahma. Ta ce oho,
yarinya da ku ka zo duba ni kwanaki ko? Na ce eh, ta ce
ba Rahma ta ce min Mamanki ta rasu ba? Na ce eh ba
Mamana ba ce, ta rike ni ne kuma yanzun 'yan uwanta
sun zo zasu rufe gidan saboda ya zama na 'ya'yanta. To
shi ne nake son ko zan samu dakin haya nan kusa da ku?
Ta ce to za a cigita, sauke yaron ki shiga da kayan ki
can dakin Rahma.
Ina jin dadin zama da su Rahma don ina yin biyayya gare
su, matar wan Rahma ce ka dai ke son min tambayar
kurilla,tana yawan cewa to wai ina iyayenki? Ban ta6a
amsamata ba, don ko Rahma bata san komai a kaina ba,
bata san Matsayin Shadad a gurina ba, duk da ta
cancanta in fada mata. Matsawar da nayi da son samun
dakin shi yasa su Mama suka sa ne man dakin, amma d
ta ce in yi zamana a nan gidan tun da ba ni da matsala,
haka dana. Na ce, a'a ni dai na fi sobn na samu daki
gidan mutunci gidan Hjy Iya aka samu dakin sai dai sun
ce min sai nayi hakur, don tana da fada. Na ce, ba
komai, in dai sai an tsokane ta ne zata yi to ba za ta
ta6a yin fada da ni ba. Matsalar in da zan dinga kai
yarona kafin ya isa shiga makaranta, ko da rainon kudi
ne. Ta ce, ki dinga kawo shi nan mana tunda shi ba mai
haya niya ba ne, Mun je naga dakin, karami ne ta ce
dubu shida shekara, dari biyar kenan dk wata, na ce ba
komai, zan biya. Naje banki na ciro dubu ashirin cikin
kudina nazo na bata shida, naje kasuwa na siyo kayan
abnci da yar tukunuya da dan risho na dawo.
Zaman mu da Hjy Iya ba matsala, don ina bn ta sau da
kafa,daga ni sai ita a gidan tun Asubahi in na tashi zan
wanke mana bandaki, in share tsakar gidan, komai na
dafa zan bata. In ko zan yi wanki na kan ce kawo naki
Hjy, kullum sai dai ka ji tana shi min albarka, Shadad
kuwa dama tuni ta ce in dinga bar mata shi tunda in
bana nan ba shi da matsala, musamman in ya gane cewa
gidan muke kwana. In ko unguwa na fita dashi kiwa ce
dashi, sannan ya yi ta 'yan rigime-rigime. Mun zauna
yanzu albashina da kyar nike kai dubu biyar banki a
wata, saboda hidimomin gida wanda a da ban san suba,
kai ko kan wannan ba zan manta da Doctor ba, domin ita
ce ke yi min komai. Burina na gaba shi ne, in koma
makaranta, amma yaya zan yi da aikina wanda shi na
dogara da shi? Wata rana da dare na shiga gurin Rahma
muna hira, na ce mata ina son na koma makaranta, ta ce
aikin fa? Na ce shi ne matsala, amma ina son in samu ko
'yar Diploma ba sai nayi jami'a ba, ta ce hakan ma yana
da kyau. Aikina daga karfe takwas din safe ne zuwa
hudu na yamma, sannan wasu su zo masu kaiwa dare,
na ce Rahma ko in koma aikin dare ne. Ta ce albashinsu
fa bai kai namu ba kuma yawan cinsu duk maza ne, na
ce to ya zanyi? Haka nan zan hakura in dai manaja zai
yarda ta ce matsayaci ba, sai shegen iko sai ka ce gurin
shi. Na ce ai dama ba shi ne da gurin ba? Ta ce ba shi
ba ne, na wata Hjy ce mai kudi, ina zaton ma ba a kano
din nan ta ke ba. Na ce to Allah dai yasa in dace zan
tare shi in masa mgn, Rahma ta ce to in ya ki fa? Na ce
ki taya ni addu'a ya yarda, Rahma ta ce to Allah yasa a
dace, in za ki masa magana sai muje tare .Haka ce kuwa
ta faru, domin washegari muna tashi daga aiki sai muka
nufi ofishin manaja, yana zaune gabn shi laptop ce.
Muka gaishe shi, cikin daurewa ya amsa, na ce "Yalla6ai
nazo neman uziri ne. Ya harare ni,wannan karon ko me
kika zo nema kuma kowa ya mutu ba zan ba ki wasu
kwanaki ba, sai dai in ki nemo wadda zata zauna
madadinki. Rahma ta ce, Sir, ba mutuwa akayi ba, tana
son koma mkrnt ne. ya ce, to sai ta bar aikin. " Ya ci
gaba da abn da yake yi. Muka kalli juna ni da Rahma, na
ce ko zan iya komwa akin dare? ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login