Showing 63001 words to 66000 words out of 105124 words
Chapter 22 - WATA KISSAR BY BOOK AISHA HUMAIRA .txt
ta ne ya kama shi, tabbas yasan yayi mata ba daidai ba, dan shi kansa ya yabawa dauriyar ta, dan ta bashi mamaki, Amma baze iya zuwa yace mata wani abu ba, to idan yaje meze ce mata?
Mufeeda harta rufe data zata kwanta aka kira ta a waya, ganin dare beyi sosai ba ta ɗaga, muryar Namiji taji suka gaisa tace
"ban gane me magana ba"
"Muffy beb, nasan bazaki gane waye ba, Amma me ƙaunarki ne, mezan samu ne daze sani nishaɗi"
"Dalla Malam Saurara, ina da Aure meyasa zaka dinga kirana, ko so kake ka kashemin Aure?"
"ƙwarai kuwa nasan ke Matar Aure ce, Amma kyakywar mace kamar ki baki dace da zama da Ammar ba, meze hana ki Auri wanda zaki huta kaman sauran 'yan uwanki?, zan baki zaɓi guda biyu ne, ko dai ki kashe Auren ki ki Aureni, ko kuma ki Amince mu dinga Soyayya muna hutawa ko kuma nida kaina ina kashe Auren, zaɓi ya rage naki"
Mufeeda ta tashi zaune tace "Allah ya shiga tskanina da kai, yayi min maganin ka, Kuma koma waye kai Na barka da Allah ya nuna maka ikon sa, Kuma nida Ammar Mutu ka raba"
Ta kashe Wayar ta, tayi blocking ɗin lambar, what's App ta koma taga Yaya Amina a online, nan ta gaya mata abunda ya faru da wanda ya kira ta yanzu da wanda ya biyo ta ɗazu.
Amina tace "Anya Mufeeda ba duk mutum ɗaya bane, inaga wanda ya biyo ki ɗin nan ne, kuma da ƙyar in be sanki koya san Ammar ba, Abunda ya kamata shine ki gaya masa"
Mufeeda tace "Kai Yaya Amina nasan halin abina, ƙyaleshi kawai idan, nayi blocking ɗin lambar sa"
"Amma kina ganin babu matsala idan baki gaya masa ba?"
"Zan gaya masa amma ba yanzu ba".
Ɓangaren Ammar har ya kwanta yaji saƙo ya shigo wayarsa, da sauri ya ɗakko ya duba yayi zaton Mufeeda ce
"KASA IDO SOSAI AKAN MATAR KA, DAN TANA AIKATA WANI ABU A BAYAN IDON KA, DAGA ME ƘAUNAR KA!!!
In an karanta amin share zuwa wasu groups ɗin dan Allah
Ayimin afuwa ba Editing
Domin sharhi gyara ko Shawara
Ayshercool 07063065680
[11/07, 8:43 PM] Ayshercool: ..✨✨✨✨
*WATA KISSAR...... *
✨✨✨✨✨
( *Sai Mata* )
*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞
( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P.W.A✍️
*_A SHORT LOVE STORY_*
*Story and written by*
'''AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)
The experience writer of ABDUL JALAL'''
Na sadaukar da wannan littafin ga Ɗaukacin masoya na, wanda nasani da wanda ban sani ba
Watpad @ Ayshercool7724
What's app 07063065680
Gmail Www.ayshertadam@gmail.com
Please follow me on Wattpad, vote and Comment
https://www.wattpad.com/1096499534?utm_source=android&utm_medium=com.fmwhatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Ayshercool7724&wp_originator=NWkhlySuZ8Eug%2BopXFfcycv2JGS3axjaccC5%2FbUYT6YzeXAYV4ybw7FnTr8fHQDwo5ncF8TNfQfelSdeR5t0OZi0%2FKAiAcvwuLa561y0j%2BMpxBPI15z3EyzU4ZruY9KP
ELEGANT ONLINE WRITER'S
Page 20
Shiru Ammar yayi yana sake juya message ɗin, tsaki Yayi ya ajiye tare da sawa ransa wrong Number ne kawai.
Ya ajiye Wayar da niyyar yayi bacci amma ya dinga tunanin Message ɗin, Halayen Mufeeda ya dinga tunawa na kirki, dan haka ya ƙara tabattar wa da kansa cewar wrong Number ne, tunanin daren su na jiya ya tsaye masa a rai, yana tuno wasu abubuwan da suka kasance tsakanin su, ɗan murmushi Ya dinga yi tare da rungume filon sa, Tunani yaita yi a ransa ko ya jikin ta? Me ya kamata yayi mata ko ya bata wanda zesa taji daɗi, yana wannan Tunanin wani nannauyan bacci ya ɗauke shi.
Da safe ma fitowa Yayi ya tarar tana ta aikace aikacen ta ya kalleta ko rigar bacci bata canza ba tana mopping
"Sannu agogo sarkin aiki, ki dinga sassautawa kanki da wannan aikin mana"
Ɗagowa tayi tare da yin murmushi ta ɗan risina tace "Ina kwana Yallaɓai"
"Lafiya ƙalau, kin tashi lafiya?"
"Alhamdilillah"
"masha Allah"
Yaje ya nemi guri yana zauna, ta kammala aikin ta, ta kalle shi tace
"in kawo Abinci ne ko se an jima, ina so inje in wanka ne"
"Je kiyi ki fito semu ci"
Ta kalle shi ta lanƙwasa kai tace
"za'a bani a baki?"
"Je kiyi wankan ki dawo dai"
Taje tai wanka ta canza kaya, sannan ta fito ta gabatar da kayan breakfast din, kaman Yadda ta buƙata Ammar ke bata Abincin a baki, yana ci yana bata.
Mufeeda ta so tayi masa zancen wanda ya kira ta amma se taga Ammar yayi mata kwarjini bata san a ya ze kalli abun ba.
Ɓangaren Ammar kuma tausayinta yake ji Sosai, yana son ya tambaye ta ya jikin ta? amma Izzar sa ta hanashi ji yake yin hakan tamkar ya faɗo ne a idon matar tasa.
Se da suka kammala yana ƙoƙarin tashi yaje ya shirya, tazo ta kwanta a jikin sa.
Ammar yace
"Ya haka? Fita fa zanyi rana ta fara yi"
"Nifa bana gajiya da ganin ka, ka bari in ƙara ganin ka mana"
"Kinga ɗagani ina sauri"
"Me kake so in girka maka kafin ka dawo?"
"Kome kika dafa zanci"
"Shikenan bari in jira ka anan ka shirya semu yi Sallama"
"Zo muje ki tayani in shirya"
Zumbur ta miƙe daga jikin sa ta koma gefe tare da tura baki
"A'a ina nan ka shirya seka fito"
Ammar ji yayi kaman yayi dariya amma ya basar ya shige ɗakin sa.
Tana nan zaune a falo ya fito ya shirya tsaf ze fita, wani murmushi tayi masa daya sa Ammar ƙura mata ido, ta tafi inda yake tsaye tace
"Kayi kyau sosai babban mutum, Allah ya kiyaye min kai ya ƙara mana Arziki, Allah yai maka jagoranci Namijin duniya"
Ɗan murmushin gefen baki Ammar yayi yace "Ameen" sannan ya fice.
**************
Mufeeda na zaune na aikace aikacen ta, yaro yayi sallama tai masa izinin ya shiga dan gidan Maman Nur ne ya gaishe ta ta amsa cikin sakin fuska, Yaron yace
"Wai cewa akayi inzo in gaya miki umman mu ta haihu"
Mufeeda tace
"masha Allah, kace ina mata barka kafin in shigo" tai masa kyautar sweet sannan ta Sallame shi ya tafi.
***********************
Nasreen zaune suna hira da Fa'iza , Nasreen tace
"Fa'iza wai ya ake ciki da mutumin ne? Ina fatan zuwa yanzu dai kinyi wani ƙoƙari?"
"bari kawai, ina ta up and down a gidan Anty Jidda ina kushe ta ina ƙara tura mata tsanar ta, in gaya miki anan naga wata guzuma wai ita ce tsohuwar budurwar Ammar wadda ze aura da, na maze in gaya miki ban nuna musu komai ba, Amma itama zata gane kuskuren ta, yanzu ba ta tata nake ba, ina nan ina shiryawa matar Ammar tarkon da ba zata fita ba se Auren nan ya mutu "
Nasreen tace
"Shikenan Allah ya taimaka, amma dai abi komai a sannu dan wallahi Fa'iza yarinyar ta fara bani tausayi, Yarinya ce ƙarama ga Sanyin Hali"
Tsaki Fa'iza tayi tace
"ki koma bayan ta kenan?"
"A'a nina isa in koma bayan ta in bar 'yar uwa ta, bata isa ba ina bayan ki har yanzu"
"In dai kina bayana to ki cigaba da goyan baya"
"Karki wani damu ana mugun tare"
Suka yi shewa tare da tafawa.
********************
Mufeeda ta kira Ammar a waya ta gaya masa anyi haihuwa zata shiga barka yace mata to.
Da Yamma Ta shirya ta fita da niyyar yiwa Maman Nur barka, amma tana zuwa aka ce mata ai, an tafi da ita Asibiti tana ta zubar da jini Jaririn ma kaman bashi da lafiya.
Mufeeda ta Jajanta musu ta fito, akwai surprise ɗin da take shiryawa Ammar dan haka ta miƙe ta tafi titi shagon da take son yin siyayyar da take buƙata.
Seda tai siyayyar ta ta gama ta kama hanyar komawa gida.
shan gaban ta akayi da Napep taji ance
"Ke 'yan mata daga ina?"
Ɗagowa tayi a fusace zata yi magana seta ga Ammar ne, Murmushi tayi tace
"Nice' yan matan? To ɗan Saurayi siyayya na fito"
Ammar yace
"kin cemin zaki shiga maƙota barka amma in ganki anan, me kike yi?"
"Allah ya bada haƙuri, Siyayya na ƙaraso titi nayi, kuma nayi niyyar gaya maka dama"
"Shikenan shigo mu tafi"
Ta ɗan kashe masa ido tace "Nawa zan biya?"
Ɗan murmushi yayi saboda haɗuwar su ta farko ya tuna.
Shiga tayi yaja babur ɗin, maimakon su tafi gida kai tsaye seda yayi zagaye da ita sannan suka nufi gida, a hanyar su ta komawa gida Mufeeda tace
"Yaya Ammar zan sai Kayan miya a gurin me kayan miyan kan layi"
Ammar ya jinjina mata kai, Kafin su ƙarasa bakin layin taga motar wannan mutumin da ya biyo ta ranar a ƙofar wani katafaren gida.
Tunani ta fara yi a ranta
"Kenan mutumin nan a unguwar nan yake kenan?"
Ammar ya kalle ta ta mirror yace
"ya dai? Akwai magana ne?"
Saurin girgiza masa kai tayi alamar A'a.
Suka tsaya gurin Sa'idu me kayan miya, suka sai kayan miya sannan suka yi gaba.
Mijin Maman Amir na gurin me kayan miyan shima yaje siyayya, Sa'idu me kayan miya yace
"Taɓɗijan Iska na wahalar dame kayan kara"
Mijin Maman Amir yace "kamar yaya?"
"Hmm ai Matan yanzu se Addu'a, wannan maƙocin naku me A daidaita sahun nan, baka ga Yadda yakewa gidan sa hidima ba, kusan kullum cikin cefane yake, ko ya shiga shagon Sunusi me kanti siyan madara, ƙwai bredi, kusan duk ɗan cinikin nasa a haka yake tafiya, Amma rannan da tsakar rana ba kunya na ganta ita matar tasa tana zance da wani Alhaji me mota, seda na ƙura ido naga ashe Wannan Alhajin ne na bayan layin nan, Alhaji Idris "
Buɗe baki Baban Amire Yayi yace
" Kai haba dai? "
" Wallahi dagaske nake, Allah ya nunamin Annabi kamar yadda na gansu "
"Taɓɗijan amma wannan anyi sakaryar mata, To Allah ya tona mata Asiri, shegiya da idon ta kamar an soya Aya, ashe munafuka ce, ai shiyasa mutum ya zama tsayayye a gidan sa, ni mata ta isa taimin wannan shirmen? A haka kalle shi kamar namijin gaske sakarai ni har ya ban haushi"
Haka Baban Amir ya ci gaba da zazzga tare da zage zage shikuma me kayan miya yana ziga shi.
Seda baban Amir ya tafi Sa'idu yace
"Aikin banza ji yadda yake wani cika baki waishi ya isa da gidan sa, Kamar ba nan matar tasa take yawo kwararo kwararo tana fallasa Asirin sa ba, anan gurin nan suke zama take zazzage sirrin sa ba waishi ke ya isa da gidan sa, aikin banza, ni ina nan gefe ayi dai mu gani"
********************
Da safe Ammar ya tashi daga bacci ze fito ya ɗakko wayarsa ya kunna, saƙo ne ya shigo wayar sa yana dubawa saƙon Mufeeda ne na birthday wishes ya shigo wayar sa, saƙon cike yake da nuna fatan Alkhairi da kuma tsantsar Soyayya a ciki, Murmushi yayi ya ajiye wayar har ya miƙe wani saƙon ya shigo wayar sa
"KA SA IDO AKAN MATARKA, TANA AIKATA RASHIN GASKIYA A BAYAN IDON KA"
Mamaki ne ya kama Ammar shiru yayi yana tunani, yana sake juya saƙon, wani irin rashin gaskiya ne Mufeeda zata aikata a bayan idonsa? Tunani yake akan Yadda take masa biyayya iya yinta, taya za'ace tana aikata wani abu a bayan idon sa? Amma zeso yasan wanda yake ya turo masa wannan saƙonnin.
A hankali ya ajiye wayar ya miƙe jiki a sanyaye ya fito falon.
Yana fitowa ya tarar da Mufeeda ta saka mini Skirt da wata 'yar ƙaramar riga shara shara bata ƙarasa rufe mata cikin ta ba, tayi parking ɗin dogon gashin ta, ta saka hular hat tana rawa a falo tana juya jikin ta a hankali tana bin sautin waƙar dake tashi a talabijin ɗin dake falon, ba tsammani ta juyo taga Ammar a tsaye yana kallon ta, da Sauri ta ƙaraso inda yake tsaye tana faɗin
"Happy birthday to you Hubby"
Kallon ta kawai yake yi, ta riƙo hannun sa zuwa falon ya samu kujera ya zauna ta cire hular kanta ta dube shi tace
"barka da zagayowar ranar haihuwar ka Mijina Allah yayi wa rayuwar ka Albarka"
"Ya akayi kika san yaune ranar zagayowar haihuwa ta?"
"Barwa zuciya abunda take so Hubby, ina son yin wani abu daze faranta maka kawai na samu labarin wannan kwanan watanne na haihuwar ka, shiyasa na maka barka da zagayowar ranar haihuwar ka"
A hankali ya janyo ta jikin sa yana shafa gashin kanta da yasha gyara ya kwanta yana ta tashin ƙamshin mayuka, tunani yake akan saƙon da aka turo masa, yana cikin tunanin yaji muryar ta tace
"Abun sona naso mu kasance cikin farin ciki yau, Amma naga kamar baka walwala, Allah ya sa ba laifi nayi maka ba"?
Tai maganar jiki a sanyaye, Ajiyar zuciya yayi yace "muyi breakfast ko?"
Jinjina masa kai tayi, har suka kammala Mufeeda na kallon sa tana tunanin meke damun sa? Sosai kayan da ta saka suka karɓi jikin ta tayi kyau sosai, Amma tunanin da yake yaƙi barin sa ya kalleta sosai.
Ya shirya tsaf ze fita Mufeeda ta bishi
Cikin sanyi jiki tace
"Allah ya kiyaye hanya, Amma gaba ɗaya inajin babu daɗi da yanayin da kake yau, ban sani ba ko be kamata inji damuwar taka ba, Amma idan ni nayi maka laifin kayi haƙuri dan Allah"
Bece mata komai ba ya fice.
Gaba ɗaya Mufeeda haka ta wuni babu daɗi, ta shirya masa abubuwa da dama yau amma taga kaman baya cikin farin ciki, haka ta dake ta ci gaba da abunda ta shirya masa.
Ɓangaren Ammar ma yana tunanin wani irin Abu Mufeeda zata yi haka a bayan idon sa, wani sashe na zuciyar sa na ƙara yadda da matar sa akan babu wani abu da zata iya aikatawa na rashin gaskiya a bayan idon sa, a zaman da suka yi ya yadda da amanar ta.
Da daddare ya dawo gida a matuƙar gajiye, tunda ga falo yaga ta sauya tsarin falon, ta canza gurin zaman kujerun, ko ina se ƙamshi yake a gidan.
Fitowa tayi daga ɗakin ta tayi simple make up, yanzu ma English wears ne a jikin ta, murmushi tayi masa tace
"Birthday man sannu da zuwa, shine ka fita ka daɗe ko? Ko ka leƙo gida ai shikenan, zomu je ɗakina am having a surprise for you, na shiryawa wannan ranar sosai fa"
A ɗan hasale yace "Ke ni ki ƙyaleni, bana son duk wannan abubuwan shirmen naki, ki rabu dani"
Gaba ɗaya jikin ta yayi sanyi ƙwalla ta cika idon ta tace
"Yi haƙuri, Allah ya baka haƙuri, ban san baka so ba, dana san baka so da ba zanyi ba Insha Allah bazan sake ba, Allah ya huci zuciyar ka, Allah yabaka haƙuri" tai maganar muryar ta na rawa hawaye na bin Fuskar ta.
Da sauri ta juya ta koma ɗakin ta ta rufe ƙofa.
Jikin Ammar ne kuma yayi sanyi da abunda yayi matan, a hankali ya nufi ɗakin sa shima, yana buɗe ɗakin yaga shima tayi masa ado, ga zane zane na heart da tayi me ɗauke da sunan su a jiki da kalaman Soyayya dana fatan Alkhairi.
Ga balloons data hura ta ƙawata ɗakin se ƙamshi yake, gefe ga cake me fari da pink ta saka HAPPY BIRTHDAY HUBBY, ga lemuka da alawoyi data shirya, tausayin ta ne ya kama shi, besan adadin lokacin da tayi tana wannan shirin ba, be san adadin kuɗin da ta kashe akai ba dan kawai ta sashi farinciki, amma lokaci ɗaya ya Gwale ta.
Rage kayan jikin sa yayi ya shiga yai wanka yana ƙara kallon ɗakin yadda yai matukar kyau, fitowa yayi ya nufi ɗakin ta.
Yana zuwa yaga ta cire kayan adon da tayi, ta zauna a tsakiyar gado idon ta sharkaf da Hawaye ta hargitse gashin kanta tana kuka.
Ƙarasowa yayi ya kalle ta yace
"Taso muje a bani cake ɗin"
Ɗagowa tayi tana kallon sa hawaye na cigaba da bin idon ta,
"Taho mana"
yai maganar yana ƙara kallon ta, a hankali ta matsa inda yake zata sakko daga kan gadon, tausayin tane ya ƙara kama shi, bata iya fushi da shi, banda lokacin da tayi fushi harta fasa masa waya, bata iya fushi dashi ko tayi ma ita ke fara sakkowa ta bashi haƙuri.
Kafin ta sakko daga kan gadon yasa hannu ya ɗauke ta, kamar wata 'yar yarinya kuwa ta kwanta tai lamo a jikin sa.
Ɗakin sa ya nufa da ita, ya ajiye ta a bakin gado ya kalleta yace
"waye ya koya miki zane ne?"
"bakowa kawai iyawa nayi" jinjina kai yayi, kayan snacks ta gabatar masa, ai kuwa Ammar yaci sosai, shi irin wannan abubuwan basu dameshi ba shi dai kawai yaci Abinci ya dena jin Yunwa, wani abunma zama da Mufeeda yasa shi iya cin sa.
Ta yanka cake ɗin nan takai bakin sa, buɗewa yayi tasa masa, tunda Ammar yake be taɓa cin cake ɗin birthday ba, jin cream ɗin nan yayi har kansa dan daɗi.
"A ina kika siyo cake ɗin nan?"
"Ni nayi fa"
"A'a gayamin gaskiya dai"
Taso ta tsokane shi tace santi yake, amma ta tuna ze iya dena ci in tace haka dan haka ta ƙyaleshi, gaba ɗaya Ammar ya manta da abunda yake damun sa kuma yaji daɗin abunda ta shirya masa sosai, Amma kunsan halin mutumin bazece ya yaba ba.
Seda suka gama ciye ciyen su, Sannan Ammar ya nemi gurin kwanciya, har zata tafi ɗakin ta, ta fasa ta dawo ta hau kan gadon tace
"Yaya Ammar har yanzu baka gayamin laifin da nayi maka ba yau, gaba ɗaya yau haka na wuni raina babu daɗi ka gayamin dan Allah"
Juyowa yayi ya zuba mata ido ba tare da yace komai ba.
"Kayi Magana mana, kabarni a cikin damuwa fa"
Maimakon yace wani abu sema janyo ta da yayi jikin sa yace
"meyasa kika ɓata gyaran gashin da kika yi?"
"Ai cewa