Showing 9001 words to 12000 words out of 31350 words

Chapter 4 - FATALWAR DEBORAHBook Complete By Mrs Sadauki.txt

Advertisement

04 Mar 2025

4662

tare da tawwasali da kyakkyawan zantukan na Ubangijina da ya kiyaye Ni daga sharrin dukkan dodanni,daga sharrin dukkan wasu dabbobi masu dafi da kuma sharrin dukkan wata ido mai cutar maita ”

“Na gode! Yanzu wacce hanya zan bi na koma gida?” na tambaya,shuru ta ɗan yi kafin ta ce “gaskiya ba zan yi miki ƙarya ba,komarwaki ba yanzu ba sai dai kina iya balaguron ruhi ki je kuma ki dawo”

Ban gane abin da take nufi ba,da na tambaye ta kuma sai ta ja ni muka wuce can gidansu.Sosai na yi mamakin yadda duniyar ƙasan ruwa ma take ɗauke da gidaje da kuma iyalai,iyayen Sarah suna da kirki sosai na samu tarba mai kyau na ci na sha sannan muka wuce ɗakinta mai ɗauke da gado da komai na buƙatar mace.

Kasancewarmu cikin ruwa ba shi ke nufin ka yi wanka ba a'a,har da toilet ke da kwai da kuma abubuwan gyaran jiki.Haka na shiga na yi wanka ina ta mamakin duniyar,bayan na fito sosai na ƙara wani mamakin ganin kayan jikina a saman gado.


“Ki yi sauri ki shirya domin ki ziyarci mijinki,in kin je ki sanar da shi duk abin da ya faru zai fahimce ki sannan ki aje hankali ki sama masa nutsuwa”

Ni dai banda kallonta babu abin da nake yi,ban bari ta yi min kwalliya ba sai da na yi sallolina sannan na shirya cikin wata haɗaɗiyar rigar bacci.Turare na fesa sannan na ce “yanzu ya za a yi na je can ɗin?”

“Kin fiya sauri kamar zawo,ki jira mana ina haɗa jirgin balaguron ne”Sarah ta faɗa tana mai zana gidan gizo-gizo,bayan ta gama ne ta umarce ni da na lumshe idona sannan na ratsa ta cikinsa haka kuwa aka yi.


Ina yin yadda ta ce sai na tsinci kaina a gidan Uncle Salem,a cikin ɗakinsa ban bayyana ko ina ba sai a cikin madubi.Ya fito daga wanka ƙugunsa ɗaure da towel yana goge gashinsa da ɗan ƙarami,sai na ga ya fara buɗe ƙofofin hancinsa alamun ya ji ƙamshi jikina kenan .Na saki murmushi na ce “kawo na taimaka maka na tsane ma jikin” da sauri ya juyo muna kallon juna,kafin ya ce “Naf?” na yi murmushi na ce “ka taimaka min na fito”

Hannunsa ya miƙo ni kuma na ɗora nawa ya jawo ni,na yi tsalle na ƙanƙame shi.Ya ce “ina jin ki a jikina amma na bar ganin ki”

“Dama ba za ka iya ganina ba saboda ni ruhi ce” na basa amsa ina mai kai wa lips ɗinsa sumba,kan bed muka zube da dukkan alamu shi ma yayi kewata na san halin Uncle sosai muddin yana gida to kowanne dare sai mun kyautata shimfiɗar aurenmu.Cikin shauƙi da bege muka raya daren,ina dab da yi masa bayanin abin da ke faruwa na ji Sarah ta fizgo ruhina na koma can ƙasan ruwa.Na buɗe ido ina kallonta cike da takaici na ce “ya kuma za ki yi min haka?”


Ita ma rai ɓace ta ce “kafin ki je sai da na faɗa miki da kin je za ki yi masa bayani amma kika fara da wata sumbatarsa,sannan tuni hasken alfijir ya keto inda na ƙara ko minti guda ne za a samu matsala don duniyar ruwa ba irin taku duniyar ba ce nan muna da ƙa'ida” tana gama faɗa ta fice ta bar ni nan.


★Gidan Uncle Salem

Shi ɗin ya yarda da akwai ɓoyayyar duniya wannan yasa bai yi mamakin ziyarar da Nafisa ta kawo masa ba.Sosai ya ji daɗin kasancewa da ita don babu wani banbanci tsakanin mu'amalar ruhi da kuma ta gangar jiki, washegari cike da walwala ya fito kusan kowa ya ga canjin amma ba wanda ya san dalili hatta kuwa Deborah wacce take jin kwaɗayinta a kansa ya ƙaru.

Yau girki na musamman ta yi wa ƴan gidan wanda ko kaɗan ba ta wani shan wahalar kunna gas,cikin iya tsafinta take yin komai.Da dare bayan ta faki idon mutane haka ta haura sama,ɗakin Nafisa ta je ta buɗe drowerta ta ɗauko kayanta sai ta shiga toilet ta tsoma kayan cikin ruwa.Da wannan ruwan ta yi amfani ta yi wanka,nan take jikinta ya fara rikiɗa ya koma irin na Nafisa.Cike da makirci ta shirya cikin wasu fitinanun kayan bacci ta fesa turare sannan ta nufi ɗakin Uncle Salem ta je haye bed ɗinsa,shi kuwa bawan Allah yana toilet yana wanka sai tunanin moments ɗinsu na jiya yake.

Yana fitowa yau ma da ƙamshinta ya fara cin karo irin na jiya,ya washe baki yana kallonta jikinsa har rawa yake ya haura gadon yana mai cewa “Naf?”

Ita kuwa FATALWAR DEBORAH wacce ke ɗauke da siffar Nafisa cike da zaƙuwa ta rungumo Uncle Salem.Daidai nan free page ya ida mai son ci gaba 500 ne via 2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank DM +22795045822


*NB:* lokacin posting sai bayan shan ruwa in sha Allah.
[28/02 10:12] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️


```LoVe aNd HoRrOr story```👽


By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.


*FCWA*☀️

________________________


01


Ra'ayi riga in ji ƴan magana, wannan haka yake a lokacin da matasa sa'anina ke sha'awar fita waje domin yin dogon karatu tare da burace-buracen ababen ƙyalƙyalin duniya ni kuma shiga ƙauyuka ne ra'ayina domin koyar da yaran da ke cikin duhun jahilci.Sunana Nafisa,matashiyar budurwa ƴar kimanin shekara ashirin da biyu a duniya.Na fito gidan sarauta,a jinin masu izza da taƙamar dukiya sai dai ni sam ba wannan ne a gabana ba.Duk da na sha wahalar shawo kan mahaifina kan ya bar ni na yi karatun zama malamar makaranta amma kuma fafur ya hana ni fita aiki wanda hakan ba ƙaramar barazana ba ce da cikar burin nawa.

Fuska shaɓe-shaɓe da hawaye na nufi ɗakinsa,shine kaɗai tilo da na san zai iya yin magana mahaifina yayi amanna da ita ba tare da gardama ba.Ko sallama ban yi ba ballantana neman izini kawai na tura ƙofar,kamar kullum yana zaune kan dadduma yana jan casbi.A gabansa na zube kamar raƙumar da ke jin ƙishi,ya ɗago fararen idonsa ya zube su a kaina kafin cikin tattausan furuci ya ce “Naf !”
Baki na turo gaba idona na sake zubo da wasu sabbin hawayen.
“ Yau kuma wa ya taɓa ki?” ya tambaye ni cikin nutsuwarsa wacce ke ƙara masa ƙwarjini.


Cikin kuka na ce “Daddy ne wai ba zan yi aikin gwamnati ba”

Yayi murmushin da ya bayyana fararen haƙoransa waɗanda kullum suke shan gugar asuwaki kafin ya ce “ki je zan yi masa magana” da sauri na girgiza masa kai na ce “ a'a Please uncle ka tashi mu tafi yanzu kafin masu hura wuta su ƙara masa ƙaimi” na faɗi haka ne saboda ahalin gidanmu suna da ɗagawa sosai ta yadda suke ganin kamar ƙasƙanci ne a ce jinin gidan ya je yana aikin gwamnati,aikin ma koyarwa.


Ya buɗe baki zai yi magana na yi saurin kamo tafin hannunsa wanda yake lutuf da tsoka sai taushi kamar na mace,hannun nasa ya duba da sauri na sake shi saboda ba tun yau ba ya yi min hani da hakan ba wai iya gare shi ba kawai a'a hatta ƙannaina maza ya hana ni raɓar su ko kuma taɓawa a tsakaninmu.


Na sunne kai wasu hawayen na sake surnano min suna ɗiga kan farin hijabina.
“Nafisatu?” ya kira ni cikin wani salo,ba tare da na ɗago ba na ce “ na'am uncle”
“Me yasa ra'ayinki ya banbanta da sauran danginki? Me yasa kike son yin aiki alhalin mahaifanki sun tanadar miki komai na rayuwa?”

Na ɗago na dube shi kafin na ce “ uncle kai ma ba ka son na yi wannan aikin jahadin na shiga ƙauyuka ina wayar da kan al'umma? Saboda me uncle? Kawai don iyayena suna masu arziki shi kenan sai na yi kwance na dogara da dukiyarsu? Me yasa ni ba zan yi aiki ba?”

“ Saboda ke mace ce!” ya bani amsa yana kallon idona,ji na yi kamar ya watsa min ruwa zafi kawai sai na tashi na fita a guje ina gwanjin kuka.Ina shiga babban falonmu duk sai na tarar da ƴan uwana kuwa suna ta cece-kuce akan maganar,ɗakina na wuce direct na haye gado na kwanta rub da ciki amma abin mamaki sai na ji tamkar kan cinyar mutum ne kaina yake amma sam ban bai wa hakan muhimmancin ba na ci gaba da rera kukana,har na fi jin haushin rashin goyon bayan Uncle Salem kan na Daddyna.A hankali na soma jin ana shafar gashin kaina wanda ke luluɓe da hijabina,ido na soma lumshewa ba tare da na shirya ba yayin da kuma na soma sauke numfashi akai-akai.Ban sani ba ko na shiga duniyar mafarki ne ko kuwa zahiri ne amma sai na tsinci muryar wata dattijuwa na yi min gatana haɗi da bani tarihin ababen tsoro kamar yadda na fi ƙaunar kallon horror film.


★A can ɓangaren Uncle Salem kuwa Nafisa na fita da gudu yayi saurin tattare littafansa kafin ya gyara zaman hiramin kansa ya fito.Direct ƙofar da za ta sada ka da babban falon ya nufa bakinsa ɗauke da sallama,tsit duk falon ya ɗauka kafin duk su yi ƙasa da idanunsu saboda yadda yake da matuƙar muhimmancin da kuma girma a idonsu.Cike da girmamawa suka soma gaishe shi “ Barka da fitowa Daddy ƙarami“ domin haka suke kiransa in ka fidda Nafisa da take ce masa Uncle ita ma ɗin shine da kansa ya koyar mata da hakan.


“Fatan dai ba ƙara ta ba aka kai wurinka,a toh don na san ba kasafai za a gan ka a nan ba” cewar Daddy yana ɗan murmushi yana kallon babban abokinsa,amininsa kuma ɗan uwansa.Uncle Salem ya ce “tun da ma ka sani ai shi kenan sai a fara shirya mata abubuwan da za ta buƙata in ta je can”


Daddy ya ɗan nisa yana kallon yaran wurin duk sai suka tashi suka kama gabansu,sai a lokacin kuma Uncle Salem ya zauna suna fuskantar juna.

Duk shuru suka yi na wani ɗan lokaci kafin Daddy ya ce “ ba wai yadda kake tunani ba ne aboki,ina da dalili na daban da yasa ban so Nafisa ta yi nisa da gida”
Uncle Salem ya murmusa ya ce “tun muna makaranta ake faɗar wannan kalmar akan kana da dalilin ƙin yin wani abu amma har yanzu ba ka taɓa faɗa min mene ne dalilin ba.Abdul Hameed ka sani cewa su yara da kake gani sun fi son bin zaɓinsu kan na iyayensu,kuma kai ma in ba ka manta ba...” sai kuma yayi shuru.
Yanayin fuskar Daddy ta ɗan sauya kafin ya ce “babu damuwa zan bari ta je ɗin, Allah ya bada sa'a ya kuma tsare ta akan abin da nake tsoron faruwar” da “amen“ kawai Uncle Salem ya amsa kafin ya miƙe tsammm ya nufi ɗakin Nafisa,ya tura ƙofa tare da yin sallama sai kuma yayi tsaye cak yana buɗe ƙofofin hancinsa saboda kalar wani ƙamshi da ya dake shi da bai taɓa jin irinsa a wannan duniyar ba....
[28/02 10:12] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️


```LoVe aNd HoRrOr story```👽


By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.


*FCWA*☀️

________________________


02


Tsaye yayi yana kallon yadda take bacci tana wani taɓe baki kamar mai kuka yayin da goshinta ke fitar da gumi.Ya furzar da wani huci kafin ya ƙarasa ya zauna bakin bed ɗin,a hankali ya cire mata hijabin nata wanda ya ɗan jiƙe saboda zufa.Sumar kanta wacce take baƙar ƙirin ya soma shafawa yana tofe ta da addu'a,a hankali ta soma sauke ajiyar zuciya tana wani motsa idonta kamar mai son buɗe su.

Kamar wanda ke wasa da maciji haka ya soma shafa farar fatar fuskarta wacce ta yi ɗan ja saboda kukan da ta yi.Wata irin azababiyar ƙaunarta ce yake jin tana bijiro masa,ji yake tamkar ya ɗauke ta ya haɗiye tsabar so.

Sam bai san abokin nasa ya shigo ba don ya lula sosai a duniyar tunanin muradun ruhinsa,sai jin saukar muryarsa yayi “ sai yaushe ne za ka sanar da ita ɓoyayyen sirrin da ka binne abinka?”

Uncle Salem yayi saurin ɗagowa ya dubi Daddy ya saki ɗan murmushin da ya zame masa jiki kafin ya ce “ har yanzu Naf yarinya ce aboki,zan ƙara mata lokaci ” sai kuma ya mayar da duban nasa ga fuskarta a iya kallon da yake jifar ta da shi ya isa ya fallasa ma sirrin da ƙunshe a zuciyarsa.


“ Shekarunta ashirin har da biyu fa,lokaci na ƙurewa girma na sake zuwar ma amma har yanzu ba ka ajiye iyali ba aboki” Daddy ya faɗa cikin rashin jin daɗi.

“ Shi aure ai ba sauri yake so ba,a'a fahimtar juna aboki.Ka yi tunanin yadda Naf za ta ɗauki lamarin ne in ta ji cewa ni mijinta ne alhalin a uba ta ɗauke ni?”

Daddy yayi murmushi kafin ya ce “ to ai kun fi kusa,ban iya na sani”


Uncle Salem na shirin yin magana aka shigo haɗi da sallama,Ammy ce hannunta riƙe da kofin ruwa.A mutumce ta gaishe da Uncle Salem wanda a girme ya girme mata sannan ta dubi mijinta hasken idaniyarta ta ce “ ga maganinta yau ba ta sha ba sam” ya karɓa ita kuma sai ta fita.

Kan dakalin gado Daddy ya ajiye maganin yana mai kallon Nafisar wacce har zuwa yanzu take baccinta yayin da kuma hannun Uncle ɗinta ke kan sumarta.


“ Aboki me kake ɓoye min dangane da Naf?” yayi tambayar cike da kulawa.
A ɗan rikice Daddy ya ce “ no babu komai zan je na duba wasu takardu in ta tashi ka bata maganin” yana gama faɗa ya fice,shi kuwa Uncle Salem kai ya girgiza tun suna yara suke tare amma har izuwa yanzu bai san dalilin da yasa abokin nasa ke ɓoye masa wani babban sirri da ke ɗawainiya da rayuwarsa.Tun da Nafisa ta soma tasowa yake lura da yadda hankalinsa kocokwam ke kanta hatta makaranta in ta je ya dinga kiran waya kenan yana tambayar labarinta,yana ɗaya daga cikin abin da yasa kuma ya basa aurenta tun ba ta san kanta ba amma har yau ya ƙi sanar da shi mene ne sirrin.


Ganin kamar baccin nata irin wancan ne da ta saba yi ,sai Uncle Salem ya ɗauki kofin maganin ya cika bakinsa da shi kafin ya taɓe bakinta yana ɗura mata shi kamar yadda tantabaru ke ciyar da junansu,a hankali kuma take haɗiye ruwan maganin da shi ne ya haɗa mata shi a haka har ta shanye shi tasss.Da ya kai ƙarshe sai da ya ɗan lashe mata lips kafin ya miƙe ya fita,sashensa ya nufa ya rage kayan jikinsa yayi wanka ya fito ya shafa turare kawai sai ya ɗauki system ɗinsa ya soma aiki yana duba saƙonnin sojawan da shine ya tura su mission a daji.Reppot ne iri-iri wasu na murna wasu na jimame,tuni kansa ya soma yin hayaƙi yana jin cewa da buƙatar ya je can ɗin da bada wata sabuwar atisaye.



★ NAFISA


Ban san iya lokacin da na ɗauka ina bacci ba,ko da na tashi da ƙamshin turaren Uncle Salem na soma cin karo wanda ya game ko ina na ɗakin.Na turo baki gaba kafin na dubi hijabina wanda na san da shi ne ya cire min shi ko shakka babu.Wanka na shiga,bayan na fito na yi sallar azahar don sallah na ɗaya daga cikin abin da na fi so a kaf cikin abubuwan ibada ita da azumi wannan kuma horarwa Uncle Salem ce tun ina ƴar shekara sha uku yake saka ni yin azumin Litinin da Alhamis,tun ina kukan yunwa har na kai na saba.

Ina zaune kan dadduma Ammy ta shigo,“yawwa kin sha maganin ashe ” shi ne abin da ta fara cewa.
Shiru na yi ina tunanin yaushe na sha magani amma ban tuna ba,amma tabbas da na tashi na ji bakina na zaƙin zuma.Na sake turo baki don kuwa tuni kwanyata ta hasaso min ina baccin ya bani magani.

“ Ammy ni yunwa nake ji” na faɗa kamar zan yi kuka,“ Sai ki je ki ci mana,ki taso ki kaiwa Daddy ƙarami abincinsa” ta faɗa tare da ficewa .Ina kukan sangarta na fita zuwa falo,cikin gunguni nake cewa Ammy “ duk ga ƴan aiki nan amma shine ba za su kai masa ba sai ni ”

Ta dube ni da mamaki kafin ta ce “ au! Dama can ƴan aiki ke kai masa abinci?”
Ba tare da na ce komai ba na nufi dianing na ɗauki ƙaton tray ɗin da aka jera komai nasa,na ɗauka tare da fita ina tafe ina turo baki har na isa sashen nasa dakyar na lalubo sallama can ƙasan maƙoshi na yi.

Bai amsa ba sai ɗagowa da yayi yana kallona kafin kuma ya mayar da dubansa kan system ɗinsa.Hakan yasa na ji haushi na ajiye tray kan table har na juya zan tafi na ji ya ce “ Naf!” na tsaya cak ba tare da na juyo ba ina jiran abin da zai ce sai kawai na ji tsayuwarsa a bayana.Da sauri na juyo muna fuskantar juna,idona tab tsoro nake kallon nasa da nake hango tsantsar ɓacin rai a cikinsu.

“ Ka yi haƙuri!” na faɗa murya na ɗan rawa.Bai ce komai ba ya kamo hannuna ya zauna da ni kan kujera,“ ki zuba abinci ki ci” shi ne abin da ya faɗa sam babu wasa a maganar sai ya je ya zauna ya ci gaba da aikinsa.


Ni kuwa kallo na soma ƙarewa kyakkyawar fuskarsa mai cike da yalwatacen saje da ɗan madaidaicin gemu,kan jajayen laɓansa na tsayar da ƙwayar idona waɗanda ke yin furucin da babu sauti da alamu wani abu yake karantawa.


Tamkar wacce aka yi wa dole haka na ƙanƙance ido ina karanta bakin nasa,na waro ido jin tamkar har da muryarsa ke yi min raɗa a kunne tana sanar da ni abin da yake cewa ɗin.
“ Ba ki ji abin da na ce ba?” ya jefo min tambayar,da sauri na mayar da hankali kan abincin haka na zuba na soma ci lokaci-lokaci ina satar kallonsa har na gama.

“ Kawo min wanda kika rage ɗin” ya faɗa ,sai na dubi plate ɗin yadda duk abincin ke cakule saboda miya da na zuba dayawa don ina son haka.
“ Uncle bari na zuba ma wani” na faɗa tare da ɗaukar wani sabon plate ɗin.
Ya ce “ wanda kika rage nake so”
Na ɗan ɓata fuska cike da kunya na ɗauka na kai masa,ya amsa ya ajiye shi kan system ɗin kafin ya soma ci hankali kwance .

“ Uncle wannan wane ne?” na tambaya ganin wani matashin soja baƙi an naɗe kansa da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login