Showing 24001 words to 27000 words out of 31350 words

Chapter 9 - FATALWAR DEBORAHBook Complete By Mrs Sadauki.txt

Advertisement

04 Mar 2025

4658

ta gama a gaban idona Grand Maa ta miƙawa wani yaro biscuit kafin su fice.
Bayan an gama cin abinci duk suka je suka jefar da abin take away ɗin a shara nan na ci gaba da yin cours ina aika kowane ɗalibi ya zo ya rubuta harafi ɗaya daga cikin ABCD ɗin da na yi musu.Ƙarfe sha biyu na rana cif aka kaɗa ƙarar rawar tashi ,nan aka zo fara ɗaukar yara ba ni na baro ajin ba sai da kowa ya watse .

A gajiye na shiga gidan,Inna A'i ta yi min Barka da zuwa na amsa ina mai rage kaya na shiga toilet.Bayan na yi wanka ta gabatar min da abinci,na saka plate ɗin gaba tare da ɗaukar waya na kira Ammy bayan mun gaisa cike da alfahari nake bata labarin yadda ranar farko ta kasance ,sai murmushi take kafin mu yi sallama ina gama cin abinci na ɓingire bacci wanda tamkar jirana ake aka ƙara yi min maimaicin duk abin da suka faru a yau ɗin tun daga lokacin da na je na yi tsaye gaban ajina har zuwa lokacin shan iska na yara.Yaron nan da Grand Maa ta baiwa biscuit na ga yana ta kuka yana kallona yana kiran “madam? Madam cikina ciwo! Madam mutuwa zan yi ,wayyo cikina” amma sam wai na kasa tashi daga kujerar da nake zaune,a gaban idona jini ya soma yi masa zuba ta ƙofofin hanci kafin kuma ya faɗi babu rai bayan yayi wata irin ƙara wacce daga nan na tashi daga baccin.


Na yi miƙa tare da duba agogo sai na ga tuni lokacin sallah yayi,kawai na miƙe na je na ɗauro alwala na gabatar da sallar.Sam ban wani bai wa mafarkin da na yi muhimmanci ba sai ma takarda da na ɗauka na soma rubuta abubuwan da zan koyar da su gobe,bayan nan kuma sai muka hau yin hira da Inna A'i lokaci lokaci kuma ina chating abina.


Ana kiran sallar magrib na tura wa Uncle saƙo kamar haka “barka da shan ruwa!”
Sai ya maido min da amsa da “ azumin da kika yi sanadin karewarsa?”
“Kamar ya?”
“Eh mana Naf ɗanɗanon yawunki ma kaɗai ya isa ya karya min azumi,uwa uba kuma tattausan ƙirjinki” da ya turo min saƙon nan na karanta shi ya fi sau goma,ina ta juya kalaman cikin tunanina ina jin tabbas Uncle nada buƙatar ganin likita don kuwa na sha jin ana cewa in mutum ya daɗe bai yi aure ba to hankalinsa na yin rauni .Da wannan na yi masa uzuri na ce kawai bai da lafiya ne kuma na yi alƙawarin zan sanar da Daddy a sama masa magani.



★Uncle Salem

Ikon Allah ne kawai ya kai shi gida lafiya,duk yadda azumin nasa ya zama gurgu hakan bai sa shi ya ajiye shi ba.Wanka kawai yayi ya ci gaba da yin abinsa har aka kira magrib ya ajiye shi,ya dawo daga sallah kenan ya tarar da saƙon Nafisa .Cikin son nuna mata fa eh haƙurin nasa ya ƙare yasa duk ya cire nauyi ya soma yi mata magana cikin wannan salon.Yayi jiran amsarta amma shuru,kawai sai ya kira Daddy ya sanar da shi ya kamata a fara shirin yin bikinsu da Nafisa amma sai Daddy ya ce ya je can gida su yi maganar ido da ido tun da tuni ya sanar da shi bai samu damar zuwa dajin ba.

Sai bayan sallar isha'i ya tafi can,a babban falo suka zauna Ammy ta kawo musu gasashen naman kaza da kuma shayi.Suna ci suna tuna baya, Uncle ne ya soma da cewa “ Abdul Hameed ka tuna lokacin da muna yara kai ne ke son gashen nama irin haka? ”
Daddy yayi murmushi ya ce “a lokacin ai tantabaru ne muke gasawa,sannan muna samari ne ba yara ba”
Uncle Salem yayi murmushi ya ce “ai kuwa dai ”
“Kamar sati nawa kake ganin ya kamata a sa ranar bikin?”

“Zuwa wata uku haka, lokacin an yi musu hutun makaranta a ranar da ta dawo sai a saka ta lalle” Uncle ya faɗa yana hasko tuni ga lokacin nan ya zo.

“To babu damuwa ,amma ka samu ka sanar da Nafisar komai?” Daddy ya tambaya.
“A'a tukuna dai amma ...” sai kuma ya ji nauyin abin zai ce kawai sai yayi shuru,shi ma Daddyn bai damu ba sai ma kiran Ammy da yayi ya sanar mata ,sosai ta nuna farin cikinta kafin ta fita.Bayan sun gama tattaunawa Uncle ya fito ya nufi flat ɗinsa,an gyara komai an share an goge.Wanka yayi ya shirya cikin bacci sannan ya soma yin wuridin da ya saba a kullum kafin kuma ya ɗauki wayarsa ya soma kallon hotunan Nafisa wanda a iya kallonsu kawai hankalinsa sai tashi yake yana jin buƙatar kasancewa da ita.


★ ƘWARGWAM

Yau ma ban ci abinci da dare ba kawai cake na ci da chocolat,sai na saka wasu a jakata wanda zan baiwa Firdausi kamar yadda na yi alƙawari.Ina yin kwance na ce “Innarmu don Allah ki yi min gatana irin ta dogon ƙarni mai abin tsoro”

“A'a Allah ya tsare ni Nafisa ,kin ga bacci ma zan yi don gobe ina son yi mana dambu tun da safe” ta faɗa tare da yin kwanciyarta gefe da ni.Na turo baki tare da lumshe ido,hoton abubuwan da Uncle yayi min duk suka dawo min.Sai wani abu nake ji yana bijiro min na shauƙi amma ban ma san taƙamaimai mene nake buƙata ba,amma sosai nake jin daɗin tunanin don abin da nake ji yana bani shauƙi sosai.Sai laɓana nake motsawa kamar wacce ke son Uncle ɗin ya ƙara shan su,a haka bacci ya ɗauke ni mai haɗe da mafarkinsa muna having sex.Yadda duk jikina ya amsa kamar a gaske yasa na buɗe idona dakyar da suka yi min nauyi,na duba lokaci a wayata sai na ga ƙarfe uku da minti uku na yunƙura na tashi zaune daidai nan hasken ɗakinmu ya ɗauke don dama ban iya bacci cikin duhu.Fitilar wayata na kunna sai dai tamkar wata wutar kyandir haka ta soma yin rawa kafin kuma ta ɗauke ɗif.Ban wani damu ba na sake ɗaukar wayar don sake kunnawa wannan karon cak screen ɗin ya ɗauka kafin kuma ta mutu da kanta.

Daga bakin ƙofa na hango wata mace mai fararen kaya a tsaye gashin kanta na tashi cikin iska.
“Wace ce?” na tambaya.
“Deborat” ta bani amsa kai tsaye,kafin kuma ƙyaftawar ido tsundum na ganta kusa da ni a zaune muna kallon juna.


Ido sune ƙofar hango ruhi, wannan yasa nake kallon ruhinta tun daga wajensa har cikinsa.“Ke ce kike yi min gatana kullum” na furta bayan na gama lalubo dukkan asalinta.Ba ta bani amsa ba sai jawo ni da ta yi ta kwantar ni kan cinyarta ta soma shafar sumar kaina,na lumshe ido don kuwa shafar irin dai ta matar da nake ji ce tana yi min haka duk dare.Sai dai wannan karon shafar ta babanta don tsintar kaina na yi a wani wurin, dube-dube na soma yi har na ci karo da allon sanarwa inda aka rubuta “DARASIN SANIN RUHANIYA” ina shiga ciki abun mamaki duk sai na tarar da kaf malaman nan da muka yi meeting da su,ga kuma su headmaster da principal su ma duk suna zaune yayin da Grand Maa ke koyar da karatu.Kamar wancan lokacin haka na zauna kusan Adama,na mayar da dukkan hankalina ga Grand Maa inda take cewa “kamar yadda vice headmaster ya faɗa muku lokacin meeting wannan school Ƙwargwam ta kasu kashi uku primary,da Sakandari sai kuma kuma Ajin Ƙwargwam wanda iya malamai ne kawai muke koyarwa” tana rufe bakinta na jefa mata tambaya,“Grand Maa me Ƙwargwam ke nufi?”

“Matsafa!” ta bani amsa kai tsaye,sai na yi shuru ina tunanin zuci na ce ‘Ƙwargwam school na nufin MAKARANTAR MATSAFA? to amma su wane ne matsafan?’

Tamkar Grand Maa ta shiga zuciyata kuwa sai ta bada amsa ta hanyar cewa “darasinmu na farko shine chapter ruhi da gangar jiki,ta wannan hanyar ce ake gane matsafi” tana gama faɗar haka sai ta yi wani abu da hannunta nan take sai ga wani table ya bayyana a gabanmu,sannan a samansa wani yaro ne kwance babu kaya jikinsa da na dubi yaron sai na ga ba kowa ne ba face ɗalibina wanda ta baiwa biscuit a ɗazu .....

My book is only 500 vi

2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank

DM +22795045822
[28/02 10:12] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️


```LoVe aNd HoRrOr story```👽


By
Chamsiya Laouali Rabo
{MRS SADAUKI💫✍️}

*SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta.


*FCWA*☀️

________________________


Last free page 10


Ganin Grand Maa ta ɗauki wuƙa za ta tsaga cikin yaron na yi saurin rumtse idona,ina jin sautin kururuwarsa yadda yake kuka yana cewa “madam ki cece ni kar ki bari su cutar da ni ” na buɗe idona da suka yi jawurrr na sake zuba su kan Grand Maa wacce ke zuba jinin yaron nan a kofi ta hanyar saka ludayi tana wani kwaso shi.
Bayan ta gama sai ta kai kofin bakinta ta sha sannan ta miƙawa principal shi kuma da ya sha ya bai wa headmaster daga nan sai vice principal da kuma vice headmaster.Grand Maa ta ƙara karɓar kofin ta ce “lamba ɗaya sha ka bai wa lamba biyu,haka za ku dinga yi har kowa ya sha” wanda aka kira da lamba ɗaya na duba, kyakkyawan saurayi ne irin sosai ɗin nan kuma sai na ga yana kama da headmaster da dukkan alamu ɗansa ne,bayan ya sha sai ya miƙawa lamba na biyu shi kuma ya miƙo min na karɓi kofin ina kallon yadda jinin ɗalibina yake kwance a ciki mugayen matsafan nan sun mayar da shi lemun sha .Na kai kofin kusan bakina na yi kamar na sha kafin na miƙawa Adama wacce ita kuma ita ce lamba huɗu,so nake na ce mata kar ta sha amma idon Grand Maa ƙurrr suke kanmu ina ji ina gani Adama ta sha jinin kafin ta ba na kusa da ita a haka har kowa ya sha aka mayar da kofin.

Daga nan sai Grand Maa ta yi wani siddabarun sai ga yaron da aka feɗe cikinsa ya tashi zaune daram da buɗaɗen ciki idonsa na shatatar da hawayen jini yana kallon tsakiyar idona har yanzu kuma bai gushe da neman taimakona ba sai dai sam ban san ya za a yi na taimake shi ɗin ba.



Wasu kwalabe ta jera saman table ɗin,ta yi wani alama da hannu a nan take duk suka buɗe kansu.Bakinta na furta ɗalasiman tsafi ta dinga umartar ruwan da ke cikin kowacce kwalba da su je su shiga buɗaɗen cikin yaron,nan ya soma yin wata irin zabura kamar an jona shi da lantarki abin da na kasa jura kenan na ce “ōvovār̃ī” hakan yana nufin komai ya tsaya wato stop cak duk komai ya tsaya kuwa yayin da dukkansu suka soma amayo jinin da suka sha suna wani waro ido kamar za su mutu.Sam ban wani damu ba sai ma zuwa da na yi na ɗauki ɗalibina ,kamar yadda uwa ke gudun matsala ta samu ga ɗanta ko kuma in ta ga wani abu zai cutar da shi take ɗauke shi tare da ɓoye shi haka na yi wa ɗalibina na ƙanƙame shi gam a ƙirjina ina kallon Grand Maa wacce ke yin ƙarfin hali tana cewa “lamba uku ki ajiye shi kar lokacin kaddamarwa ya wuce duk ki ɓata mana shiri ki maido mu baya”

Na girgiza mata kai na ce “ba zan bayar da ɗalibina ba”


“Lamba ɗaya je ka ƙwato min abin farauta” Grand Maa ta basa umarni ai kuwa sai ya miƙe tsaye ya tunkaro ni,muna kallon juna cikin ido sai na ga tamkar na san shi yana dab da kawowa wurina kuma sai na tuna a inda na san idon,wato tsakakar ranar nan ce da na bugewa bindi.Na dubi ƙafarsa sai na ga yana yin ɗingishi,“kār̃bās!” na furta nan take kuma ya ɓangwale ya faɗi yana ihu,nan kuwa na ga hankalin headmaster ya tashi ya nufo shi duk da kuwa ƙoƙarin tsayar da shi da Grand Maa ta yi don ba a so kowa ya gusa daga wurinsa sai da umarni.

Ta yo kaina za ta ƙwace shi da ƙarfi ni kuma da mugun sauri na bi ta rufin ɗakin na tashi sama cikin iska muka bar wurin.Ban san inda na ɓoye yaron ba amma tabbas na kuɓutar da shi kuma na basa tsaro,daidai nan kuma na tashi daga baccin saboda kiran sallar asubah da aka yi.


Dukkan cinyoyina na ji suna yi min ciwo kamar wacce ta yi wasar tsere,dukkan abubuwan da suka faru da ni kuma sai na manta da su .Wanka na yi tare da alwala na zo na yi sallah,bayan na gama na soma yin Azkhar ina lumshe ido alamun bacci ne yake son ƙara yin gaba da ni amma kiran Uncle Salem ya shigo wayata na je na ɗauka tare da yin kwance na kara wayar a kunne.
Yau shine ma ya gaishe ni da farko,na amsa cikin mayen bacci ina jin yana cewa “ mafarkin me kika yi Naf ?”
Baccin da nake ji ne ya sake ni a nan take tuna na yi mafarkinsa mun haɗa shimfiɗa da shi muna mu'amalar aure ,amma me yasa yake yi min tambayar nan shine abin dubawa .Cike da gyatse na ce “kai wane iri ka yi?”
Sai da ya saki murmushi kafin ya ce “mafarki na yi ga shi nan an kawo min ke gidana,muna kwance kan bed duk babu sutura a jikinmu ina yi miki zazzafan romance ke ma kina maido min da kuma na fara kusantarki sai kika fara yi min kuka kina kiran sunana Uncle Sal zafi ka bari ban so.Amma sai na soma rarrashinki har kika yi shuru kika bar kuka,Naf na ji daɗin mafarkin nan sosai kin ga yanzu ma da zan yi sallah sai da na yi wanka”

Tun da ya soma magana na rumtse ido,wato shi ko kunya bai ji yayi mafarkin suna sex da ƴarsa sannan har wani labari yake bani.Ina ƙoƙarin kashe kiran ya tsayar da ni,“ Please Naf kar ki kashe min kira faɗa min yau ma kin yi mafarkin tsoro?”

Jin ya canza akalar zancen yasa na yi shuru,sosai na tuna na yi mafarkin ban tsoro amma na kasa tuna abubuwan da suka faru.
“Faɗa min me kika gani?” ya sake faɗa .
Na ce “ni na manta komai”
“Kin sha maganinki kuwa kafin ki kwanta?” ya jefo min tambaya,ni sam na ma manta da ya bani magani.Na ce “eh a'a...”
“Baby ina ga ke ma kina son na zo kusa da ke shi yasa kike wasa da shan magani,amma babu damuwa duk weekend zan dinga zuwar miki” da sauri na ce “a'a ban so ka yi zamanka ”
“Saboda me? Naf me yasa kike son hana cikar burinmu ne ? Haƙurina ya ƙare fa ina buƙatar kulawa kin san abin da nake ji duk dare? Da zazzafan feeling ɗinki nake bacci ina tuna surar jikinki na matsu na ji komai na jikinki a hannuna yana sarrafa shi ...” kuka na saka masa ina roƙonsa don Allah ya bari ban son irin wannan zancen daga ƙarshe na ƙara da cewa “uncle ka je asibiti don Allah likita ya duba ka”
“Ke ce likitata domin ke kaɗai kike da maganin ciwona,kin ga yanzu ma duk kin tayar min da hankali ji nake...” ban bari ya ida ba na kashe kiran ina mai ci gaba da yin kuka.


Inna A'i wacce ta fito daga toilet ta ce “in kin gama kukan sai ki tashi ki yi sallah”
Na ɗaga kai na dube ta ina mamakin yadda aka yi ta canza min,na turo baki gaba na ce “Innarmu kin bar sona ” na faɗa ,ba ta kula ni ba ta haye dadduma.Ni ma tashi na yi na shiga toilet na yi wanka sannan na ɗauro alwala na zo na gabatar da sallah,ina Azkhar ina tuna mafarkin da na yi da Uncle Salem nan take kuma na soma jin jikina na saki har wani sanyi-sanyi nake ji yana rufe ni.Na je na ƙara haye katifa tare da jan bargo na rufa ina lumshe ido,karon farko da na ji ina muradin yin saurayi mu yi soyayya sannan aure ya biyo baya sai yayi min duk abin da Uncle ɗina yayi min cikin bacci.Da wannan tunanin bacci ya sake yin awon gaba da ni sai kuma na ci gaba da mafarkina daga inda na tsaya wato cikin wani daji na tsinci kaina.A gabana kuma wani ɗaki ne na kara,a bakin ƙofa wata tsohuwa ce zaune tana hura wuta amma ban ganin fuskarta.


Na matsa kusa da ita na ce “Kaka jiya na yi ajiya a wannan ɗakin cikin dare” ko kafin ta ɗago idona ya sauka kan ƙusumbinta.

Ta ɗago tana kallona,ganin mun san juna sai na sakar mata murmushi na ce “Kaka dama ke ce? Nan ne gidanki?” na faɗa ina nuna ɗakin.
Ta jinjina kai kafin ta ce “ki shiga ciki yana nan yana bacci amma kar ki tashe ”

Na shiga ɗakin sai na tarar da ɗalibina kwance bisan kunnuwan ganye yana bacci,fuskarsa kawai ake gani saboda yadda aka yi masa rufa da wata fatar dabba.

“Ya samu rauni sosai Allah yayi sa'a ma kin kawo shi nan kan lokaci da saura ƙiris ya rasa ransa” Kaka ta faɗa wacce ta shigo hannunta riƙe da ƙwayar sai tururi ke tashi.


Zama ta yi kusa da shi kafin ta yaye fatar,da sauri na kawar da kai ganin yadda ciwon nasa yake buɗe har yanzu.
“Ki matso ki soma ɗinke masa cikin ” ta faɗa .
Na juyo da sauri na ce “ni kuma?“
“Eh kin zata wa zai yi miki aikin?” ta faɗa tare da miƙo min wani mashi mai kamar wuƙa da kuma baƙin zare.
Jikina ne ya soma rawa haka na zauna ina kallon yadda ta ƙara wanke cikin nasa tare kuma da zuba wani magani,hannu na kyarma na soma ɗinki yayin da ita kuma take faɗar wasu surkullen da ita kaɗai ta san ma'anarsu a haka har na ida.


Na yi baya ina mayar da numfashi,ta tashi ta je can gaban wani babban teburi ta ɗauko min zuma ta bani na karɓa ina washe baki saboda ina son zuma kullum sai Uncle Salem ya bani ita tun ina ƴar yarinya.

Zumar na soma sha muna kallon juna ni da Kaka kafin ta ce “ban san dalilin Deborat ba da ta zaɓi ta ɓoye miki baiwarki,amma na so a ce kin zama tamkar Kakarki Ayodele ciwon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login