Showing 42001 words to 44930 words out of 44930 words
Chapter 15 - Yar Talakawa Complete Hausa Novels by Afrah.txt
takeji....
Su abba ma suka ce basu yarda ba, na hakikance ni sai sun aura min lateefa.
Da kyal suka yarda, akayi bikin mu da ita.
Watan mu daya na samu aikin soja, aka maidani lagos, kullum muna kan aiki ba hutu, lateefa kullum cikin complaining take.
har dai mahaifiyarta ta gano halin da muke ciki, tazo ta ringa daukar diyar ta suna yawon kasashe suna business dinsu...
Abun nan ya dame sosai, har su dad suka zo sukaji lbrn.
Ba karamin fushi sukayi dani ba.
Ana cikin haka, mukaje libya wani aiki, na kamu da ciwon zuciya da kidney failure. ..
Saboda tunani da yayi min yawa, da kuma rashin cin abinci.ga aikin karfi da muke.
An maido ni abuja wurin iyayena.
, abun haushin ma, su lateefa na kasar Cyprus lokacin.
An min treatment sosai, amma shiru rashin lafiya sai karuwa take, dan basu gano kidney dina bata da lafiya ba..
An kaini india, anan suka gane, har koda ta sai an cire.
, sun min kedney transplant, lateefa zuwan biyu kawai dubani, saboda yanzu idonta ya bude da manyan masu kudin da suke business dasu.
Mahaifiyarta ta zuga ta sosai, gashi lokacin tana dauke da cikina, ni banma saniba.
An maido ni gida nigeria,ina ta jinya, har wurin watanni biyar, na rame nayi baki, saboda yadda nake jin jiki.
Na dan fara samun sauki, dan iyayena na kula dani sosai, mami da mum suke jinya ta, lokacin zuby da zarah da faruk na makaranta.
Ba karamin haushin lateefa naji ba, ko zaman jinya ta batayi ba? Zuwa gaishe ni sau uku kawai tayi, wai tana da abunyi..
Ina wata na 9 da cinya, ta kawo yaro jinjiri ta bawa mai gadin mu, tare da letter
.
Abun nan ya bala'in bawa iyayena haushi, suka tsaya akan na bata takarda kawai, dan rashin imanin ta yayi yawa, aikuwa, na rubuta takarda aka bawa wani ya kai musu kadunan.
Mum da mami suka ci gaba da kulan min da amir, bayan dad yace aje ayi test a duba ko jini na ne.
Test ya nuna amir dana ne.
Bayan na samu sauki na koma bakin aikina.
Toh har yau da nake baki labarin nan bamu kara haduwa da lateefa ba..
◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇◇
Neena ta share hawayenta, ta rike hannun sa, insha Allah bazan taba gudun kaba my prince charming, ko wane irin ciwo kayi, ko wane irin aikin kakeyi, I will always be by ur side....
Prince ya mike ya zauna, ya rungume ta, yace I knw mrs na'im alkali, bazata iya kyamata ba, ko a wane irin hali nake zata kaunace ni.
Neena ta kada masa kai, ta kara matse shi a jikinta, ba karamin tausayawa amir da prince tayi ba, ta dauki alkawarin kula dasu har karshen rayuwar ta....
°•○●◇☆★ dedicated to my loving, _DIDI NEENAT_
[8/9, 7:22 PM] .: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*YAR*
🎃 *TALAKAWA* 🎃
By→afrah
Episodes→1⃣3⃣1⃣
→1⃣3⃣5⃣
Bayan sati biyu, su amir suka samu hutu.
Prince yazo weekend, suna falo suna kallo abunsu, amir ya juyo ya kalli papa dinsa, papa can we go for a vacation?
Neena ta kalli prince tana jiran taji mai zai ce, prince yace no son, ur momma wil start school, next week.
Amir ya shagwabe fuska,plss papa, ai zamu iya zuwa for 1 week, plss
Prince ya kalli neena, tayi saurin dauje idon ta daga kallon shi, yace okay okay zamuje....
Amir yace papa, lets go to Italy. ..
Neena taji gaban ta ya fadi, take ta tuna da mahaifin su daya barsu..
Prince yace yess son nice one, amir ya kawo hannu sukayi high five..
Prince ya nemi hutun sati daya..
Sunje gidan su umma da yayaB sun masu sallama, sannan sukaje wurin su mum da mami, sukayi musu suma, anan suka iske deeja da zarah, suka danyi fira sannan suka wuce.
Washegari, sadeeq da zuby suka zo suka kai su airport.
By 9 jirgin su ya tashi✈....
Sun isa Italy lafiya, prince ya sama musu hotel mai tsadar gaske...
Kwanan su biyu suna hutawar su a hotel din, suyi games dinsu har su gaji.
Yau sun shirya fita ganin gari, neena taci gayun ta, cikin English wears, riga three quarter sai wando skinny jeans. .tayi rolling gyelen ta, ta dauki gucci side bag dinta..
Prince da amir ne suka shiga cikin dakin, amir yace momma kinyi kyau.
Neena tayi murmushi, ta duko tayi masa peck a goshin sa...
Prince yace saura papa shima..ya miko mata bakinsa ya kulle ido....
Neena tayi murmushi, ta jawo hannun amir suka yi saurin ficewa daga dakin suna masa dariya..yana bude idon sa yaga sun gudu, yaya murmushi yace zamu hadu dake ne...
Sun sha yawo sosai ranar, sunyi pictures ba adadi...
Sunje wani side fast food restaurants.
Prince yace musu, ku jira ni a nan, ya shige cikin shop din..
Suna nan tsaye suna fira da amir..
Wani mutumi yazo shiga shop din, dai dai wurin su neena, ya dafe kirjin sa, sai ganin sa sukayi ya fadi a sume....
Neena ta rikice, tazo wurin sa tana bubbuga shi, mutumin da ganin sa dan nigeria ne...suna nan a wurin mutane sun zagaye su, prince ya fito daga shop din dauke da ledoji kuda biyu...
Yana ganin halin da ake ciki, neena tace my prince mu taimaka wa bawan Allahn nan, da gani sa kasar mu daya..
Please yadan tsaya na wasu minutes, sannan ya nemi taimakon wasu suka saka shi a taxi dinsu, suka tafi kai shi asibiti....
An musu bayanin cewa mutumin ya kamu da ciwon zuciya saboda tunanin da yayi masa yawa...
Sun tausayawa bawan Allahn sosai..
Suka shigo dakin da aka kwantar dashi..
Lokacin yama farka, ameer na basa labarin yadda momma dinsa da papa dinsa suka taimaka masa..
Suna shiga mutumin ya kurawa neena ido...
Sukayi masa sannu..
Ya amsa yayi musu godiya..
Prince ya shiga tambayarsa ko dan nigeria ne.
Yace kwarai daga nigeria yake..
Prince ya fada masa abunda likita ya fada musu.
Sai ganin shi sukayi yana kuka.
Prince da neena suka shiga lallashin sa.
Prince yace idan ba damuwa suna so su san maike damun sa.
Mutumin ya fada musu, yayi wani babban kurkure ne a rayuwar sa, yanzu abun ya dame sa amma yasan wadan da yayiwa da wuya su yafe masa.
Sun tausaya masa sosai.
Prince yace kada ya damu, zasu taimaka masa da addu'a amma yaje ya nemi gafarar mutanen nan.
Ya amsa da toh, inshaAllah cikin satin nan zai koma nigeria.
Prince ya amsa card dinsa, shima ya amsa na prince din.
sannan suka masa sallama suka tafi..shidai sai kallon neena yakeyi, itama sai kallon sa takeyi.
Sun sha hutun su, cikin jin dadi, sun yo wa yan'uwa tsaraba sosai.
Ranar da suka dawo,gidan su mum suka sauka, sai farin ciki sukeyi, kowa yazo gida ana ta fira da barkwanci.
Sai dare dukka yaron suka yiwa iyayen su sallama suka tafi gidajen su.
☆☆☆☆☆★★★★★★☆☆☆☆☆
Bayan shekara biyu...
Neena na gani za'a shiga da ita dakin haihuwa, mum, mami, umma, yayab, zuby da wata yar baby a hannunta, sai zarah da tsohon ciki, deejah da intee dinta, suna ta zarya a bakin labour room din...
Faruk da sadeeq suka shigo, suka tsaya wurin mami suna tambayrta ko an haihu lafiya, mami tace tukunna dai...
Prince duk ya rikice, yana kan jirgi dan zuwa ganin yanayin da matarsa ke ciki, sai kiran su faruk yakeyi....
Ya sauka daga jirgi, yazo daukar mai taxi, dan ba wanda yazo daukarsa..
Wata katowar mota ta tsaya a gaban sa...
Aka sauke mirror, prince na kallon cikin motar yaga wannan mutumin da suka hadu a Italy, mutumin ya sakar masa murmushi, yace shigo mana Na'im...
Prince ya shiga shima yana murmushi..
Mutumin yace, naji dadin kara haduwa dakai, dama a abuja kuke ne? Prince yace eh, yanzu ma matata na asibiti zata haihu...
Mutumin yace Allah ya sauke ta lafiya, nima nazo neman mahaifiyata ne, da kuma yan'uwana...
Prince yace Allah sarki, Allah yasa ka gansu toh, mutumin yace amin, muje na kai ka asibitin a ina ne?
Prince yace a maitama ne.
Ya ajiye prince a bakin gate, suka yi sallama, prince ya basa address dinsa.
Prince na cikin buga sauri dan zuwa wurin matarsa...
Sukaci karo da *Lateefa* wani irin burki suka ci a tare...
Lateefa na ganin sa ta zube a kasa...
Ta saki wani irin kuka, wanda suke tare yace, lateefa lafiya, lateefa ta rike hannun sa, hafiz hafiz, wannan shine Prince shine na'im, din da muke nema....
Hafiz ya kalli prince, yace na'im ka taimaka ka yafewa matata, I know she did wrong u, pls ka yafe mata...
Lateefa dake kuka kamar ranta zai fita, tace prince, ka yafe min ka yafe min nasan banyi daidai ba, ka yafe min ko Allah zaisa na sake ganin tsatso na.....
Prince ya tsaya tsak yana kallon ta, ya kalli hafiz, yanzu ina cikin sauri ne, matata na labour room...
Hafiz ya rike hannunsa, yace pls abokina...
Prince ya sauke ajiyar zuciya, na yafe miki lateefa, amma ki nemi yafiyar danki shima...
Ta mike da sauri, tace ina yake yanzu.
Prince yace ga address dinmu, kuzo gobe inshaAllah....yaya saurin tafiya, har yana hadawa da gudu.....
Neena ta haifi diyarta mace, kyakkyawa sosai, kamar su daya da prince....
Sun koma gidan su mum.
Dad da abba na falo suna fira da yayab da umma dasu mum da mami, faruk ya shigo ya sanar musu sunyi bako..
Abba yace shigo dashi mana...
Faruk ya fita ya shigo da bakon...
Gaba dayan su suka mike..
Yayab tace almustafa kai neh!!!!??
Almustafa ya iso gaban su ita da umma ya shiga neman gafarar su...
Ansha kuka, kafin nan aka yafe wa juna...mum tace bari a kira yaran ku gaisa ..
Taje dakin da neena ke jego, ta kirasu duka..
Suna zuwa neena tayi ta mamakin ganin mutumin da suka taimakawa..
Prince da safeeq suka shigo suma..
Shima prince yayi mamakin ganin mutumin...
An dai aka sanar dasu ko waye...
Neena da sadeeq, suna hawaye sukaje suka rungume baban su...
Sai sallamar su lateefa sukaji...
Gaba daya falon anji mamakin ganin ta, ta duga gaban su dad ta basu hakuri...
Hakama mu mum da mami...
Kowa ya yafe mata, yayaB ta nuna mata neena tace ga matar na'im...
Suka kalli juna, lateefa tayi mata murmushi...
Sai ga faruk ya shigo da amir...
Lateefa na ganinsa tayi gunsa ta rungume sa,....
Ya kalli neena yace who is she momma. ...
Neena tace shes ur momma also..
Amir yayi murmushi, lateefa tayi ta kallon yaron, tana sumbatar sa...
Sai da sukayi mangariba sannan suka tafi, mijin lateefa yace idan ba damuwa, suna so amir ya ringa zuwa musu hutu kaduna...
Prince yace ba damuwa, sukayi exchange din contacts, ya raka su har gate suka tafi....
Sai mun hadu anjima dan jin karshen yar talakawa
°•○●◇☆★ dedicated to my loving, _DIDI NEENAT_
[8/9, 7:22 PM] .: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*YAR*
*TALAKAWA*
*FINAL* *episode*→1⃣3⃣6⃣
To
1⃣4⃣0⃣
Ansha suna, an sawa baby suna aysha, amma zasu ringa kiranta hanan.
Zubaida ta haihu ta samu yaro namiji ahmad suna kiransa Ayman.
Zarah na dauke da tsohon ciki...
Baban su neena almustafa, ya kara gyara gidan sadeeq kuma ya dawo da kasuwancin sa nigeria, ya saka sadeeq a matsayin CEO, ya sai wa neena mota har biyu, sannan ya sake musu kayan daki dukkan su harda su zarah da zuby dama deeja.
♥♥♥♥♥♥♥♥♥♥
Bayan shekaru ashirin.......
Na sake cin gayu na naje dan kara samo wa masoyana rahoto..
Wani handsome sarauyi na gani yana saukowa daga jirgi....
Na goge idanuna...like seriously wannan Amir ne....
Oh my G, ya girma ya zama cikakken saurayi.....
Ya amir ya amir! Over here brother. .....
Wasu pretty flowers na hango, babbar su yar shekaru 22(intee), sai mai binta mai kimanin shekaru 20 (hanan) sai dayar mai shekaru 19 (diyar zarah mai suna salma)
Gaba dayansu sunci gayun su cikin black arabian abaya...
Ameer ya karaso wurin su yana murmushi...
Hanan tayi tsalle ta rungume shi, ya manna mata kiss a kumatu...
Babbar ta cire sun glasses dinta, tace welcome back brother, amir ya kura mata ido, d little intee...ta shagwabe fuska brother kai koh...
Karamar su ta juya masa baya tana kumbure kumbure...
Ameer ya kallo ta Oh Oh, matar ya akayi ne?
Salma tana dariya yeeh. Welcome brother ta rungume sa itama, intee tadan buge ta oh wasa ma kike yi da brother ko? Sukayi dariya duka..
Ameer yace gals lets get going na kagara naga momma dina....
Sun isa babban gidan su dad da abba da suka canza.
Kowa da kowa na gidan lokacin ana jiran babban jika ya dawo..
Neena na hango sanye da riga gown ta yafa babban gyele a jikinta sanye da glasses. ..sai faman girke girke takeyiwa danta...
Prince ne ya shigo kitchen din ya dan manyanta daka ganshi kaga tsohon soja....
Yazo yayi bag hugging neena, wat is mrs na'im alkali still doing? Neena tayi murmushi ta juyo tana kallon shi, my prince charming, ta manna masa kiss. ina ka shige ne yau? Yayi murmushi ina tare da Aiman a garden....
Neena tace nidai kun maida ni maman maza, anty zuby ta kwace hanan...
Prince yace oh yes, kina da yaro lawyer, ga kuma Aiman soja....
Neena tayi dariya prince ya janyota jikinsa, yakamata muyiwa hanan sister fa...
Neena takai masa dukan wasa, shiiiiish a kicin muke...
Prince yayi dariya.....shigowar yayab sukaji, tana cewa ni faruk da sadeeq zasu hadewa kai, har zubaida da deeja zasu shige wa mazan su...
Nima inada jikata ai, neena neeena, prince ya shige bayan kofa, toh matar nan uwar surutu zata shigo....
Neena tayi dariya....
Babansu neena da umma, mum da mami, dad da abba duka suna falo suna firan su.....
Aiman ya shigo cikin murna, grannies guess what?
Mum tace Amir is back?
Aiman yayi dariya oh yes, my big bro is back yahau tsalle, zubaida tana saukowa kasa falon tace maza ka fadi....
Amir ne ya shigo falon tare da yan'matan...
Yayi wurin zuby ya rungume ta aunty, ta shafa kansa, our amir congrats an gama karatu..
Yayi murmushi ya karasa wurin kakanninsa, ya shiga rungumar su suna sa masa albarka...
Ya tsaya tsakiyar falon, ya rike kugun sa ya kalli nan ya kalli can...
Ina dr ? Where's my momma, our dr....?
Neena ta fito daga kitchen din cikin sauri, my son an dawo, amir na korarin rungume ta, yayaB ta shige tsakani....
Ta rungume amir tana washe baki...
Sannu da dawowa dan albarka....
Amir yace granyB mun same ku lafiya...?
Ya janye jikinsa ya rungume neena, ta shafa kansa....my son Allah yayi maka albarka..
Prince ya fito shima, amir ya karasa ya rungume sa...
Deeja da zarah suka shigo gidan suma, tare da faruk da sadeeq, amir gaba daya cikin farin ciki yake....
Yayi wanka ya fito ya iske kowa da kowa ana fira, intee ta mike da sauri ta kawo masa abincinsa...
Salma ta mike itama ta kawo masa juice. ..
Hanan ta kalli aiman sukayi dariyar gulma...
Suna cikin firan su akayi sallama, mummy tare da ikram...
Mum, mami, neena, zuby, zarah, faruk, deeja, dad, abba, yayab suka mike...
Mummy ta karaso cikin falon...
Ikram taje gaban prince ta duka har kasa ta nemi yafiyar sa, neena tazo ta mikar da ita tace mijina ya yafe miki ikram....
Duka falon sukayi murmushi. hanan, intee, da salma suka ringa damun amir, brother who's she?
Ameer yace ur auntie. ..
Sallama aka kara yi....lateefa da mijin ta hafiz, tare da diyarta minal suka shigo...
Duka yaran sukayi gunta suka rungume ta....
Ameer ya rike hannun minal, ta rungume sa itama tace welcome brother, dad yace woo ameer kai kam kannen ka har sunyi yawa...
Gaba daya falon suka kwashe da dariya....
Nima Afrah na murmusa....
Sannan na bawa phone dina hot kiss, thanks for all your hard work durling...😘
♡♡♡♡♡♡♡♡♥♥♥
Love u all yar talakawa fans...
I love u all habibaties muah muah😘😘.
*About d story*→ dis labari is just an imagination/frictional, nina zauna na kirkire shi, just to entertain my readers. ...I hope u will forgive me idan na bata muku a rashin sani.
°•○●◇☆★★°•○●◇☆★°•○●☆★
*Godiya*
♥A gareku masoyan novels dina
♥Godiya gare ki _DIDI NEENAT_
♥ nagode my lovely chingos, afrah n ayeesh, my sweetsis, khadija chafe, my habibty Munay, my love anty jamila muhammad ali lov u all😘