Showing 126001 words to 129000 words out of 155423 words

Chapter 43 - A GARIN MU Book Compelet BY HAERMEEBRAERH.docx

17 Oct 2025

279

mai yawa mai albarka...Allah ya karbi ibadun mu...ina nan ina jiran barka da sallah na😃❤️*

PAGE 56:

Mubaraka dai na zaune a mota, har wannan lokacin ba ta daina sharar hawaye ba, hawayen da ke zubo mata daga can qasan zuciyar ta ya ke tahowa, rayuwar da suke ciki bata da suna, balle fassara, ina ma ina ma su na da iyaye na gari? Lallai da ba wanda zai fi su jin dad'in rayuwa ,amma inaaa, rayuwa na ta gara su, duk inda ta kad'a can take kai su, su kuwa bin ta suke a koda yaushe.

Hanyar da ya ke shiga sabon waje ne a wajen Mubaraka , Ita dai nata ido, bata ce komai ba, har suka tsaya a wani madaidaicin gida.

Fita ya yi, ya zagaya ya bude mata qofar, sannan ya kama hannayen ta biyu, ya tsaida ita a gaban shi, fuskar ta ya d'aga ya na kallon cikin kwayar idanun ta, hawaye ya gani kwance su na rige rigen fitowa, wani abu me zafi da rad'ad'i ya ji a zuciyar shi ya na dukan shi , cikin kad'a kan shi ya ce,

"Ya isa haka nan, daga yau in shaa Allahu ba ki koma yin kuka Barakana, indai su ba za su so mu kamar kowanne iyaye ba, na maki alqawalin zan so ki kamar yanda iyaye nagari ke son d'iyan su, zan so ki kamar yanda yaya nagari yake son qaunar shi, Barakana duk abinda ki ke so na zamo miki ni Lawwali na maki alqawalin zama shi, abu guda ni ka so wajen ki, shi na ki dena kuka, ban san ya zan fahimtar da ke kukan ki ke yi min ga zucciya ba,"

Kwantar da kan ta ta yi a qirjin shi, ta qanqame shi, ta na jin dikkan soyayyar da ya lissafa na shigar ta, tabbas Lawwali babbar katanga ce a rayuwar ta, bata fatan abinda zai raba ta da shi duk duniya, za ta yi ko mene ne da bai sabawa Allah ba dan ganin ta tabbata tare da shi cikin farin ciki.

Kama hannun ta ya yi, suka shiga ciki, yaran oga na ganin shi suka hau fara'a, domin tun kan ya zo ya sanar da kowa shirin shi, ya kuma yi wa kowannen su alkhairi, No 1 aka kira ya fito, gaba daya Mubaraka bata gane shi ba, dan kuwa ya zama gurgu, ya daku matuqa, ya azabtu, duk jikin shi ya nuna alamar wahala da gajiya da azabtuwa.

Godiya ya yi wa Lawwali da ya kauda kai daga ganin shi, ba dan alqawarin da ya yi na dena kisa ba, tabbas da No 1 ba zai bar wajen nan da rai ba, amma ko gurgantakar da ya samu a qafar shi ta hagu ta ishe shi tuna abinda ya aikata har qarshen rayuwar shi.

Kallon da ya kure Mubaraka da shi ne ya sa ta gane ko wane ne, ai kuwa da sauri ta labe a bayan Lawwali, Lawwali kuwa a harzuqe ya kai masa shaqa,

"Shin kallon mi ka kai mata? Ba ka tahiya sai na sauya ra'ayi na na sa harsashin bindiga na hwashe ma kai?"

Da sauri Mubaraka ta riqe hannun shi, amma har a wannan lokacin bata fito sosai inda No 1 zai gan ta ba, ta na labe a bayan Lawwali, hakan ke baqanta ran Lawwalin, No 1 kuwa zubewa ya yi a guiwowin shi duka biyun, ya duqar da kan shi,sai da mubaraka ta saki qara ta yi baya ta sake qanqame Lawwali.

Hakuri No 1 ya fara bata, cikin wata iriyar murya mai son yin kuka, Lawwali ne ya janyo Mubaraka gaban No 1 ya ce,

"Sanya ijiyar (idon) ki cikin na shi, ki gan shi a qasqance a qasa a gaban ki,ba shi iya miki komai wallah, in har baki dena jin tsoro nai ba zan kashe shi yanzun nan, dan ba zan bar abinda ki ke tsoro ya ci gaba da yawo a doron qasa ba"

A hankali ta fara jin tsoron No 1 na barin jikin ta, ko dan kar a kashe shi, dole ta ware, sai da Lawwali ya ga Mubaraka ta daina kyarmar da take sannan ya sa aka tusa qeyar No 1 ko na mota ba wanda ya bashi, ya na ji ya na gani aka rufe gidan,aka bawa Lawwali key, suka shige motocin su suka bar shi a wajen.

Su Lawwali basu tsaya a ko ina ba sai asibiti.

"Yah Auwal waye ba lafiya?"

"Mu tai ki na ganin ko waye"

Asibiti ne na hamsaqai, riqaqqun masu abun hannu, Mubaraka sai kalle kalle take, sai da Lawwali ya samo dakin da za su, ya ja hannun ta suka tafi, 'yan sanda ne guda biyu a bakin qofar dakin, su na tsaron wajen, Lawwali bayani ya musu da cewa shi surukin mara lafiyar ne, sannan suka barshi ya shiga.

Hajiya Ikee na ganin shi ta tafi da sauri cikin kuka ta tsugunna a gaban shi,

"Dan Allah Lawwali ka yi hankuri, ka yahe muna, ka tausaya wa halin da Daddyn Sultan ke ciki, ba shi iya magana, qafar shi ta shanye, hannun shi guda ba shi motsi, gashi har yanzu damuwa bata bar shi ba, rashin ganin yaran shi na damun rayuwar shi,duk daren duniya da ihu, da kururuwa muke kwana, kamar ya na ganin wani abu, gashi ba shi magana balle mu gane me ya ke gani, "

Dariya Lawwali ya yi sannan ya ce,

"Me zai gani ko banda aljannun da ya ke wa tsafi? Bai basu jinin bil'adama ba kwana biyu, ba dole su biyo sahu ba? In ba ku je aka rushe dakin da ya gina ya na tsahi cikin shi ba,kuma baku yi wa aljannu sadaka ba walle yana cikin tashin hankali, kad'an ya fara gani"

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, yanzu ya za mu yi?"

"Ina nissani? Na so gobe yaran ku su zo ganin ku, Sultan ya dawo gare ku, amma 'yar ku ta lalata shirin, ta ci amana ta, ta qone duk wata shaida da zan hannintawa hukuma, dan mu karbi hukuncin mu daidai da abinda muka aikata, amma ta qone su, dan haka ba za su dawo yanzu ba,"

Kuka Hajiya Ikee ta fashe da shi ta ce,

"Yau na shiga uku ni Ikileema, ina zan sa rayuwa ta? Yanzu Lawwali ba wata alfarma da zaka yi muna mu gan su?ka duba halin da Daddyn Sultan ke ciki"

Dariya Lawwali ya yi, sanda ya kalli yanda Excellency ke dalalar da yawu, ya kasa magana sai hawaye.

"Ke walle wanga aljannu ka damun shi ba kewar d'iya nai ba, in ku na neman maganin aljannu ku nema, sai an jima"(ke wannan aljanu ke damun shi ba kewar yaran shi ba, in zaku nemi maganin aljanu ku nema se an jima)

Mubaraka ce ta ce,

"Hajiya ki gafarce ni, ni qarama ce, amma ina mai baku shawara, da ku nemo mallammai na kwarai,wanda sunka san Allah, su yi addu'a aljannun su tafi, amma in kuka yi musu yanka, za su dawo su ce wani abu suke so, ko rayuwar wani a cikin ku, Allah shi kiyaye"

Ai Hajiya ikee na jin rayuwar wani a cikin su, ta tsure, kallon Gwamna Halliru ta yi, ta ce,

"Mu na zaman zaman mu da rufin asirin mu ka doko muna siyasa, gashi nan, mu na ganin ibtila'in rayuwa, ba mulkin, ba dukiyar, ba d'iyan mu, ga wani tashin hankalin yanda za mu rabu da aljanun da ka jajibo muna"

Lawwali kam dariya kawai yake kamar wani wawa, cikin surutai da sambatu suka bar Hajiya Ikee, Gwamna Halliru kuwa na kwaranyar da hawaye ta gefen ido.

Sai da suka tsaya Lawwali ya yi siyayya ta kayan kwalama, da duk wani abu da ya san Mubaraka na so, har zai fita daga wajen shopping din bai sai wa Sultana komai ba, sai ya ji ya kasa tafiya, komawa ciki ya yi, ya daukar mata best chocolate din ta, da candy din da ta fi so, sannan ya ga wani turare mai kyau na mata, daukar mata ya yi, ya na murmushi.

Sai da ya biya kudin komai, sanan ya koma mota, Mubaraka na nan zaune, ta na ta tunanin yanda za ta sanya Lawwali ya bar Su sultana Su je su ga iyayen su, Hajiya Ikee ta matuqar bata tausayi.

Ajiye mata ledojin ya yi a cinyar ta, ya koma mazaunin driver ya zauna.

"Barakana ga naki nan, wancan na Sultyna ne, ki bata amma kar ki ce ni ne na bayar a bata,"

"Yah Auwal kenan, ana soooo ana kaiwa kassuwaaa"

Dariya suka yi, sannan ya tada motar dan komawa gida.

Mubaraka ta matsu su koma, dan basu yi sallar azahar ba, ga la'asar ta Kunno Kai.

************************

Hajiyan Hansatu ce ta kira Hansatu, ta ke tambayar ta, tunda Isah ya tafi sun yi waya kuwa? Saboda yau sati d'aya da kwana uku ba labarin Isah ko ta ina, layin shi tun ya na shiga ba a dagawa, yanzu ya ma dena shiga.

Hansatu ta rasa amsar da za ta ba Hajiya, kawai sai ta ce,

"Shi na lahiya qalou Hajiya, kar ki damu, in mun kai waya zan sanar masa ki na so ku gaisa"

"Ahhh ahh basshi d'ai, dama son nikai na ji lahiya shike ko ah ah"

"Shi na lahiya lumui Hajiya, ina Yayah Musa? Shin aunty bata dawo ba har yanzu?"

"Shekaran jiya dai Yayan ki ya aika musu da takardar saki, ya ce ya gaji da iskancin ta,na so na hana shi, na kira na mata magana, ta inda take shiga ba ta nan taka hita ba, wai na bi na qanqame d'a na, na hana su sakewa, ban barin shi ya je wajen ta, ke ki ji hwa?"

"Kayyaa ban ji dad'in rabuwar su ba, Allah shi sa hakan shi ne ya hi alkhairi"

"Ameen, ina wannan me gidan da bai iya cehwane ba?"

"Shi na lahiya, ya ce zai siyo maki haqorin roba ki laqa, tunda na ki ya hwara tsuhwa"

Dariya Hajiya ta yi, suka ci gaba da hira cikin nishadi, ita da yar ta

************************

A kurkuku kuwa, Isah.............

*Sai anjima Inshaa Allahu*

💅🏻 *A GARIN MU* 💅🏻

BY HAERMEEBRAERH

PAGE 57:

Isah na can an miqa shi wajen kuliya manta sabo, ba irin bayani da Isah bai yi ba,amma abu ya ci tura, duk iya bincike da shaidu sun nuna koken ta Isah ce,dan haka nan take aka yanke masa hukuncin shekara goma a gidan maza da horo mai tsanani,dan kuwa Saudiya ba kamar Nigeria  bace, ba su b'ata lokaci wajen yanke wa duk wani mai laifi hukunci, Isah ya yi kuka, ya yi kuka, ya godewa Allah, ba irin yunquri da bai ba na a bashi dama ya kira gida ba wanda ya bi ta kan shi, haka aka ingiza qeyar shi zuwa kurkuku.

Duk da cewa kurkukun su ba irin namu bane, mai cike da datti,qazanta da rashin abubuwan da mutum zai buqata, amma kurkuku kurkuku ne, Isah ya yi dana sanin zuwan shi Makka, ya yi dana sanin sanin sana'ar saida goro a rayuwar shi.

Tun ya na kuka da qarfi, ya koma yin na zuci, sai dai hawaye da ke kwaranya kamar an bude magudanar ruwa, rayuwar shi tun daga yarinta ya ke tunawa, shi dai gaba d'aya bai da sa'a a rayuwa, bai rabu da iyaye lafiya ba, ga iyalin shi ya baro su na fushi da shi, bai kyautata alaqa da su ba balle su neme shi, yanzu da ace a baya ya na kiran Hansatu da ya zo,ya san da ta ji shi shiru dole za ta neme shi,

"Kaico na, kaicon rayuwa ta ni Isah, yanzu ina zan saka rayuwa ta na ji dad'i, shekara goma ba kwana goma bane ba fa,"

(A haka Isah ya samu rangwame ne, domin kuwa wasu hukuncin kisa ake yanke musu a Saudiya, indai aka kama mutum da miyagun kwayoyi, wasu shekara biyu da bulalai, wasu goma da bulalai)

A ranar ko abinci Isah bai iya kaiwa bakin shi ba, duk ya fad'a ya yi zuru-zuru kamar ya yi shekaru a wajen.

A can gida Nigeria kuwa Hansatu ta d'auki shawarar Hajiyan ta, sun saka yaran a makarantar kud'i, driver guda Yaya Musa ya sama musu da mota, ya je ya kai su, in an tashi ya maida su gida.

Da yamma kuma Hansatu da kan ta za ta raka su Islamiyya, ta kuma gargad'e su kar su kuskura su koma gida ba tare da ta je daukan su ba, su zauna wajen Baba me gadin makarantar har ta je.

A cikin gida kuma ta kama sana'ar had'a sabulan gyaran jiki, dan kuwa ta kware sosai a haɗawa, jikin ta ya yi luwai luwai kamar matar wani hamshaqin.

Ta na yin sabulun tumeric

Sabulun water melon

Sabulun hinna

Sabulun carrot da

Sabulun cucumber.

Sai man kitso mai kyau da gyaran gashi, ta dage sosai wajen bunqasa sana'ar ta, da inganta ta, ta yanda kowa ya gani zai sha'awa, in mutum ya siya ya yi amfani da su, sai ya koma, kafin wani qanqanin lokaci Hansatu ta fara shiga gari itama,ta maida wa yaran ta da sana'ar ta hankali,lokuta da dama, in ba wani abu ne ya faru ba, mantawa take da Isah, ita kan ta ta na mamakin yanda a lokaci daya ya fita a ran ta.

(Duk Mai son man kitso Mai Sanya gashi tsaho da santsi da maganin amosalin Kai da karyewar gashi, ko Kuma Mai son sabulu Mai kyau da zai gyara wa mace fata ta yi kyau da sheqi, ko body scrub ko body oil ta nemi wannan No 09031416423...HAMIBRAH PRODUCTS sune na d'aya wajen maida TSOHUWA YARINYA )

(Haka lamarin yake, duk sanda aka samu namiji azababbe, da ya addabi iyalin shi da mugun hali da d'abi'a, to za a wayi gari duk wata soyayya, biyayya, da tsoron shi da iyalin ke ji ta kau, qiyayya mai qarfi da rashin jin qai za su maye gurbin soyayyar da aka masa a baya, haka in mace ce da bata iya magana ba, kuma bata da kyakkyawan hali da d'abi'a, a hankali take fita a ran miji, duk kauda kan da yake akan ta, kuma da ya fito mata da halayyar shi ta musguna wa shima, sai ka ji mace na fad'in mugu ne, ba shi da dad'in zama)

In sun samu lokaci da weekend sukan kai wa Hajiya ziyara, watarana kuma Hajiya da kan ta take zuwa,su gaisa.

Bayan Hansatu ta tura yaran ta makarantar boko ne, ta yi wanka, ta shirya cikin wani yadi mai kyau, da tsada, Hajiya ce ta musu anko har su Ameenatu, kulle gidan ta yi, ta fad'a na maqotan ta, wato 'Yabbuga, bakin ta dauke da sallama ta shiga.

Shiru ta ji ba wanda ya amsa,

"Shin mutanen gidan ga su na nan kuwa?"

Cikin wata iriyar murya, kamar an shaqe mutum, ko kuma mutum na cin abinci, haka ta ji an amsa mata da,

"Ko ni shigo ciki,na amsa"

Qarasawa ta yi, dan ta san masifar 'Yabbuga, ko ba abinda akai, ta na iya b'ata rai, ta na amsa wa mutum magana d'aya d'aya.

Hansatu ce ta ja ta tsaya, tare da rafka salati,

"Waggaa, mi ya faru hakan  na gankin  huska ta qabe (kumbura) me ya kwashe maki huska? Shin gobara ta kun ka yi ban sani ba? Ko hatsarin mota?"

Wata harara 'Yabbuga ta samu da kyar ta wurgawa Hansatu, sannan ta lashe dan saman bakin ta da ya haye, ya yi sintim, zama Hansatu ta yi a gefen 'Yabbuga, ta nata watsawa'Yabbugan tambaya, dan ta na son sanin me ya faru da ita, ta ga guiwar ta d'aya a dauje, ga gefen fuskar ta ya dauje shima, baki ya haye, 'Yabbuga dai bata kula ta ba, sai ma wani tuquqin baqin ciki da ke taso mata a rai da take ji, wai me ma ya kawo Hansatu gidan a irin wannan yanayin?

Sallamar Dan Jumma ce ta karad'e tsakar gidan, Dan Jumma da Hansatu sun gaisa ta masa ya me jiki ya amsa, tare da fad'in,

"Jiki dai ga shi nan, mai shi na jin shi,tunda kin gane ta nan, ta dai girme ki, amma kin hita hankali, da sanin ciwon kai, ta je jidali(fad'a) , can gidan Dan Talo, sun ka liqa mata mugun kashi"

A hasale 'Yabbuga ta kalle shi da kumburarran baki, ta ce,

"Wai shin uban wa yacce kashi an ka ban? Wacce ma kashi an ka ban eyee?"

"Tau sanda kin ka yi aniyar tahiya yin hwada(fad'a) akan atanhwar (atampa) da ko dubu uku ba a siye ta ba ban hana miki zuwa ba? Nan nan na dinga baki hankuri, zaman tare ba a haka nan, kema su na kyautata maki, kin ka ce ba ki iya hankuri sai sun biya, ki ka tai, kuma ki ka dawo a haka, bani cewa liqa miki kashin wahala an ka yi?"

"Banga wahala ba, sai dai ka gan ta nan bisa kan ka, ba wadda ta isa liqa min kashin wahala duk shiyyar nan balle gidan Dan Talo, bai auri matar da zata liqan kashi  ba, nace bai auri matar da zata ban kashi ba,"

"To in ba kashi sun ka baki ba mi na na ya hwaru?"

Cikin bata rai ta labarta musu duk abinda ya faru, Hansatu da Dan Jummaa kasa riqe dariyar su suka yi, sai da suka dara sosai, sannan Dan Jummaa ya ce,

"Ko da na ji, ashe ke da giinaa (gini) kin kai hwada tak-kashe ki qas, (ashe ke da gini ki kai fada ta kayar da ke qasa) kuma ke da d'an ki menene na gudu har da haure gini? Inda kin samu karaya hwa?"

"Walle gwanda na samu karaya a gini, da ace yaron nan mai baqar zucciya ya kammin, na zama abar kwatance ga shiyya,iyayen shi ma ba barin su ya yi ba balle ni"

Dariya kam ranar Hansatu ta yi ta har da hawaye, daga qarshe ta zari dubu daya ta bawa 'Yabbuga ta ce ta sai madara, dan kuwa bata ga ta inda abinci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login