Showing 39001 words to 42000 words out of 44363 words
Chapter 14 - YAR GIDAN TSOHOWA Docment Complete Book .txt
saurin ture plate d'in tuwon dake gabansa ya fad'i K'asa
Gaba d'aya abinci ya zube k'asa duk ya b'ata masa jiki,
K'afarsa ya rik'e yana fad'in wash k'afata."
Hankalin kowa ya koma kansa anayi masa sannu,
Kuma marairacewa yayi yana fad'in "wash mommy k'afata, da sauri Abba ya shiga diba masa k'afar Wanda ba wani abu da yakeji gareta."
Sai da ya ga ya d'auke hankalin su gaba d'aya zuwa gareshi.
Sun mnta da maganar dijama snn ya sauke ajiyar zuciya ya mik'e tsaye yana d'ingisa k'afa ya nufi d'akinsa."
Kallo dijama ta bishi dashi tana mmki a gaban idontafa ya ture plate d'in abinci,
kuma bbu wani Abu da yasame shi a k'afarsa,
Tab tace lallai yaya khalil babba ne."
Zaka warke ka dawo ne."
Bayan ya wuce ne ya shiga d'akinsa kai tsaye akan gado ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya. Yana murmushin samun nasara ya tserewa tarkon dijama."
*GA WNN YA TAYAKU FIRAR DARE*
🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅
Writteng
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*29*
Murmushi yakeyi idan ya tunada dijama a lokacin da take cewa
In tona."
Sai ya tsinci kansa yana mai sakin dariya,
Ya mirgina a kan gadonsa tare da rungune pillow."
Tabbas ko ba'a fad'a masa ba yasan ya kamu da son dijama,
Wanda ita kuma yake ganin matsananciyar tsanarshi a idonta."
Dogon nishi yaja ya kuma rungume pillow yace "dole ki soni dijama domin ni nakine bakida wani miji a fad'in duniyar nan Wanda ya wuce ni,
Ni nakine ke tawace."
Yana cikin wnn tunanin bacci b'arawo yyi awon gaba dashi."
Tun daga lokacin wasan b'uya ta Shiga tsakaninsa da dijama,
Koda zasu fito break fast, 9:am har ya karya yayi tafiyarsa,
Darana kuma lokacin da zaici abincinsa har suntafi makarantar islamiya, da dare sai bayan ya tabbatar da sun shige yake shigowa yaci abinsa yayi tafiyarsa."
Gudun kar su had'o da dijama ta tona masa asiri a gaban Abba da mommy, kamar ynda tace."
Hakan sukaci gaba da yi da ita har zuwa lokacin da hutyn makarantar su ya k'ara zata koma."
Duk wani shige da ficinta a kan idonsa takeyinsa yana kalllonta wani Abu idan tayi shi yayi dariya wani kuma ta yaji ta kuma Shiga ransa."
Yana lissafe da hutun makarantar ta ya k'are, lokacin da ya taso daga makaranta ya biyo ta wani katafaren store yayi mata siyayyar kayan makaranta masu yawa ya shigo dasu,
A lokacin Mahmud ya turo yaronsa da siyayyar duk wani Abun da yasan tana buk'ata ya saya mata."
D'an Aiken yana fita kenan,
Khalil ya tsaya da motarsa ya shiga jido kaya yana shigowa dasu."
Ido Abba da mommy suka bishi dashi cike da mmki basuyi masa maganaba sai da ya gama shigowa da kayan gaba d'aya snn ya nemi wuri ya zauna a kusa da mommy yana fad'in wash nagaji da yawa."
Suka bishi da ido cike da a yar tambaya???"
Sai da ya natsu snn Abba ya kalleshi ya nuna kayan da ya ajiye tsibi guda, yace "wa d'an nan kayan fa na meye?"
Khalil yayi murmushi yace "Abba Nana khadija. na sayomawa." kasan cewar hakan yake kiranta yanxun ya tsani a kirata da dijamar nan,
Yaci gaba da cewa domin ina lissafe da gobe ne suke komawa makaranta."
Abba ya kalleshi da kyau yace Ummie ta gode amma sai dai kayi hak'uri anrigaka."
"Meye aka rigani Abba?"
Ina nufin ka kwashi kayanka kaje ka mayar dasu a inda kasawosu domin kuwa Mahmud ya rigaka, babu abunda bai sawo ya turo akawo mata taba kamar yanda ya saba a koda yaushe.
Ba kamar kai daka tsira ynxun da rana tsaka."
Khalil bazan gaji da fad'a maka a kan kacire Abunda kakeso ka fito dashi a rana tsakar nan ba."
Dan haka ka kwashi kayanka ka mayar dasu a inda kafito dasu,
Ya fahimci inda maganar Abba ta nufa. Ransa ya b'aci amma kuma ya danne yace "Abba wai menayi?" Naga kamar duk an tsaneni a gidan nan?"
Sai a lokacin mommy tayi magana tace "khalil kazo ka dakemu kawai ka huta."
Tunda har tambayar abunda kayi kakeyi, ai ina ganin kafi kowa sanin Abunda ke cikin ranka Wanda bazai tab'a yiyuwaba,
Dan Allah malam tashi ka kwashe mana kayan nan naka wad'anda suka tare mana filin wuri kasan inda dare yayi maka dasu."
Jiki ba kwari ya mik'e tsaye cike da b'acin rai idonshi ya rikid'e zuwa launin ja."
Yashiga kwasar kayansa yana xubawa a mota."
Washe gari, dijama ta kammala shirinta cikin uniform ta fito sukayi sallama da mommy, da fateema."
Abba da kansa ya d'auketa ya nufi mkranta da ita."
Bayan sun wuce ne khalil ya fito cikin da kakkiyar shadda 'yar ubansu sai k'amshi yake zubawa, ya durk'usa har k'asa ya gaida mommy, snn yace "Nana khadija tafito muwuce kawai na shirya."
Mommy ta kallesa da kyau tayi murmushi irin nasu na manya tace " ai tuni Abbanku ya tafi wurin kaita."
Saurin d'aga kai yyi ka kalli mommy Wanda itama shi take kallo, ganin b'acin rai a fuskarsa ta zaro ido tace "meyafaru ne Khalil?"
"Ba komai yace had'ida mik'ewa tsaye jiki ba kwari yace "natafi makaranta."
Mommy tace break fast d'inkafa?"
D'an juyowa yyi yace "banajin yunwa idan naje can zansamu wani Abun da zanci."
"To Allah ya bada sa'a inji mommy ta bishi da kallo tana tausayin d'an nata."
**************
A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah. Yau ne ake bikin rantsar dasu mahmud a aikin soja."
In da sun kammala trening d'insu cikin nasara da taimakon Allah tare da sanya hannun Alhaji Atiku Mahmud ya fito da babban muk'ami."
Bikin rantsar dasu akeyi a garin Abuja inda aka tara manya mutane shuwa gabanni da 'yan siyasa domin shaidarwa."
Abba da mommy da khalil da fateema duk Suna wurin a zazzaune inda suke hango Mahmud zaune cikin uniform d'in soja wad'anda suka yi mashi masifar kyau sai kallonsu yakeyi yana murmushi farin ciki."
Gefensa d'aya kuma sulaiman ne, shima zaune yana hango matarsa da d'ansa yana aika masu da murmushi."
Kiran sunansu akeyi d'aya bayan d'aya, ana rantsar dasu tare da fad'in muk'amin su a kuma basu ta kardar shaida."
Abba yana tare da Abokinsa Alhaji Atiku suna fira sai godiya yake masa."
Shuru Abba yayi saka makon sunan Mahumd da yaji ana kiran tare da muk'amin da yaji ba'a kira kowa dashiba,
Ya kuma kashe kunne domin ya k'arajin abunda ake fad'i."
_"CAPTAIN MAHMUD HASSAN TOFA_ yaji ana fad'i, sai ganin Mahmud yayi ya taso yana murmushi aka Shiga rantsar dashi."
Abba bai San lokacin da ya rungume Alhaji Atiku ba sai godiya yake masa, domin duk matakin da yaga Mahmud ya taka dasa hannun Shi a ciki."
Alhaji Atiku yace "ka daina yimun godiya mahmud d'ana ne. Babu abunda bazan iya yimasa a rayuwa ba"
Idan ina da rai da lafiya mahmud sai ya hau kujerar da nake kai a yanxun ta commondent general."
Abba yaji dd'i sosai har yakejin a rayuwa babu abunda ba zai iya yiwa Alhaji Atiku ba."
Hkan dai akayita rantsar dasu, d'aya bayan d'aya, snn daga k'arshe aka sallamesu da cewa kowa yatafi gida sai nan da wata d'aya idan kud'insu suka fito za'ayi posting d'insu wurin da zasu fara aiki, domin su fara yiwa k'asa aikinta."
Gidan Alhaji Atiku su Abba suka nufa, gaba d'ayansu,
A inda aka shirya masu liyafa kala kala, cikin karamci."
hakan suka taru gaba d'aya har Alhaji Atiku da matarsa suka shiga cin abincin."
Abba ya duba baiga yusra ba ya dubi Alhaji Atiku yace "Alhaji Atiku wai ni ina 'yata ne yusra bngantaba?"
tun a can nakeson na tambayeka hankalina ne ya d'auku."
Dariya Alhaji Atiku yyi yace 'ai Shalele ta tafi England wurin hutawa, .d'azun da muke waya da ita nake gaya mata yau ne ake bikin rantsar da yayanta Mahmud rigima ta sanyamun tana kuka wai meyasa ban fad'a mata ba, domin ta shiryawa mahmud kyautar da zata bashi domin tayashi murna."
Abba yace "gskya ba'a kyautawa yusra ba mutum da yayanshi."
Suka Sanya dariya gaba d'ayansu."
Mahmud bai kulasu ba sai cin abincinsa yakeyi Wanda yakejinsa kamar yana cin magani."
Domin gaba d'aya ya tsani Alhaji Atiku da duk wani Abu da yafito daga gareshi sboda yafiya son kansa da yawa."
Hakan suka kammala cin abincin ko wannensu ya mik'e tsaye had'ida yi masu sallama, Abba sai godiya kawai yake tare da mommy suka fito."
Motar Khalil Abba yashiga tare da mommy,
Khalil kuma ya shiga motar mahmud tare da fateema da mahmud d'in gaba d'aya suka d'auki hanyar kano."
K'arfe goman dare suka sauka garin kano,
Gaba d'ayansu ko wannensu a gajiye yake."
Suna sauka kai tsaye ko wanensu ya nufi b'angarensa domin ya watsa ruwa ya huta."
Mahmud yana shiga d'akinsa kai tsaye toilet yashiga yayi wanka yafito ya shinfid'a abar sallah yayi sallah sann ya fad'a kan gadonsa ya kwanta tare da sauke ajiyar zuciya, babu abunda ya fad'o masa a rai a dai dai wnn lokacin sai dijamah."
Murmushi yayi domin shi kansa ya so ya ganta, yga ynda ta koma Allah yasa dai tayi hankali ta kuma daina rashin ji."
Da tunani gobe idan Allah ya tashesu lfy zaije har mkrantar ya kaimata ziyara."
Washe gari bayan yayi shirinsa cikin k'ananun kayansa wad'anda suka karb'i jikinsa suka fitar masa da mazan takarsa na jirumin maza, cikakken soja,
Inda yake ajiye turarensa yanufa, sai ganin wani kalar turare yyi Wanda shi bai San yana da irinsaba, baima tab'a ma'amala da irin turarenba."
D'auka yayi ya fesa a jikinsa saiji yyi wani k'amshin dad'i yana fita a turaren."
Lumshi idonsa yyi domin k'amshin turaren ya sanyashi farin ciki, da har yna tunawa da wasu abubuwa da sukayita faruwa na farin ciki."
Cikin nishad'i ya fito yanufi babban falon gidan, kowa da kowa ya hallara domin k'aryawa shi kad'ai akejira."
Durk'usawa yayi har k'asa ya gaida maihaifansa, snn khalil da fateemah suma suka gaidashi cike da girmamawa, yana murmushi ya amsa masu."
Anan ya jawo kujerar da ke kusa da Khalil ya zauna suka fara yin break fast,"
Bayan sun kammala ne mahmud yace wa Abba,
Abba zanje makarantar su dijama na dubata."
Gaban Khalil ya fad'i yayi saurin d'aga kai ya dubi mahmud ya kuma sunkuyar da kansa k'asa."
Abba yyi murmushi yace "ya kamata kuwa, amma idan kayi ido biyu da ummie na zakasha k'orafi."
Snn idan kadawo, ya kamata ka shirya katafi tofa wurin tsohuwa ka gaida ita, domin tana yawan yi mun k'orafi a kanka."
Dariya mahmud yyi yace "tsohuwa matsala ni har na mnta da ita."
Abba ya turo ido waje had'ida kallon mommy ya nunata da yatsa yace "wnn ce matsala,
Mahmud ya rik'e baki yana dariya yace "Abba mommy nan ce fa?"
Abba yace b'ace mun dagani Mahmud karna sab'a maka." Ai uwa batafi uwaba😊
Suka Sanya dariya gaba d'ayansu ya mik'e tsaye ya kalli Khalil yace muje ka rakani d'an uwa."
Ba ynda Khalil ya iya hakan ya mik'e tsaye, yabi bayansa, Abba da mommy suka bisu da Addu'ar adawo lfy."
Suka d'auki hanyar makarantar su dijama."
Suna cikin ofishin shugaban makaranta suna hira,
Mahmud nayi masa godiya hak'urin da yyitayi da dijama suka rik'eta batare da sun kuretaba."
Shugaba dariya kawai ykeyi, Khalil kuma yana zaune gefe d'aya yana murmushin da yafi kuka ciwo."
Wata siririyar murya tayi sallama ta shigo, ciki natsuwa, Wanda Khalil yanajin muryar sai da gabansa ya fad'i domin yasan mai wnn muryar ko ba'a fad'aba dijama ce."
Cikin uniform dinta take Wanda sukayi mata kyau tana shigowa cikin natsuwa ta fara cin karo da Khalil ta had'e fuskar had'ida murgud'a baki domin bata lura da Mahmud ba dayake zaune a kusa da Khalil duk a tunaninta Khalil ne yazo ya aika akirata."
Mahmud kuma ya tsura mata ido yana kallonta saboda mmkin ynda yaga ta canza masa kasa yin magana yyi."
Idonta ta wurga cike da tsiwa ta kalli kusa da Khalil d'in tayi ido biyu da Mahmud,
Wata kalar dariya tasaki tare da ihu cike da murna tayi kansa ta fad'a kan jikinsa tana fad'in oyoyo yaya Mahmud I miss you."
Runtse idonsa Khalil yyi ynajin wni Abu na masa yawo a zuciyarsa."
Mahmud bai San lokacin da ya maida ita a jikinsa ya rungumeta tsaf yana sauke ajiyar zuciya Wanda bai San yana yintaba cike da farin ciki. Ya lumshe idonsa."
🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅
Writteng
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*30*
Sai da suka d'auki kusan minti biyar a hakan snn mahmud ya cireta a jikinsa, had'ida rik'e mata hannu still idonsa a kanta yana kallonta yana murmushi."
Gefensa taje ta zauna a kusa dashi akan kujera ta zuba mashi ido tana kallonsa tana murmushin farin ciki."
Can ta nisa taja dogon ajiyar zuciya tace "shine ka kawoni nan kayi tafiyarka inda bnsan kowa ba, bayan kayi mun alk'awarin cewa danayi wata d'aya zakazo ka d'aukeni ka cireni ka cireni a wnn mkrantar.
Meyasa katafi ka barni?"
Bata barshi yayi maganaba taci gaba da cewa, had'ida kallonsa "tab yaya kaga ynda kayi kyau kuwa?"
Dama hakan aikin soja yake sanya mutum yayi kyau ya zama kamar balarabe?"
Dafe kai yayi, yace "dijamah halinki yana nan har ynzun baki canxaba."
Ta marairace fuska cikin shagwab'a Wanda ta kuma yi mata kyau tace "Allah na canza ka tambayi uncle kaji. Ganinka ne kawai sanyani nishad'i Dan Allah yaya karka tafi kabarni kai fa kayimun Alk'awari."
Magana takeyi amma kallonta yakeyi irin ynda take shagwab'a abun yyi mta kyau saiji yyi ta kuma shiga ransa,
Tunda aka haifi dijama yake sonta domin duk a cikin qannenshi yafi sonta a kan kowa, rashin jin da takeyine da rashin karatu yake had'ashi da ita, yake nuna mata kamar baya sonta domin kawai ta tsaya tayi karatu.
Ya kuma rik'o hannunta ya mik'ar da ita tsaye zuwa jikinsa,
hakan ya yasanya khalil yasaki wayar hannunsa bai saniba,
saka makon wani a zababben bugun zuciya da yaji k'irjinsa nyi masa.'
Mahmud bai lura da shiba hankalinsa na wurin dijama sai zuba masa shagwab'a takeyi tana kan k'afarsa zaune."
Labari take bashi na Anty rukayya irin karamcin da tayi mata da taimako."
Mahmud yace "wnn Anty rukayyah Allah ya biyata,
Akira mun ita nayi mata godiya."
Tasaki dariya Wanda sai da khalil ya runtse idonsa,
Tace "yaya Ashe kaga wnn turaren a d'akinka."
Ya kalleta cike da mmki yace "kece kika ajiyeshi?"
Ta langwab'e kai Wanda yin hkan ya k'ara mata kyau tace "tsarabarka ce Dana ajiye maka, lokacin da akayi mana hutu,
saboda nasanka kana da son turare, shine na ajiyema a d'akinka Dan kadda fateema tace nabata."
Khalil najin hakan hnkalinsa ya kuma tashi wayar hannunsa ta kuma sub'ucewa ta fad'i a karo na biyu, duk ta farfashe glass d'inta,
wnda yasa hankalin mahmud ya dawo Kansa,
Yace "subuhanallah."
D'an uwa meke faruwa?" Ya akayi hakan ya faru?"
Khalil da idonsa yyi masa ja, gaba d'aya duk haushin mahmud yakeji, wato bai Masan ko maike faruwa ba kenan."
Dakewa yyi ya k'irk'iro murmushin Dole yace "nima bnsaniba tana hannuna ta fad'i."
Dijama ta kallesa sukayi ido biyu ta wurga masa harara ta kawar da idonta."
Khalil na ganin hakan ya mik'e tsaye yace brother bari natafi mota na jiraka kaina keyimun ciwo."
Mahmud yace "eyya sorry to kaje ka zauna kajira yanzun zanfito sai mutafi gida."
Mahmud ya kalli dijama yace "bakiyiwa yayanki sannu ba?"
Ta shagwab'e fuska tace " ai shine."
Khalil najin tace hakan tun kafin ta k'arasa fad'in abunda zata fad'a yayi saurin ficewarsa, ya bar wurin domin duk a tunaninsa tonawar zatayi."
Mahmud yace "ai shine me?"
Meya mki?"
Ta turo bki tace "ai shine ya tsaneni baya son ya bud'i ido ya ganni."
Mahmud yyi murmushi yace "wnn kuma saboda bakyason karatu shiyasa kowa yake nuna mki baya sonki."
Amma tinda ynxun kina karatu kowa zai shirya dake."
Khalil yana shiga mota ya had'a kansa da sitiyarin mota, zuciyarsa na k'una, wani kalar azababben son dijama yakeji a ransa Wanda idan ya rasata jiyakeyi kamar zai iya rasa rayuwarsa."
Photon dariyar da takeyiwa Mahmud da shagwab'a da yanda suka rungume juna yake gani a idonsa, ko ba'a fad'a makaba da zarar ka gansu a hakan zaka tabbatarwa kanka da cewa masoya ne suna son junansu kuma sun shak'u da junansu."
Mahmud bai fito ofice d'in shugaba ba sai da yayi masa kyauta ta ban mmki snn ya nemi Alfarma da amayar da dijama aji uku tunda ya fahimci cewa tana da k'ok'ari sosai kuma tayi girma aji d'aya."
Anan take Shugaban mkrnta ya Amince domin shi kansa yyi wnn tunanin domin ya yaba da karatun dijama domin tana d'aya daga cikin d'aliban da makaranta take Alfahari dasu."
Anan sukayi sallama mahmud yafito tare da dijama ta biyoshi tayi masa rakiya sai shagwab'a take zuba masa tare da yimasa k'orafin ita dai a fitar da ita a mkrantar nan."
Murmushi kawai mahmud yakeyi tare da bata hak'uri."
Ahakan har ta kaishi bakin Mota, khalil ya had'a kansa da sitiyari yanajin duk abunda suke fad'a zuciyarsa na suya."
Mahmud ya shiga mazaunin direba ya zauna had'ida yimasa sannu snn yaja motar suka tafi, tare da yiwa dijama Alk'awarin cewa zai dawo nan da sati d'aya."
Cike da farin ciki yake tuk'i,
ya rasa dalilin farin cikinsa sai murmushi yakeyi yana shafar sajansa."
Khalil yana lura da hakan, sai ji yayi kansa ya kuma Sara masa."
Ahakan har suka kawo gida kai tsaye khalil ya bud'e murfin mota ya fito batare da yabi ta takan mahmud ba bare ya kallesa kai tsaye b'angarensa mahmud yaga ya nufa."
Ido Mahmud ya bisa dashi yana mmki, tare da tambayar kansa duk ciwon kan ne hakan?" Ko dai da akwai abunda yake damunsa."?
******************
Wata d'aya da rantsar dasu mahmud a