Showing 9001 words to 12000 words out of 44363 words
Chapter 4 - YAR GIDAN TSOHOWA Docment Complete Book .txt
jiran sufito surakasu, sukaji shuru basuda niyar fitowa, kai tsaye suka shiga d'akin, suka ta tarar dasu a zaune rungume da juna suna hawaye."
Sukansu saida suka tausaya masu ganin cewa tunda aka haifesu basu tab'a rabuwaba,
A yanxun shekara Ashirin da bakwai kenan sai yanzun da girmasu lokaci d'aya zasu rabu tabbas dole suyi kukan rabuwa."
Hakan suka shiga lallashinsu da ban baki da komai sannan suka lallab'asu had'ida yi masu rakiya suna d'agawa junansu hannu sukatafi."
Tsohuwa da Kaka sunyi kewar tafiyar tasu, sai dai daga k'arshe suka bisu da Addu'a Neman dacewa."
Wata d'aya da tafiyarsu suka shiga aiki gadan gadan baji bagani, kuma sun tsare gskiyarsu da Amana,
Kullu suna kiran junansu a waya ko kuma su hau charting suna fira cike da kewar junansu."
albashinsu na farko suka shigo garin na Tofa suka shiga rarrabawa tsofafin garin da masara k'arfi."
Sukayiwa tsohuwa gyaran gida aka mayar mata da ginin zamani, Kaka yacika da murna da farin ciki, suka wadata fahaifan nasu snn daga k'arshe suka koma wurin aikinsu."
Bayan shekara d'aya da fara aikin Nasu, ba laifi kud'i sun zauna masu a rayuwa babu abunda suka nema suka rasa, Kaka ya tayar masu da fitina akan cewa zamansu a hakan ya isa,
Ya kamata kowanne daga cikinsu ya nemi mata domin yayi aure, ko zasu ga jikokonsu tun suna da rayuwa."
Suka amsa gaba d'ayansu da to." daman abunda suke jira kenan."
Bayan wata biyu da yimasu maganar dukansu suka nemo matar aure a garin da suke aiki,
Hassan ya nemo auren Hajara, Husaini kuma ya Nemo auren Bilkisu."
Saida suka turawa junansu photo nan yan matansu dukansu sukayiwa juna sambarka da dacen da sukayi sannan suka isarwa da Kaka umurnin sa."
Kaka da tsohuwa sunji dad'i sosai sunyi murna, cikin sati d'aya aka tsaida magana aka sanya ranar bikin nasu nan da wata d'aya masu zuwa."
Akwana tashi lokacin bikinsu yayi aka shiga hidimar biki gadan gadan, in da Hassan ya k'era k'aton gida naji da gani a cikin garin kano,
Shima Husaini hakan,
gida iri d'aya sukayi duk abunda ke akwai gidan hassan akwaishi gidan Husaini gari kawai ya babbanta Hassan a kano husaini a lagos."
Ansha shagalin biki anyi taron bikin da ba'a tab'ayin irinsaba a cikin k'auyen na Tofa."
Ko wannansu Amaryarshi ta tare a gidansa."
Hmmmmm."
Bayan wata tara da aurensu matar Hassan ta haihu ta haifi d'anta namiji mai kama da Husaini sak👌🏻 mmki kowa yakeyi sai. Sai dai ba abun mmki bane kasancewa jini d'aya ne."
Murna Husaini yashigayi dajin labari, tun kafin ya iso yasanyawa yaro suna *Mahmud* Hassan yaji dad'i sosai domin shi a kullum farin cikin husaini shine nashi. Kuma duk abunda yakeso shima shi yakeso."
Shekarar Mahmud Uku aduniya aka Haifa mashi k'anwa aka Sanya mata suna Asma'u."
Har a lokacin matar Husaini ko b'atan wata bata tab'ayiba."
Ta d'auki damuwar duniyar nan ta d'orata a kanta, inda shi kuma Husaini sai dai ya dinga Addu"a, Allah yabashi mai Albarka idan lokaci yayi."
Wanda a wannan lokacin Hassan kud'i sun zauna mashi ya daina aikin kamfani yashiga harkar siyasa gadan gadan."
Shima Husaini hakan ta kasance a gareshi yazama babban d'an jarida a garin lagos wanda akeji dashi, kud'i sun zauna masu."
Bayan matar Hassan ta yaye Asma'u ta kuma samun wani cikin ta haifi d'anta namiji aka sanya mashi suna Adamu wato sunan Kaka kenan suna kiranshi da Khalil."
Wasa wasa sai da sukayi shekara goma sha uku da Aure sannan Allah yabawa matar Husaini ciki, Wanda yayi dai dai da kuma samun cikin matar hassan haihuwa ta hud'u."
Samun cikin Bilkisu matar Husaini ba k'aramin murna sukayi ba gaba d'aya family musamman Hassan, da yakeji tamkar matarsa ce keda cikin."
Haka sukaci gaba da renon cikinsu har ya kai watan haihuwa, ta haifi 'yarta macce sak Hassan,
Masu karatu kusan dai Hassan da Husaini kamarsu d'aya idanba saninsu kayiba bazaka iya tattace d'ayansuba."
Hassan yayi mata hud'uba yasanya mata suna Nana Khadija wato sunan tsohuwa kenan, inda tsohuwa taji dad'in wannan kara da akayi mata aka sanya sunanta, amma kuma ta shinfid'a sharad'in cewa baza'a canza mata sunaba akirata da ainahin sunanta Nana khadija."
Hakan akayi domin bin umurnita, ba'a canxa mata sunaba da sunanta kowa ke kiranta, amma bnda mahaifan nata sai dai suka dinga kiranta da Ummie." Inda tsohuwa take kiranta da deejamah."
Tunda akazo da Mahmud wurin bikin sunan Nana khadija, yaji yana sonta musamman da duk wanda ya gansu ake cewa kamarsu d'aya a lokacin mahmud yana da shekara goma sha d'aya."
Idan zai kwanta barci dole sai a kusa da ita yake kwantawa. Wnn abun bak'aramin dad'i yayi wa mahaifan nasuba."
Bayan haihuwar khadija da sati d'aya matar hassan ta kuma haihuwa ta haifi 'ya mace aka sanya mata suna Fateemah."
Bilkisu tayi Arba'in d'in Nana Khadija cike da k'oshin lafiya, dijama tayi kyau harta gaji sak kamannunta suka dinga komawa na mahaifinta."
Shiri sukeyi zasuzo Kano yawon Arba'in domin ya d'auk'i huto a wurin aikinsa."
Sun shirya tsaf cikin Shiga ta Alfarma, anyiwa Deejamah kwanliya tayi kyau tana sab'e a kafad'ar mahaifiyarta, Husaini yana janye da a kwati yana k'ok'arin sanyashi a but,
Bayan ya shirya komai suka shiga mota yajasu suka d'auki hnyar kano."
Tafiya sukeyi suna yiwa 'yarsu wasa cike da so da k'auna,
Suna kaf da kawowa Husaini yana yawa da Hassan kan cewa gasunan sun kusan kawowa, domin sai sunfara tsayawa cikin kano wurin hassan idan sukayi kwana biyu sai su wuce Tofa wurin tsohuwa idan suka gama kwanakin da zasuyi sai su dawo gida."
Yana cikin waya da hassan saigani sukayi mai mota ya gifta masu ta gabansu ya daki motarsu,
Tayar motar husaini ta fita ya yanki daji babu abunda sukeyi sai Addu'a domin kuwa yayita k'ok'arin ya tsayar da motar amma yakasa."
Saida takai gindin wani k'aton icce, ta daki icce gaba d'aya motar takife,
Wadda yyi ddai da zuwan mutanen da abun ya faru a gabansu suka biyo bayansu domin ceto rywarsu."
K'ok'arin tsiratar da rayuwarsu aka shigayi, da kyar aka samu a ka fito dasu a k'ark'ashin motar wanda a lokacin ko wannensu baya motsi Allah ya karb'i rayuwar bayinsa."
Cikin ikon Allah Nana khadija ko kwarzane batayiba, koda aka cirota a motar sai wasa takeyi da hannunta alamar tana cikin k'oshin lfy."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅
Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*9*
Gudu takeyi tana ihu,
Buba na biye da ita.
Samarin Antyn lantana ne, suka hangota tana tik'ar gudu suma suka dafo mata dama jiranta sukeyi sunada haushinta."
Tana ganinsu suma sun biyota, ta kuma k'ara gudu tana fad'in wayyo jama'a kufito Ku taimakeni 'yan fashi da makami."
Wani tsoho a kan kekensa yana tafiya yanajin hka yasaki keken ya xuba da gudu ya nemi ma b'oya."
Matan Aure sai kama d'iyansu sukeyi suna rufewa a d'aki suna Addu'oi domin a tunaninsu 'yan fashin ne suka shigo cikin garin."
Dantijawan garin da samaru suna ganin su Buba na gudu tareda dijama,
sun d'auka 'yan fashin sukeyiwa gudu, ai kuwa har 'yan rigaggen gudu sukeyi suna shigewa gida had'ida rufo k'ofa da sanya sakata."
Duk inda dijama ta gifta tana ihu su Buba na biye da ita suna Neman kamata,
Jin ihunta tana fad'in wayyo 'yan fashi da makami, jama'a kufito Ku taimakeni
Kowa ta Kansa yakeyi baya tsayawa saurarenta."
Da kyar tasamu ta kawo gida, tana shiga gida ta mayar da k'ofa ta rufe ta sanya sakata,
Ihun takeyi bakinta yak'i yayi shuru tana fad'in "wayyo tsohuwa 'yan fashi da makami."
A razane Abba ya mik'e tsaye cike da tashin hankali da tsoro ya tallabi Kaka yashigar dashi d'aki,
Tuni tsohuwa ta kai d'aki zaninta a hannu daga ita sai dogon siket, saura kad'an tayi tuntub'e ta fad'a wurin tashi."
D'aki d'aya suka shige suka rufe ko wannensu sai zarar ido yakeyi."
Can sukaji ana dukan k'ofar waje da k'arfi kamar za'a cire k'ofar.'
Jikin tsohuwa ya soma rawa tana kallon Abba tana cewa "yanxun Hassan ya zamuyi?" Karfa su shigo su kashemu."
Abba yace "kwantar da hankalinki tsohuwa baxasu kashemuba,
jin haushina d'aya na baro bindigata a cikin mota."
Kaka kuma ya sunkuyar da kai sai salati yakeyi yana addu'a jikinsa sai rawa yakeyi'
Dukan k'ofa akeyi ba girma ba arziki, tsohuwa ta dinga rawar jiki zanenta a hannunta takasa d'aurawa sai addu'a takeyi idan tasaki wannan ta kwaso wannan."
Dijama ta dubi tsohuwa ta dubi kaka ta rik'e ciki tashiga kwasar dariya, tana nunasu da hannu."
Tsohuwa na ganin hakan ta fara tunanin ko dijamace ta janyo fitina a waje ba 'yan fashin bane."
Tsohuwa tace Hassan ina ganin ba 'yan fashibane dijama ta janyo mana fitina."
Abba yayi saurin waigawa ya dubi dijama da sai dariya takeyi idan ta dubi tsohuwa da kaka.
"Yace dijama suwaye ne? Mekikayi masu?"
Turo baki tayi tace Abba su Buba ne, bata k'arasa maganarba sukaji dukan k'ofar yayi yawa, kamar harda hayaniyar mutane a wajen,
Sai a lokacin Kaka yayi magana yace "ai saikatashi kafita kaji abunda ke faruwa,
Indai wann hatsabibiyar yarinyarce wata rana sai ta janyo mana mgnar da za'a cinnawa gidan nan wuta duk mu k'une gaba d'aya
Yana gama mgnar ya wurgawa dijama harara ya d'aga sandarsa ya zungureta mata k'afa da ita."
Abba ya mik'e da Sauri ya bud'e k'ofa yafita,
Bbu abunda tsohuwa takeyi sai wurgawa dijama harara domin yau ta kaita bango."
Abba yana fita yaga mutane jimjim a k'ofar gida, babba da yaro, tsofaffi da samari,
kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama,
a gefe d'aya tawagarsu Buba ce da makamai a hannunsu,
d'aya gefen kuma samarin Antyn Lantanane suma rik'e da makamai, rik'e baki yayi yacika da mmki."
Suna ganin fitowarshi sukayi saurin ajiye makamansu suka zube k'asa suna gaida shi."
Bai tambayi abunda ke faruwaba Dan yaji duk abunda suke fad'i, illah yashiga basu hak'uri, tare da rarraba masu kud'i."
Wani dantijo yagani zaune wuri d'aya ya rafka tagumi, kowa yana zuwa karb'ar Kud'i shi yana zaune wuri d'aya baya da niyar motsawa,daga inda yake,
Abba ya isa kusa gareshi yace "Baba lfy meya faru?" Ko wanine bashi da lfy a cikin iyalinka."
Dantijon ya dubi Abba yace "Alhaji dama ciwon ne ai da sauk'i."
Abba yace "Baba meke faruwa?"
Ina kan keke na ina tafiya yarinyar wurinka tadinga ihu tana fad'in 'yan fashi da makami, bansan lokacin da nasaki keken hannuna naba,
wurin intsiratar da kaina,
Kafin in ankara ansace mun keke, kuma wlh Alhaji shi kad'ai na mallaka shine kaddarata."
Abba ya lallasheshi had'ida kirga kud'i masu yawa wad'anda sukafi na keken yabashi had'ida bashi hak'uri,
Hakan Abba yayi bawa mutane hak'uri yana yimasu Alheri suna wucewa daga ciki kuwa harda Buba da yaranshi da saurayin Antyn lantana."
Harda wani magidanci wurin gudun 'yan fashi bai saniba ya ture 'yarshi ta karye a hannu, bai ankaraba saida yaji ance ba yan fashin bane snn ya fahimci Ashe ya karye 'yarshi a hannu."
Shima Abba yabashi hak'uri had'ida bashi kud'i masu yawa da zai nemarwa yarshi magani harta warke."
Sann Abba ya juya yashiga gida yanata mmkin hatsabibanci irin na dijama,
Dijama ta rakub'e wuri d'aya sai zarar ido takeyi tsohuwa sai faman fad'a take mata kamar ta daketa."
Abba shima yashiga yimata fad'a kamar ya doketa abunda bai tab'a yi mataba tunda aka haifeta,
Kaka dake zaune gefe d'aya yace "gwara da Allah yasa ka nan a gaban idonka hakan ta faru,
Kullum a rana d'aya sai sama da mutum goma sunkawo k'ararta tsohuwa ke tare mata,bata son ganin b'acin ranta."
Amma tunda ynxun ka ganewa idonka sai ka d'auki mataki, akai,
Ga ganta nan Ko mkranta bata zuwa gaba d'aya makarantar biyu Arabic da boko duk ankorota, saboda hatsabibancinta gata bata gane komai sai fitina da rashin kunya. Yakai k'arshen maganarshi yana zungura mata sandar hannunshi."
Tsohuwa bata tanka masuba saima taja bakinta tayi shuru, domin yau itama dijama ta kaita bango."
Abba yayi kyaran murya ya dubi tsohuwa yace "inna kiyi hak'uri kibani dijama natafi da ita na nema mata ilimi Wanda zatayi dogaro da kanta tazama abar Alfahari a cikin Al'umma, yin hkan shi zai Sanya mana natsuwa a zuciyarmu ganin mun rik'e marainiyar Allah tsakani da Allah."
Kaka yayi karaf yace "aikuwa wlh da ka taimakemu ka taimaki mutanen garin nan mundun katafi da dijama kabar garin nan da ita,
ni wlh wani lkcin idan na tsaya ina tunanin inda dijama ta gado wnn halin nata sai inkasa tunano kowa a cikin zuri'armu, ina ganin wata k'ila a can cikin dangin mahaifiyarta tayi gadon wnn halin."
Tsohuwa tace "nidai ya isa haka malam kamata yayi kadinga yiwa dijama Addu'a ba aibatataba."
Kaka yace "ni Sam bana aibata dijama a kullum Addu'a ta d'aya Allah ya shirya mana ita, yabamu ikon rik'e amarta da Allah ya d'ora mana a kai."
Abba ya katse zancan da yace "to Ummie tashi kishiga ciki ki had'o kayanki mutafi marece yafara."
Tana murna tana tsalle zataje birni. Ta tashi tashiga d'aki ta fara had'a kayanta."
Tsohuwa bata son tafiyar dijama dan dai ba yanda zatayi ne, dole ta hak'ura tabari za'a tafi da ita."
Sai da ta shirya kayanta tsaf a jaka ta tallabo jakar tana dariya tana jin dad'i, ta fito."
Abba har ya kammala shirinsa ya fito had'ida yiwa su tsohuwa sallama dijama na gabansa Jakarta a hannunta suka nufi hanyar waje,
Tsohuwa dai Addu'a take masu Wanda takejin kanta duk ba dad'i an d'auke Mata dijamarta."
Kaka kuma saboda dad'i kamar ya zuba ruwa a k'asa yashi, domin yasan yau idan ya kwanta barci ba bak'ocin da zai tayar dashi domin kawo shedun dijama."
Har mota suka rakasu, suna yimasu add'o'i."
Mutanene cimjim gaban motar k'awayen dijama suna bangwana, Abba ya bud'a mota yashiga dijama itama tashiga gidan gaba sai wasar baki takeyi tana dariya tana d'agawa su suwaiba hannu."
Murmushi Abba yayi ya kunna mota ya fara tafiya, Dijama ta lek'o ta k'ofar marfin mota tace "suwaiba idan kukaje gonar Audu wurin satar gwaiba,
idan kukaga Buba kuce masa natafi birni amma zandawo don saina rama abunda yayi mun."
Abba yace Ummie na wai meye hkan? Ki zauna dai dai mana karda kiji ciwo."
Snn tayi saurin gyara zamanta Abba yaja mota
Yatafi yana dariyarta, suka d'auki hnyar kano."
_dijama a birni ikon Allah🤔_
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
8⃣
Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya,
gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya,
ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo."
Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke."
Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce."
A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba,
kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi."
Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini."
Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr,
Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya."
A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa,
Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara."
Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema,
Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba."
Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba."
Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa."
Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta."
Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa."
Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba."
Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi."
Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa."
Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa."
Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta,
Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa."
Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu,
bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka,
zarar hutunsu ya k'are Idan