Showing 15001 words to 18000 words out of 44363 words
Chapter 6 - YAR GIDAN TSOHOWA Docment Complete Book .txt
ya shiga murzawa yana kallonta had'ida kashe mata ido d'aya."
Yace "kinsan wani Abu kuwa?"
A kasalance ta dubeshi ta girgiza kai alamar A'a."
"A kullum idan ina tare dake jinakeyi tamkar ina tare da yarinya yar shekara 17,
saboda komai naki na dabanne a koda yaushe yarinya kike komawa."
Ya kuma shege mata a jiki yana shishinar daddad'an k'amshin jikinta,
had'ida sab'ule mata d'ankwalin kanta yana shafa gashin kanta dayasha gyara da mayunka masu Sanya laushin gashi da santsi uwa uba kuma k'amshi."
_Ina ganin hakan nayi saurin fitowa cike da mmkin su Abba da momy ba'a tsofa๐ค_
Mahmoud yaje makarantarsu fateema yayi duk abunda Abba ya umurceshi,
ya k'arb'o mata uniform d'inta da littafanta yataho mata dasu,
Ranar Monday zata fara zuwa makaranta."
Da sallamarshi ya shigo cikin babban falon gidan,
ba kowa a cikinsa, sai tausin k'arar TV kawai yakeji yana tashi, gefe d'aya yaji sai dariya akeyi harda buga k'afa.'
Koba'a fad'a masaba yasan dijama ce."
Mmki yashigayi yanufi wurin TV yayi saurin kashewa,
Ya juya ya kalleta, sukayi ido biyu da ita,
ta turo baki tana hararsa k'asa k'asa."
Cikin fushi yace "lallai d'an k'auye yashigo birni yafara wayewa,
Tomu a nan gidan ba'a mana kallo a k'urema volume, anan gidan karatu akeyi a koda yaushe ba zaman shashnciba da rashin kunya, takwala kawai Wanda bata gane karatu."
Ya jefa mata ledar kayan makarantarta yace "gasu nan ki kwana da shiri gobe Monday zaki fara zuwa makaranta, kuma nizan kaiki da kaina, zan shaida masu cewa baki gane komai kwakwalwar kifi ce dake, kuma da zarar kinyi masu irin rashin kunyar da kikeyi a k'auye, zance suyi fata fata da naman jikinki su jefar dake a bula."
Dama tsohuwa ke tare maki yanxunfa?"
Kallonshi tayi idonta cike da hawaye domin a rayuwarta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmoud ya kirata da takkwala mai kwanyar kifi."
Shima yayi mmkin ganin zubar hawaye a idon dijama anan take lokaci d'aya."
Zata bud'a Baki tayi magana kenan ya matso daf da ita, yace "muddun kika bud'a baki kikayimun rashin kunya saina tattakaki."
Ta fasayin maganar ta sunkuyar da kanta k'asa tana aika mashi da Allah ya isa a zuciyarta.'
Mik'ewa tayi tsaye ta d'auki ledar uniform d'inta, saida ta kwatanci saiti wurin k'afarshi ta
sakar mashi remote d'in TV a babban d'an yatsan k'afa, sai da yayi sarin runtse idonshi yace "washh."
Saboda zafin dayaji wurin namasa."
Ta zuba da gudu ta haiye sama tanufi d'akinsu, taja tayi tsaya a bakin k'ofar d'aki, tana kallonshi tana burgud'a baki tace "kuma bani bace takwala sai dai inkaine."
Kuma tunda kakeyimun gorin karatu saina baka mamaki mugu kawai, dan kana ganin nazo gidanku, to kasani duk abunda kakeyimun a rubuce yake a kaina saina fad'awa tsohuwa."
Ganin ya nufota tayi saurin shigewa d'akin had'ida sanyawa k'ofar key."
Tsaye yayi yakasa tafiya yana kallon babban d'an ya tsanshi da ya somayin ja,
Yana tunanin dijama wato bata daina halintaba kenan lallai akwai aiki a nan gaba."
Yana nan tsaye wuri d'aya saiji yayi andafashi a bayanshi, Khalil yagani yace "brother lfy kayi tsaye a nan?"
Su momyn basu dawobane?"
Mahmoud yace "fita sukayi ne?
"Khalil yace "sunje gidan gaisuwa tare da Abba."
Ya mik'awa Mahmoud wani takarda Mahmoud ya karb'a yana dubawa yana cewa "takardar meye?"
Khalil ya yamutsa fuska yace form d'in islamiyar wnn bagidajiyar nan ne, wadda Abba yasanyani karb'owa, nagama cika komai sunanta ne kawai bansaniba,
Wlh bnsan abunda yasa Abba ya dawo da ita gidan nan ba, da zarar munyi ido biyu da ita jinakeyi kamar zanyi amai."
Mahmoud ya dubeshi yace "khalil 'yar uwarka face, gakya ya kamata ka canza hali Kuma ka canza rayuwa, kadaina ganin 'yan matan Jami"a kyawawa wayayi suna rud'arka har kake kyamatar jininka. To kasani asalinka k'auye a can Abbamu ya tashi a can ya girma har gobe mahaifansa suna k'auye."
Wani saurin ja da baya yayi yana duba bayansa, ganin baiga kowa a wurinba yace "haba brother bazaka gane bane, nagodewa Allah da bakowa a kusa dani lokacinda kake fad'in hakan daka sanyani naji kunya."
Ido Mahmoud ya tsora mashi yana mmkinsa domin yanda ya d'aukeshi sai yaga ya wuce nan."
Takarda ya mik'a mashi yace "ynda bakasan sunantaba nima bnsan sunantaba, kabari idan Abba ya dawo shida ya sanyaka saika tmbayeshi sunanta kagani sai ya fad'a maka."
Yana kawowa nan yayi tafiyarshi ya barshi nan tsaye zuciyarshi cike da mmkin khalil."
Khalil yabi mahmoud da kallo yace "ya za'ayi na tambayi Abba sunanta, nasan yanda yakejinta a gidan nan yana iya kafsamin a gabanta
Zan dai jira har lokacin da fateema dawo daga mkranta saina tambayeta."
Yajuya yanufi d'akinshi yana mamakin mohmuod ganin yanda shima yakeji da wann bagidajiyar a gidan nanโน
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMAH*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_ )๐
Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*13*
Da sauri shugaban mkranta ya nufo ajin har da tuntub'e. Yakeyi domin lbrin da ya isar mashi anjiwa 'yar ciyaman da 'yar kassila ciwo."
Ganin saurin da yakeyi yasa sauran malamai suka fahimci a akwai abunda ke faruwa, suka rufo mashi baya."
Ganin jinin dake zuba a bakukansu ya d'agawa malamai hankali. Anan take aka Shiga basu taimakon gaggawa."
Shugaban makaranta ya d'aga waya ya kira ciyaman da kassila yake shaida masu abunda ke faruwa."
Ko wannensu cikin tashin hankali suka bugawa jami'an tsaro waya, anan take mota biyu ta 'yan sanda kamar had'in baki, motar ciyaman da motar kassila."
Suka shigo cikin mkrantar sai jiniya kukeji kamar za'a tashi makarantar, 'yan sandan kowanensu da zungureriyar bindigarshi a hannunshi."
Sai tambaya sukeyi ina yarinyar da taji masu ciwo, a wuce da ita atafi da ita a hukuntata."
Dijama dake tsugune gefe d'aya sai Zarar ido takeyi ta karkace kai duk Wanda ke magana tana binshi da kallon tana kallon bakinshi."
Turanci kawai takeji yana tashi Wanda bata san abunda suke cewaba kallonsu kawai takeyi."
Can taga shugaban makaranta ya nunata da yatsa yana fad'i da Hausa yana cewa "kunganta can itace, yau yau d'in nan da zuwanta makarantar nan amma har ta fara dazamun bala'i."
Shekarata goma sha d'aya da bud'a makarantar nan hakan bata tab'a faruwa daniba sai zuwan wann fiti nan niyar yarinya."
Tsawa aka dokawa dijama Wanda yasa tayi saurin mik'ewa tsaye saboda ganin zungureriyar bindigar dake hannun d'an sandar."
Tashiga ja da baya tana "fad'in Dan Allah kuyi hak'uri karku harbeni sune suka fara tsokanata."
Fateema kuma babu abunda takeyi sai aikin kuka, Wanda a cikin mutanen wurin bbu Wanda ya lura da ita tana gefe d'aya a tsaye."
Kuma doka mata tsawa d'an sandar yayi, yace "ba kasheki zamuyiba tafiya zamuyi dake sai munji ko waye ubanki a garin nan snn mu d'aukar mki hukunci."
Haka aka sanya k'eyar dijama a gaba tare da shugaban mkranta aka sanyasu a mota aka tafi dasu."
Dijama sai Zarar ido takeyi wuk'i wuk'i a bayan mota, shugaban makaranta da juya ya kalleta sunyi ido biyu da ita sai ya wurga mata harara."
A zuciyarshi yana da yasani karb'arta da yayi a matsayin d'aliba."
Fateema na ganin antafi da dijama, ta kuma fashewa da kuka,
tayiwa wani malami magani tace "dan Allah uncle kabani Aron wayarka zankira Abba na na fad'a mashi abunda ke faruwa."
Zaro ido yyi cike da mmki yace "dama kinsanta ne?"
Ta d'aga kai alamar "eh tace yayata ce uwarmu d'aya ubanmu d'aya."
Uncle ya xaro ido waje yace "kina nufin 'yar Alhaji Hassan Adam CE?"
To ya akayi bansanta ba a cikin gidanku?"
Cike dajin haushin tambayarshi fateema ta turo baki tace "bazaka Santaba saboda ba'a garin nan takeba,
dan Allah uncle kabani aron wayar mana."
Yace "Ayyah fateema kiyi hak'uri banada waya a hannuna, amma nasan za'aje da ita ta nuna gidansu."
_kuyi hk'uri d wnn pls yau sai a hnkli_
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMAH*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_ )๐
Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*12*
7:30am. Shiri sukeyi domin zuwa makaranta,
tasanya uniform dinta, wad'anda sukayi mata kyau sunfito mata da fuskarta sak 'yar fillo."
Fuskar nan tata tasha hoda da jambaki,
fateema dake gefenta zaune,
ta dubeta tace "dijama ki goge wnn kwanliyar ta fuskarki tayi yawa sosai idan mukaje Anty tana iya sanya hijabinki fari ta goge mki ita."
Ta murgud'a baki tace "bazan gogeba, a hakan zanje kuma bata isa ta gogemun kwanliya taba."
Fateema zata kuma yin magana tajiyo sautin muryar yaya Mahmoud yana fad'in "wai bazaku fitoba lokaci fa na tafiya, Allah duk kuka kuskura kuka bari na hawo saman nan sai jikinku ya gaya maku."
Da sauri fateema ta d'auki school bag d'inta ta goya. Bata kuma bi takan dijamaba don tasan halin yaya Mahmoud ba sauk'i ne dashi ba."
Dijama da ke k'ok'arin sanya sendel a k'afarta tana turo baki cikin magana k'asa k'asa tace "to idan ka hawo karka barmu da rai ka kashemu."
Ido fateema ta zaro waje tace "yayan kike cewa hakan lallai dijama bakisan halin yaya Mahmoud bane, tana fad'in hakan tayi saurin bud'e k'ofa ta fita, tabar dijama na sanya takalmi."
Tana gama sanyawa itama ta biyo bayanta, ta fito tana tafiya harda wani rangwad'a takeyi wai ita 'yar boko."
Gaba d'anyansu Suna babban falo zaune suna Brest fast, Abba da shirinsa na zuwa Office khalil shima da shirinsa zuwa makaranta BUK."
Mahmuod a tsaye da key d'in mota a hannunshi yana jiran fitowarsu ya kaisu, yadawo yana da inda zaije, har sun b'ata mashi time."
Fateema ta fara fitowa sann dijama ta biyo bayanta,
Abba na ganinsu cikin uniform yaji dad'i sosai sai murmushi yakeyi a fuskarshi,
Momy itama murmushin takeyi tana fad'in "iye 'yan matana lallai kunyi kyau musamman 'yata ummie."
Mahmoud dake tsaye gefe d'aya yanayi yana kallon agogon gwal dake d'aure a hannunshi."
Khalil ya d'aga kansa yana ya mutsa fuska yana kallon dijama. Da take k'ok'arin k'arb'ar flast d'in break d'insu. Wanda momy ke mik'a masu,
Ido biyu yayi da fuskar dijama datasha kwalliya,
mai zaiyi idan ba dariya ba,
Dariya yakeyi yana nuna fuskarta yana fad'in tab "mutumin k'auye baiyi ba wlh ke wai kwanliyace kikayi hakan ko meye?"
Brother wlh karka bari wnn abar ta shigar maka mota, ai sai kuzama abunda kwatance duk inda kuka gifta."
Cikin zafin rai Abba ya doka mashi tsawa da k'arfi yace "khalil tashi kafita karna na sab'a maka wlh."
Momy Itama tabishi da harara tana fad'in "ni bansan irin rayuwar khalil ba a cikin gidan nan."
Ta jawo hannun dijama dake tsaye wuri d'aya tana cije baki had'ida girgiza kai, ranta ya b'aci matuk'a."
Mahmoud dake tsaye a inda yake, ya had'e fuska,
yayi saurin waigawa ya wurgawa khalil harara cike da jin haushinsa."
Mmy ta rik'o hannuta tace "zo nan 'yata na gyara maki fuskarki karki damu da abunda khalili yayi mki hka halinshi yake."
Momy tashiga gyara mata fuskarta, ta goge mata janbakin da 'yar gira, ta kuma rage mata hudar fuskarta,
Sauran kwallin da tashafa a idonta ne yak'i goguwa. Gudun karsuyi latti momy ta barta haka suka tafi."
Bayan sunfita ne Abba ya maida kallonsa ga momy yace "nafara ganin take taken khalil a gidan nan a kan ummie zan d'aukar mashi mummunan mataki idan hakan ta kuma faruwa a kan idona."
Inason Allah yabani iko da nisan kwana nacika Alk'awarin da nayiwa d'an uwana kafin ya mutu,
na aurawa muhmud Ummie idan ba hakan ba a yanda naga khalil na kyamatarta a gidan nan da bbu abunda zai hana na aura mashi ita, domin kawai naga iya karshi."
Hak'uri momy kawai take bashi domin ganin ranshi ya b'aci sosai."
A bayan mota suka shiga mahmud bai kulasuba, fuskarshi a had'e, ya tayar da
motarsa yaja yanufi makarantarsu."
Suna shiga cikin makarantar yayi parking d'in motar shi a cikin harabar makarantar,
, tun kafin ya fito dijama ta rigashi fitowa harwani sauri takeyi k'asa na tashi,
Da sauri ya doka mata tsawa yace "ke 'yar k'auye da Allah malama ki dawo ki tsaya."
Kina wata tafiya k'ura na tashi sallan ki b'atawa mutane jiki da k'asa, 'yar k'auye kawai
Takkwala mai kwanyar kifi, kamar da gske sai kace ganewa kikeyi.
To bari na fad'a mki nan ba k'auye bane mudun kikayiwa malamai rashin kunyar da kikeyi a k'auye tsinanen dukan tsiya zakici kuma ba Wanda zai rama maki."
Juyowa tayi tana kallonshi ta sunkuyar da kanta k'asa, a rayuwar ta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmud ya kirata da mai kwanyar kifi, ta d'aukarwa kanta Alk'awarin cewa zata maida hankali tayi karatu Wanda yaya Mahmud sai yayi mmkinta,
a lokacin zata bud'e baki ta mayar masa da raddin takkwalar da yake kiranta da ita."
A fusace ya juya wurin fateema da mmkinsa bai gantaba sai ma hangota da yayi ta kusan shigewa class."
Gaba ya shige dijama na biye dashi, office d'in shugaban mkranta ya shiga ya gabatar da dijama, sann daga k'arshe gaban idonsa aka kaita class,
Aji d'aya aka ajiyesu da fateema kamar yanda ya buk'ata, saboda fateema ta dinga koya mata wasu abubuwa wad'anda bata saniba."
Sai da yaga shigarta aji sann ya shiga motarsa ya dawo gida."
Da shigarta ajin d'alibai sai kallonta sukeyi ganin yanda ta tsurawa silin roba ido sai kallo takeyi, gaba d'aya sai k'arewa ajin kallo takeyi da kujerun dake ajiye a cikin class d'in."
Fateema ta hango a can zaune tayi saurin bud'e baki tare da d'aga murya tace "lah fati Ashe aji d'aya aka ajiyemu ai kuwa naji dad'i."
Gaba d'aya ajin suka tuntsere mata da dariya, wata 'd'iyar chiyaman d'in garin,
Wanda suke mak'otaka da Abba, tace "amma dai ke 'yar k'auyece wlh."
Suka kuma shek'e mata da dariya, wata d'aliba daga cikinsu tace "dubi yanda ta shafa kwanli a idonta, ta fad'i hakan had'ida nuna idon dijama suka kuma shek'ewa da dariya."
Dijama taji haushi sosai, fateema ta mik'e tsaye ta kama hannun dijama da tayi tsaye takasa zama saboda jin haushi, ta zaunar da ita a kan kujera kusa da ita."
Dijama taja wuri d'aya ta zauna tana sake sake a ranta,
Malam mai English ya shigo ya fara yi masu karatu ta kashe kunne ta kwantar da hankalinta tana saurare kuma tana fahimta."
K'araurawa taji an buga alamar antashi break fast, hakan yayi dai dai da fitar malma mai English, d'alibai suka fara fita waje domin cin abinci."
Da sauri dijama ta duro a kan kujera ta shagaban 'yar gidan chiyaman
karon farko mari ta fara kai mata, ta cire hijabin jikinta tasha d'amara cikin d'aga murya tace "ubnwa kike cewa 'yar k'auye?" Tashiga nusarta, baji bagani, saida bakinta ya fashe da jini,
gaba d'aya ta b'ata gaban hijabinta,
D'aya yarinya wanda harda ita wurin yi mata dariya,
ta matso wurin dijama ta cimuimuye mata riga a bayanta,
Dijama tasanya k'afa ta bayanta ta shure mata baki, aikuwa yarinya ta kwatsa ihu ta duk'e ta rik'e bakinta da jini yaketa zuba."
Ihu 'yan aji keyi da gudu suka fita suka kira shugaban makarantar."
Babu abunda fateema keyi sai aikin kuka,
Dama kuka baya mata wuya, saboda kwata kwata fateema bata da fad'a batason tashin hankali,
sanyin hali ke gareta."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMAH*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_ )๐
Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)
*14*
12:30pm Abba ne zaune a Palo ya dawo daga office Mahmud zaune a gefensa yana shaida masa cewa Alhaji Atiku ya kirashi a waya akan cewa ya xama cikin shiri satin nan ya shirya kayansa ya sameshi Abuja domin sunansa ya fito zasu wuce wurin trening."
"Alhmdulillahi Abba yace,
Yana murmushi cike da jin dad'i da farin ciki, ya dubi Mahmud yace "Alhaji Atiku mutumin k'irkine abokina ne tare muka tashi mukayi makaranta d'aya dashi,
A rayuwata ta duniya bbu abunda Alhaji Atiku zai nema gareni banyi mashiba indai baifi k'arfinaba, saboda yanda yake nunamun k'aramci da k'auna."
Mahmud inaso idan kaje ka kula da kanka,
Kabishi sau da k'afa kayi mashi biyayya kamar yanda kasan kanayi mun Allah yayi mka Albarka."
Bai rufe bakinsaba fateema tashigo ko sallama bbu idonta yayi ja alamar taci kuka,har ta gaji."
Mahmud ya dubeta cike da kulawa yace "fateema meyasameki?"
Abba yace "ina Ummie take?"
Kafin tabasu amsa sukajiyo jiniyar motar 'yan sanda a k'ofar gida,
Saiga Baba maigadi yashigo da saurinsa ya zube k'asa gaban Abba yace "ranka ya dad'e 'yan sanda na sallama da kai a waje."
Abba ya zaro ido cike da mmki yace "yan sanda?"
Meyafaru?"
Mahmud shima hakan,
Fateema ta kuma fashewa da kuka tace "wlh sune,
Momy ta taso tashiga girgixata tana tambayarta "sune suwa?"
Meya faru?"
"Sune wad'anda suka kama dijama suka tafi da ita,
Mahmud yayi saurin juyowa ya kalleta, ya kuma kallon Abba da momy, yace "dijama tayi halinta kenan tajanyo mana fitina."
Suka d'unguma gaba d'ayansu suka fita,
Mahmud ke gaba sai Sauri yakeyi Abba na biye dashi snn momy da fateema."
Yana tukarar motar ya hango dijama zaune a bayan mota sai zarar ido takeyi"
'Yan sandan na ganin Abba sukayi saurin fitowa suna gaisuwa gareshi kasan cewar Abba ta fito takarar d'an majalisa na jahar