Showing 6001 words to 9000 words out of 44363 words
Chapter 3 - YAR GIDAN TSOHOWA Docment Complete Book .txt
to kasani yasanya mun ido, kullum sai ya dakeni
bansan abunda na tare mashi ba.
So nakeyi ka tsoratar dashi ya daina dukana, domin kuwa duk abunda yaga inayi sai ya sanya min ido, kuma ya dakeni."
Buba ya d'aga hannu
ya zunduma ashar yace "Alk'awari nayi duk Wanda ya tab'amun ke a garin nan sai nayi gunduwa gunduwa da namansa."
Dijama tadinga tsallen tana jin dad'i tace "yawwa Buba,
Amma karka dakeshi, karkayi mashi illah, kawai dai so nake ka tsoratar dashi saboda ya daina dukana."
Buba ya kuma b'arkewa da dariya ya na kuwa ya fadin "saini na dije "yar gidan tsohuwa kowa yatab'aki agarin nan bazai kwana lafiya ba,"
Dijama najin hakan ta dinga dariya tana zugashi
"Gaskiyar Buba sai kai na dije "yar gidan tsohuwa,
nan fa tadinga zugashi yanajin dad'i saboda mahaucin son da yake mta."
Sai kuwa yakeyi yana zage2
Ita kuma ta k'ara gaba tana cewa "sakarai wawa, waye zai auri d'an shaye2, tajuya ta hngeshi yayi nisa, taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki."
Wani gefen dad'i yacikata tana za a dakar mata yaya mahmud,haka dai har ta kai makarantar tasu",
Tana zuwa tasamu wuri a gefe d'aya ta zauna batare da ta tsokani kowaba
A Can ta dubi wani yaro ya hangame baki ya na bacci aiko tasanya hannun ta ta d'allamai baki sai da sauri ya bud'e idonshi yarik'e Baki yana kuka,
Anan take bakin nashi yayi tudu, ya kunbura."
Ta dubeshi tana dariya tace "yaro ubanka yajamaka tunda yana gani d'an taxi zai tafi dani amma ya kasa bada hak'uri sai dai yaja yayi tsaye yana kallonmu Dan haka nacire jin haushinsa a kanka."
Ta kuma matsawa gefe d'aya ta zauna,
ko wanne yaro yana zuwa afad'a masa karatu,
amma ban da ita, domin acewar ta kotaje an fad'a mata ba ganewa zatayi ba garama tayi zamanta",
Can itama sai tafara gyan gyad'i mlm dayaga tana bacci ya d'aga bulalar hannunshi ya doka mata a jiki, yana fad'in
" aikin ki kenan bacci, baki gane komai
mai kwanyar kifi keda jaki banga babban cin kuba,
Ai kuwa d'alibai suka d'auki yimata dariya,
ta hasala sosai taji haushi tashiga gun guni tana mgna k'asa k'asa,
Ni dai ban daiji metake fad'aba
Can ta nisa, tace mlm zanyi fitsari?
Yace "tashi kitafi dama aikin kenan daga kashi sai fitsari, ko aci akwanta, amma kai kam wayam ba komai acikinsa sai rashin kunya,
Da kuma majina, ya mere baki yace
"ALLAH dai ya kyauta."
Rab'awa tayi ta Wuce tagefen malam, ta dubeshi ta sakar masa murmushi,
Mlm kuma harara ya kuma wurga mata,
Hmm kun dai San dijama bata murmushin banza."
bata zarce ko inaba sai cikin wani kango dake nesa da makarantar kad'an a hankali tashiga kangon tana waige waige, can ta hango leda fara,
Ta duk'a ta d'auki ledar,
Can nesa kad'an ta hango ramin cinnaka tashiga tsinta tana zubawa a cikin ledar,
Tana tsinta tana fad'in
Yau zaka ci ubanka mlm ni zaka zaga har kasa ayimun dariya,hmmmmm yau kaima za'ayi maka dariya."
sai da ta tsinci mai isarta ta zuba a ledar, ta saki dariyar mugunta sannan ta mik'e tsaye. Ta fito,
hannunta goyo a bayanta sai da tazo kusa da mlm
Ya juya bayansa yana gayawa wad'ansu d'alibai karatu,
ta faki idonsa ta lallab'a a hankali saiti rigarsa ta d'aga ledar cinnakan ta zuba mashi cikin riga d'alibai na ganinta amma ba halin yin magana."
Dama sun san za'ayi hakan, tunda malam ya zageta, tayi shuru ta nuna alamar bata damuba,
Kowa yashiga mamakin "dijama ce za a zaga bata tankaba hmmmm, akwai wata a k'asa
Mlm da yaji anfara mintsinarshi, yafara sosawa,
tun yana Sosawa a hankali harya ya zabura ya mik'e tsaye nan fa yakama susar jikinsa da sauri
d'alibai me zasuyi inba dariyaba,
kuwa takeyi tana tsalle tana tab'i da hannunta tana dariya,
tasanya d'alibai najansa tana masu wak'a suna amsawa
Itake fad'in cinnaka yaci jeshi
Sunafad'in tashi kar ya k'arama
😅
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*6*
malm sai so she2_ yakeyi, yana hararar dijama had'ida da yimata dakuwa🖐🏿
har yakai sai da ya cire rigar sa, ganin cinnakun basu fita ba daga k'arshe ya tub'e wandon sa ya , yashiga kakkab'a ya koma daga shi sai gajeren wando."
Can saiga cinnaku suna fad'owa d'aya bayan d'aya."
tsaye yayi ya kasa magana yana sauke ajiyar zuciya,d'aya bayan d'aya
Yakasa d'aga ido ya dubi d'alibansa saboda kunya domin ya fahimci cewa duk shairin dijama ne."
Dijama tayi tsaye tana kallonshi tana dariya, ya dubeta da kyau cikin b'akin ciki da jin haushinta yace " dijama kitafi gida nakoreki karki k'ara zuwanmin mkrnta,
Ta b'arkewa da dariya had'ida rik'e ciki tana nunanshi tace
"toh saimi Dan ka Koreni,
ainaga kai kafara zagina ni kuma narama,
Harda yimin gorin ilimi, kuma ai naga shi ilimi Allah ke badashi nima ba Dan ya manta daniba,
Kuma ai naga itama 'yartaka jakace bata San komiba sai jakanci,kuma doluwa ce,
Idan ina da kwanyar kifi ita kuma kwanyar kwad'd'i ke gareta,
Ta k'are maganar had'ida mur gud'a baki, tayi tafiyarta."
Sai da tayi nisa da tafiya snn ta waigo a lokacin malma yana k'ok'arin maida kayan jikinsa tace "kuma sai naci uban Larai idan muka had'u rafi,
Tunda ka koreni, daga makarantarka, sann ta juya rik'e da Allonta, tayi tafiyarta."
Koda ta isa gida tana gunguni,
Tsohuwa ke tmbayarta lfy?
Meya dawo da ke gida ynzun?"
Idonta ya cika da hawaye tashiga fad'awa tsohuwa abunda yafaru tun daga farko hark'arshe saboda dijama duk rashin jinta bata k'arya."
Tsohuwa taja bakinta tayi shuru na minti goma, sannan tanisa tace "toh zauna kihuta, gaskiya dijama banji dad'in korarki da malam d'ahiru yayi ba."
To yanzu yazanyi? An koroki a mktantar boko, gashi yanxun islamiyar ma ankoroki.
gashi kuma ke ba k'ok'ariba,
allonki sai yayi wata ukku bakiyi wankiba, haka boko baki ganewa, to ni yanzun miye mafita?"
Dijama tayi shuru sai zarar ido takeyi Can taja dogon nishi tace
"yauwa tsohuwa tunda kinga baganewa nakeyi ba shawara kawai ki sanyani makarantar koyon sak'e sak'e, watak'ila a can nafara ganewa kinga saina koyi sak'a
dama nafison can."
Mahmud dake tsaye yana jinsu tun shigowarta me zaiyi inba dariyaba,
Yace kinko kawo shawara mai kyau, tunda da keda kwad'o bakuda wani banbanci,
Bako mai a k'wak'walwarki sai rashin kunya da gidadanci,
babu abunda kika iya, sai k'auyanci da jakanci takwalla me kan kifi me idanun mujiya." Idan har ba canxa hali kikayiba mki gama yawon makarantuba."
Murgud'a baki tayi cike da jin haushin kala mansa tace "sai naga ai kamar gado nayi a wurinka tunda kamarmu d'aya da kai."
Kuma k'wak'walwarmu d'aya,
kaga kuwa gareka na gada, yayi saurin ja da baya
yace wah?"
Ni ?Allah ya tsaren Dake."
Yana fad'ar hakan yayi waje abinsa domin ida yabiye mata zata hasalashi Dan yasan dijama badai bakiba."
Ai kuwa tsohuwa ta hau masifa, tana fad'in "da kake ce mata kwanyar kifi gareta ai dai 'yar uwarka CE, kuma jininka CE, ni dai bansan irin tsanar da kake yiwa dijamaba."
Mahmud baima San tsohuwa na masifaba yayi ficewarsa abunshi."
tafiya yakeyi yana dariyar dijama saboda rashin kunya da tayi mata yawa akai ita da kanta tasan bata gane karatu, kai Allah dai ya kyauta."
Yana shanye kwanan gidansu, bai ankaraba yaji ankwad'a masa sanda akai, waiga warda da zaiyi wa zaigani, Buba ne da yaransa sun zagayeshi suna shan taba."
Cike da mmki Mahmud yake kallonsu, zai bud'a baki yayi masu mgna suka kuma yunkurin kuma buga masa sandar a karo na biyu,
Hannunsa ya kara suka yashiga jujuwa yaron Buba ya yarb'ar dashi gefe d'aya,
nanfa danbe yakaure tsakaninsu."
Nanfa Mahmud ya shiga dukansu, baji ba gani
,duk suka zube warwas wasu kuma suka tsere a guje,
Daga cikin masu gudun harda Buba😅
D'aya daga cikinsu daya daku ya kasa iya gudu, Mahmud ya shak'o wuyanshi ya mak'areshi, yashiga tmbyarsa, "waye yasanya Ku?" Menamaku kukeso kuga bayana?"
Jinkinsa na rawa yace dijama ce tasanyamu."
"what dijama?" Yace cike da mamaki,
yanzu dijama bayan rashin kunya harda ta'addaci takeyi?"
Ya wurgar dashi gefe d'aya yayi tafiyarshi, zuciyarsa cike da bak'in ciki d mmki."
Haka ya koma gida Rigarsa rataye a kafad'arsa,
Yana shiga cikin gidan, ya ta rar da dijama tsakar gida zaune,
Tana ganinsa ta tashi da gudu ta tafad'a d'akin tsohuwa.
Baibi ta kantaba yayi shige warsa d'akinsa, yashiga har had'a kayansa, cikin akwati.
Saida ya d'auki komai nashi. Ya tallabo akwatinsa yafito."
Lokaci da yafito janye da akwati, yayi dai dai da fitowar
Tsohuwa daga band'aki ta dubeshi cike da mmki tace "Mamuda lafiya?" Ina zakaje da akwati?"
Mahmud ya dubi tsohuwa yace "gida zantafi tunda naga har anfara turomin "yan iska su dakeni
,watara na maganin b'era za a sanya min a abinci domin naci na mutu,
Dan haka tsohuwa kinga tafiyata sai wani lokacin."
Ya kai dubansa ga dijama dake zatsaye a bakin k'ofar d'aki, ta marairaice fuska,
duk bataji dad'in tafiyar da yace zaiyiba
, yace " toh meye kuma na tsayawa kina kallona?"
Zaki turosu ne su kuma tareni a hanya?",
.
Bata tanka masaba illah ta kuma sunkuyar da kanta k'asa,
, tashiga tunanin kaddai ace Buba sanyawa yayi aka daki yaya Mahmud."
Bai kuma bi takan kowaba ya Yakama hanya yayi tafiyarsa." Tsohuwa ta bishi da Addu'ar Allah ya tsareshi ya saukeshi lfy."
bayan fitarsa tsohuwa ta dubi dijama da kyau,
taga ba gaskiya a fuskarta tace dijama me ke faruwa da mahmud?"
Bata b'oyewa tsohuwa ko maiba tashiga bata lbr abunda yafaru."
Aikuwa tsohuwa tashiga yiwa dijama fad'a ta inda take shiga batanan take fitaba, fad'a takeyi sosai kamar ta daketa,
dijama bata tankaba illah turo baki takeyi."
*******************
*The following day*
Tsohuwa takira dijama domin ta aiketa,
Tafiya takeyi tana rawa a kan hannya tana d'an karkad'a k'ugunta,
Ta k'ofar gidansu Buba tabi inda suke zama suna majalisa,
ta hangosu ta d'aure fuska tayi kamar bata gansuba,
Sai da tazo daf dasu abokanansa sukace Baba ga mutuniyar can,
yana ganin takawo daf dasu ya wangame bakin sa da ya kunbura yayi suntum, yasha duka wurin mahmud."
yayi saurin tashi ya shiga gabanta yana fad'in "dijama ta sai ina hakan?" Ta d'aga kai ta dubeshi taga yanda labbansa suka sundume kamar ganda,
Bata San lkcin da ta tuntsire da dariya ba, tana nuna bakinsa da hannu, tana kuma dariya."
Muzanta Buba yayi,
Yashiga kallon kansa,
yaga metake yiwa dariya?"
Fahimta yayi da bakinshi take yiwa dariya ya, farajin haushi, amma kuma sai ya waske."
Ta kuma karkace kai tana kallonshi had'ida ya motsa fuska, kamar ba ita bace ke dariya yanzun,
Tace wai dama kai ragone?" Ina taurin naka yake wanda kake tsoratar da mutanen garin nan?"
Shin wai meyasa harka bari yaya mahmud yaji maka ciwo, lallema amma dai buba kabani mmki,
Ta kuma kallonshi ta tuntsire da dariya tace " toh Allah ya tsare gaba kaga tafiyata", ta barshi nan tsaye
Ta rab'ashi ta wuce, me abokansa zasuyi inba dariyaba, da suka tuna da gudun dasukaga yayi jiya."
Sukace gskya "oga munfaji kunya jiya wai ya akai hkan ta faru? Musamman kai oga duk kafimu gudu a nan take kashanye kwana,
Nanfa yafara k'uluwa. Ya dubesu ya doka masu tsawa idonsa sunrik'e zuwa launin ja."
Dijama nayin nisa snn tawaigo ta kallesa taga yana nan a inda ta barshi tsaye,
ta kuma b'arkewa da dariya ta d'aga murya ynda zaijita tace "amma dai Buba Kai wawa ne wlh da mace zatasanya kaci duka hka, tunda ma Nagano kai ragone na rantse bazan aurekaba, tun wuri ka nemi matar aure amma ba dijamaba ehe, tana kaiwa nan ta zuba a guje ta b'ace masa."
Aikuwa Buba ya k'ulu iya k'uluwa yashiga zage2, yana d'aga anda yana kirarinsu na 'yan tauri,
Had'ida borin kunya."
"Karya kike dijama na rantse da Allah Indai ina numfashi a garin nan bawani Wanda ya isa ya aureki saini, saini Buba na dijama yar gidan tsohuwa."
*wacece dijama*?" Waye Mahmud?"
Muje zuwa yanzun lbr yake ba'ayi komai ba."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
7⃣
Mahaifin Mahmud da mahaifin Dijama Hassan da Husaini ne,
Hakan suka tashi a tare duk abunda zasuyi a tare sukeyinsa, har sha'awa suke bawa mutanen k'auyen Tofa dake cikin k'aramar hukumar Kano."
Hassan da Husaini sun taso cikin so da k'auna da kulawa a wurin mahaifansu, Malam Adamu da Hadiza,
Wanda a yanzun jikokinsu suka canxa masu suna suka mayar dasu tsohuwa da Kaka
Babu wani Abu dake raba Hassan da Husaini,
ako da yaushe suna tare da juna, a cewarsu a yanda suka fito tare sun d'aukarwa Kansu Alk'awarin baxasu tab'a rabewa ba."
Tun haihuwar Hassan da Hussaini tsohohuwa bata kuma k'ara samun haihuwa ba, wannan dalilin yasa suka d'auki son duniyar nan suka d'orashi a Kansu."
K'auyen Tofa k'auye ne mai tattare da Ni'ima da wadatuwa. Da kuma yalwar makarantun boka dana islama."
Wannan dalilin yasa mlm Adamu ya tashi tsaye tsayen daka domin ganin Hassan da Husaini sun samu ilimi boko dana Islama, kasan cewar mlm Adamu manomi ne, akwaishi da wadatar zuci, da son yaga ya wadatar da iyalinshi batareda sun gani a wani gidan ba."
Hakan kuwa akayi suntashi cikin hazak'a da k'ok'ari Wanda gaba d'aya k'auyen na Tofa, suna Alfahari dasu, suka zama abun sha'awa da kwatance."
Akwana a tashi har suka kammala karatunsu na _secondary_ har suka tafi Jami'ar Bayaro _university_ dake cikin garin Kano."
Shigarsu jami'a ra'ayinsu yarafa banbanta a wurin karatu domin Hassan _Business_ yakeson karanta, shi kuma husaini _mass_ _communication_ yake son ya karanta."
Hakan suka Amincewa junansu amma kuma duk da hakan a cikin mkrantar a tare suke kwana a tare sukecin abinci,
idan har ba saninsu kayiba bzaka tattace Waye hassan ba waye husainiba."
Hakan sukayi karantunsu cikin Aminci da soyayyar juna tare da taimakon mahaifinsu har sukayi masters."
Allah ya taimakeso suka fito da sakamako mai kyau,
Nan take har rugogowar d'aukarsu aiki akeyi."
Hassan aiki baya gabansa yafi ganewa kasuwanci domin tun kafin takardunsu su fito har ya bud'a d'an karamin shago a k'ofar gidansu yana sayarda atamfofi da shamdodi da takalma, wadda yin hakan harda taimakakon mahaifin nasu."
Wani babban kamfani ne na sarrafa motoci, dake cikin garin Kano a can Hassan yasamu aiki inda ya samu matsayin manager campanin za'a dinga yimashi Albashi mai tsoka." murna a wurin mahaifan nasu da kuma d'an uwan nashi Husaini abun ba'a mgna
Bayan kwana biyu da faruwar hakan, garin Lagos suka d'auki Husaini aiki a gidan TV na garin Lagos, inda shima suka bashi babban muk'ami."
Hmmmm Hassan Husaina sunyi bak'in ciki sosai da rashin samun aikin da basuyiba a gari d'aya, inda suka buga Kansu da k'asa sukace sun fasa yin aikin indai ba gari d'aya suka samuba.".
Tsohuwa da Kaka suka Shiga lallashinsu suna basu hak'uri a kan cewa rabuwar aikinsu ai bashine rabuwarsu ba, kuma ai ba'a can zasu dawwamaba."
Da kyar a ka samu suka hak'ura had'ida yiwa junansu Addu'a."
Ranar da zasu fara tafiya wurin aiki, ko wannensu ya shirya kayanshi a akwatinsa,
sunja wuri d'aya sun zauna suka rungume junansu ko wanne idonshi ya cika da hawayen rabuwar da zasuyi."
Tsohuwa da Kaka dake tsaye a tsakar gida suna