Showing 3001 words to 6000 words out of 44363 words
Chapter 2 - YAR GIDAN TSOHOWA Docment Complete Book .txt
baki yafeba."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMA*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_๐
)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*3*
Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school."
Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue
ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta,
ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta."
tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi."
Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya,
Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti."
Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita."
Saida ta kai k'ofar gida,
Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta,
Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki."
Wa zata gani yaya Mahmud ne,
ya juya bayansa yana wanka,
ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando,
Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje."
Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin,
ransa yayi matuk'ar b'aci
Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando."
Gudu take falfalawa kamar filfilwa,
bata zame a ko inaba sai makarantarsu,
Da shigarta makarantar ta cikin,
Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi,
Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji."
Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa,
kai tsaye ajinsu ya nufa,
ya tarar da ita zaune a kan kujerarta,
Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita,
koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane,
idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya."
Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta
yace "ke dijama fito nan waje,
Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji,
Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai."
Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba,
Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?"
sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni."
Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar."
Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga,
kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane.
Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta,
amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido."
Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska,
ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa."
Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki,
amma ina ta cimuimuyeshi tana ihu tana fad'in
"wlh bazan fitoba."
Suna hakan Allah yakawo malam mudi,
Yashiga tmbyar mlm sani abun da kefaruwa?"
ganin ya had'a zufa sai jujuwa shi akeyi, bai samu damar bud'e baki yayi maganaba illah yyi mashi da hannu zuwa cikin rigarshi."
Aikuwa malan mudi yana lek'awa ya hango dijama ta cimuimuyeshi sai ihu takeyi, da kyar aka samu aka b'anb'ari dijama a jikin malam sani, sai nishi yakeyi kamar wanda yayi wasan tseren gudu."
Ai kowa yana samu ancire mashi ita,
bai kuma bi takan kowa ba yafita daga ajin da saurinshi,
.dijama kuma na gefe d'aya tsugunne sai zarar ido takeyi tana turo bki cike da tsiwa,
malam mudi yace "tashi kiwuce kitafi gida na koreki daga nakarantata sai kinzo da mahaifinki."
Da sauri ta mik'e tsaye,
Tana magana k'asa k'asa tana cewa "to sai me?"
Kuma wlh duk nakama salihu sainayi mashi shegen dukan tsiya tunda har ka koreni makaranta."
Salihu babban d'an malm mudi ne Wanda yake duk sa'a nine da dijama, tana kaiwa nan tafita waje tayi tafiyarta."
Malm mudi dake tsaye yaji duk abunda tace yace "to idan kika kamashi karki barshi da rai kikashe kinji
, kaji min hatsabibiyar yarinya."
Tafiya takeyi akan titi duk inda taga mota ajiye
saita lek'a kanta ta glass d'in motar ta hango abunda ke cikin motar sannan ta k'ara gaba."
A can taci Karo da yan taxi su biyu suna rigimar fasinja a tsakaninsu, tsayawa tayi tana kallonsu, sai da ta fahimci a kan abunda suke yiwa fad'a,
sannan ta k'arasa wurinsu ta rik'o rigar d'aya daga cikinsu wadda ya fahimci yafi fitina,
Tace "yayana ina kwana, harda 'dan runsunawarta, kamar ta Allah, kallon rashin sani yayi mata cike da jin haushi yace "waye yayan naki?" Ke wai daga ina?" A ina kika sanni?"
Tace "yi hak'uri dama turoni akayi daga gida akace idan naga mai taxi nakirashi domin, yayana ne zaiyi tafiya xuwa kano kuma bayason zuwa tasha shiga mota saboda baya son jira,
gaba d'aya zai d'auki shatar mota domin ta kaishi har k'ofar gida,
kud'ine gareshi sosai."
Mai taxi yanajin hakan ya kyale abokin fad'an nashi ya maida hankalinshi a wurin dijama, yace 'a wace unguwa gidan naku yake?"
Tanuna masa hanya tace "can gaba kad'an bama da nisa sosai."
Yace "yawwa 'yar Albarka shiga mota mutafi,
Girgiza kai tayi,tace "tsohuwa ta hanani shiga mutar mutane saboda kar'a saceni."
Mai taxi da yake yaji maganar kud'i yace "to kishiga gaba kawai saiki dinga nuna min hanya."
"To tace had'ida shigewa gaba, tana tafiya."
Tana gaba d'an taxi na bayanya biye da ita, duk inda ya gifta mata matafiya sai tarenshi akeyi yana girgiza kai alamar ba aiki yakeyi ba dijama kawai yake biya."
Sunzo kwanar da zata sadasu da gidansu,
yara sunyi tsaye tsaye, a bakin hanya,
tashiga kore yaran da hannu tana fad'in "kugafara nan ga mota nan zata shigo, kujanye daga nan."
Tsofaffin unguwa da samari,
kowa sai kallonta yakeyi yana mmki,
yana kuma kallon mai taxi din dake biyeta da ita,
yana k'ok'arin shigowa kwana."
Tabb!!!
su furta had'ida rik'e baki๐ค
Suka ce, yau kuma wannan hatsabibiyar yarinya mai taxi ta janyo mana?"
Ido kowa ya bita dashi saboda ba damar ayi mata magana cibi ya zama k'ari,
Domin duk wanda yayi mgna da zarar d'ansa yafito waje,
Idan ta rik'ashi sai tayi mashi shegen duka tsiya, tace "babanka ne janyo maka, idan ka koma gida kafad'a mashi ya daina sanya min ido."
Wnn dalilin yasa kowane mutum sai dai yasanya mta ido."๐
Da kyar d'an taxi yasamu yashiga kwanar,
saboda rashin kyawon hanyar, a ransa yana danasanin biyo ta da yyi,
amma kuma idan ya tuna da shata 'a ka d'aukeshi sai ya d'anji sanyi yyi murmushi yaji dad'i."
Suna zuwa daf da k'ofar gidansu ta hango yaya mahmud zaune a kan dakali,
Gabanta ne yanke ya fad'i data tuna da shigarda tayi a b'and'a ta iskoshi."
Taja dogon nishi, tace "to shi kuma wancan mugun ko zaman me yakeyi a waje?"
Shima Mahmud d'in zaman da yayi, a nan zaman jiranta ne
har zuwa lokacin da zata dawo daga makaranta,
domin yau babu Wanda ya isa ya hana yaci ubnta."
D'an taxi na zuwa sai ti k'ofar gidan tashiga d'aga masa hannu tana fad'in wait wait ya isa ga gidan nan."
Dan taxi yaja burki ya tsaya had'ida sauke ajiyar zuciya wahalar da yasha wurin shigowa wannan hanyar."
Mahmud na ganin hakan ya cika da mmki da Alajabi ya tashi tsam yashiga gida, yana mmkin dijama ko dai Aljanu sun shegeta ne?"
Tsohuwa tashiga dokawa kira tun a waje,
tsohuwa dake kishingid'e tana gyangyad'i, jin muryar dijama yasa tayi saurin bud'e idonta had'ida kai idonta ga dibon agogo,
Mmki tashigayi ganin lokacin tashinsu daga mkranta baiyi ba."
Kai tsaye ta fad'a kan jikin tsohuwa tana fad'in wash Allah tsohuwa nagaji."
Tsohuwa tace "dijama meya dawo dake gida yanzun, bayan nadiba agogo na ga lokacin tashinku daga mkrsnta baiyi ba."
Ta turo baki idonta ya cika da hawaye tace "wai malam Mudi ne yace ya koreni a mkrantar gaba d'aya,
wai sainazo da mahaifina."
Kuma na rantse da Allah tunda ya koreni, duk nakama d'ansa Salihu sainayi mashi dukan tsiya."
Tsohuwa ta rabka sallalami, tace "ya koreki mekikayi mashi?"
"Wai saboda kawai nayi latti ."
Tsohuwa zata kuma yin magana taji ana rangad'a orda da mota a waje ba kafkaftawa, duk a rud'a mata kunne."
Sai kuma ga yaro yashigo yana fad'in wai a waje wani mai mota yace yana kiran dijama."
Tayi sauri ta fito da kayan sauri yakeyi."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMA*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_๐
)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*4*
Tsohuwa ta juya ta dubi Deejama, itama Deejama tsohuwa take kallo."
Tsohuwa tace dijama a ina kika samo mai mota kuma?" Sann Wad'anne kaya ne naji ance kiyi sauri kifito dasu?"
Dijama ta turo baki cikin shagwab'a tace "yaya Mahmud ne nasamowa mota, domin ya kwashi kayansa yayi tafiyarshi garinsu, saboda nagaji da zaman da yakeyi a gidan nan kullum sai ya zalunceni,
Ko kuma ya dokeni."
Tsohuwa tayi tagumi๐ค tace "dijama waye yasanyaki ki taro motar mutane, shin kinada labarin cewa direbobi wasunsu basu da mutunci?"
Ai kuwa bata rufe bakiba taji ankuma danna wata irin orda da k'arfi,
had'ida dukan k'ofar gidan iya k'arfinsa,
sai da tsohuwa da dijama suka razana."
Da sauri tsohuwa ta mik'e tsaye ta janyo mayafinta had'ida Sanya talkaminta, ta dubi dijama tace "karki kuskura kifito, kibari nafara tafiya na bashi hak'uri, har musamu yayi tafiyarshi,
amma dai yau dijama kin janyo mana fitina da bala'i 'yan taxi."
Duk abunda akeyi mahmud yana d'akinshi yanaji bai fitoba, jira yakeyi a k'are da d'an taxi, ya rik'ata yaci ubnta, la'ada waje."
Tsohuwa tafita waje ta tarar da mutane sunyi cincirindo manya da yara, kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama, suna fad'in indai dijama ce har abunda yafi wannan zata iya aikatawa."
D'an taxi na ganin tsohuwa ta fito, yabita da kallo ya nufo wurinta, yana fad'in "tsohuwa fito min da yarinyar gidanki,
yau na rantse da Allah tunda iskancinta ya kawo kaina, to ta kai k'arshen rashin kunya, domin ni a tasha nake kwana."
yau zanyi mgnin rashin kunyar da takeyiwa mutanen garin."
yanxun nan a bakin mutanen unguwa, nkejin labarinta tsaf, to tunda rashin kunyarki takawo gareni tazo k'ashe."
Tsohuwa tashiga bashi hak'uri. Tana masifa da mutanen unguwa tana fad'in "dama tasani an dad'e da tsanar dijama a garin nan to ta Allah batasu ba, kuma bazasu iya komai da dijama ba."
D'an taxi shima sai ruwan masifa yakeyi yana dukan mota yana fad'in bazai bar unguwar nan ba sai yayiwa dijama shegen dukan tsiya,
ko kuma a biyashi kud'in mansa da ya k'one wurin shigowa wannan unguwar."
Mahmud dake d'akinshi zaune yanajin duk abunda kefaruwa ganin fad'an ba mai k'arewa bane, yasashi fitowa, yanufi cikin gida kai tsaye d'akin tsohowa ya shiga ya tarar da dijama zaune a kan kujera abincinta kawai takeci, hnkalinta kwance."
Ganin Mahmud da tayi yashigo ya sanyata sakin kwanon abincin had'ida zaro ido waje cike da tsoro,
Tun kafin yakai wurinta tashiga matsar hawaye tana fad'in "dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba."
Dank'ota yayi yashiga kwad'a mata mari yana dukanta, dama yana da takaicinta,
Dukanta yakeyi ba girma ba arziki, sai ihu takeyi, tana neman tsira,
sannan daga k'arshe ya rik'a hannunta yafito da ita,
Yana jayen da ita yanufi k'ofar gida da ita, kai tsaye d'an taxi ya mik'awa ita yace "gata kaci ubnta, idan da hali dan Allah katafi da ita, domin ko mu kanmu ta addabemu ta zamar mana fitina."
D'an taxi ya rik'e hannun dijama yana Neman ya turata a mota,
Dijama ta kurma ihu tana fad'in nashiga uku tsohuwa kina gani d'an yankan kai zai tafi dani?'
Tsohuwa tayo kansa tana masifa ta rik'e hannun dijama tace "na rantse da Allah ba inda zakaje min da yarinya."
Nawane kud'in manka?"
kafad'i ko nawa ne sai na biyaka."
D'an taxi yayi murmushi yace "dubu biyu ne tsohuwa."
Tsohuwa ta kama bakin zanenta ta kwanto dubu biyu ta mik'awa d'an taxi.
Sannan ta janyo hannun dijama had'ida wurgawa mahmud harara."
D'an taxi yace "kin fanshi jikanyarki tsohuwa, amma kija mata kunne Dan na rantse banda darajar wannan mutumin,
ya nuna Mahmud dake tsaye
da konawa kika biyani sai nayi mata dukan tsiya a wurin nan kafin na kyaleta."
Dijama ta dubeshi cike da tsewa tace "mudai Dan Allah karka cika mana kunne da suruto tunda anbiyaka kud'inka sai kaja akwalar motarka kabar mana k'ofar gida."
Ta d'aga kai ta dubi tsofafin da suka zagayesu suna kallonsu ko hak'uri bazasu iya bayarwa ba,
Ta girgiza kai tace "duk wad'anda ke wurin nan babba da yaro duk na ganku, zamu had'e daku,"
Sunajin hakan kowa ya watse ya kama gabansa, saboda sanin halinta, d'iyansu da jikokinsu bazasu zauna lafiya ba, wurin dijama."
D'an taxi yaja motarsa yayi tafiyarsa,
Tsohuwa taja hannun dijama suka nufi cikin gida."
Mahmud na ganin hakan ya fasa shiga cikin gidan saboda masifar tsohuwa shima ya kama gabansa."
Tabarma tsohuwa ta d'auko ta shinfid'a mata a k'ofar d'aki, tana jera mata sannu had'ida yimata fifita inda Mahmud ya daketa wurin duk yayi kwancin bulala gashi Abu ga farin mutum."
Tsohuwa ranta yakai k'ololuwa wurin b'aci sai masifa takeyi tana fad'in bari mamuda d'in ya shigo, yazo ya had'a kayanshi yayi yafiyarshi gidansu, ni banga amfanin tahowar nan tashiba, tunda yazo garin nan kullum cikin d'aga maki hankali yake."
Dijama ta kuma marairaicewa sai nishi takeyi kamar Wanda zata mutuwa."
Wasa wasa jikin dijama ya d'auki zafi alamar zazzab'i yakeson rufeta,
Hankalin tsohuwa ya kuma tashi ta mik'e tsaye tashiga d'aki ta d'auko mata maganin zazzab'i ta k'ak'k'are mata tabata tasha, sannan barci mai nauyi ya d'auketa."
Yinin ranar dijama ko k'ofar gida bata fitaba, jinya tajeyi."
Sai bayan sallar isha'i Mahmud ya dawo, gidan
Da sallama yashigo ya,Tarar da tsohuwa zauna,
K'asa k'asa ta amsa mashi had'ida kauda idonta gefe d'aya hushi takeyi dashi."
Murmushi yayi had'ida girgiza kai domin yasan za'ayi hakan tunda ya tab'a 'yar gidan tsohuwa."
Ya kuma kallon tsohuwa yace " 'yar tsohuwa hushi kikeyi da namijin naki, to kwantar da hankalinki na kusan tattara kayana na barmaku garinku nayi tafiyata gidanmu"
Yana kaiwa nan ya d'auki buta ya Shige ban d'aki."
Fitowar da zaiyi sukayi ido biyu da dijama dake kwance a gefen tsohuwa,
ta tsura mashi ido. Tanatana kallonshi
Ajiye butarshi kenan yaji ta saki dariya harda rik'e ciki tana kallonshi tana kallon k'ofar b'an d'aki."
Sai ta dubeshi ta dubi ban d'aki ta kuma b'arkewa da dariya.'
Anan take ya fahimci abunda take yiwa dariya, wato d'azun da ta iskoshi yana wanka, kenan
To metake yiwa dariya?"
Duk haushi ya kamashi yaji kamar yaje yasameta yayi ta dukanta amma ba hali, tsohuwa bazata bariba."
Amma kafin ya bar garin nan sai ya koya mata hankali, sannan yayi tafiyarshi."
Washe gari dijama taji sauk'i, sosai
Tafiya takeyi D'auke da allonta zataje makarantar islamiya ta d'ora allonta akai ta sha d'amara da gyalenta a k'ugunta,
Tafiya takeyi tana rera wak'arta tana rawa a kan hnya."
Karo taci da Salihu d'an mlam Mudi, Wanda ya koreta a makarantar boko,
Ta ajiye allonta a gefe d'aya,
tasha gabanshi yana d'auke da markad'en kayan miya a Kansa, ta ture markad'en ya zube,
Tace "yawwa wana nakama?"
Aidama nacewa babanka duk na kamaka sainayi maka duka, tunda har ya koreni a makaranta.
Ai kuwa ta kamashi da kokawa, saida tayi mashi dukan tsiya,
Sannan ya duk'a ya d'auki robar markad'ansa yanufi gida yana kuka."
Dijama kenan, ita ba girma garetaba sai fitina, kwata kwata shekararta goma sha hud'u a duniya."
Sai da taga yayi nisa yana tafiya yana kuka sann ta d'auki allonta tanufi mkranta."
Gafda zata isa makarantarsu
Ta kuma cin karo da Buba d'and'an mai gari tare da tawagarsa 'yan tauri."
Buba d'an maigari kowa a cikin garin tsoronsa yakeyi, Domin ya kama mutum yayi masa duka saiya karkayashi ba wani abun bane gareshi."
Allah ya d'ora mashi son dijama saboda hatsabibancinta da k'arfin hali irin nata, bugu da k'ari tafi duk 'yan matan garin kyawo."
Gabanta ya Tara, yayiwa yaransa nuni da hannu da suyi tafiyarsu zaiyi magana da masoyiyarshi."
Ita kuma dijama a duniya babu Wanda ta tsana kamar Buba, saboda shaye shayen da yakeyi, bata son ganin fuskarshi ko kad'an."
Buba ya bud'e baki yana dariya bak'ak'en hak'oransa da sukayi bak'i suka dafe wurin shan sigari๐ค suka bayyana,
Yace "dijama 'yar gidan tsohuwa matar buba duk Wanda ya tab'aki a garin nan zanci........
Murmushi tayi masa Wanda bata tab'a yimasa ba,
Domin tasamu wata dama da zata sanya buba ya rama mata dukanta da yaya mahmud yayi mata jiya."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: ๐น *DEEJAMA*๐น
( _'Yar gidan tsohuwa_๐
)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*5*
Ganin murmushin da takeyi ne, a kan fuskarta
ya kuma bawa Buba damar k'ara bud'e baki yana dariya,
Yace "dijama ki amince dani naturo magabatana a d'aura mana aure."
Dijama najin hakan ta had'e fuska had'ida ya tsine baki,
Ta dubeshi da kyau tace "Buba kanaso nadinga kulaka?" Har na aureka?"
Buba yace "abunda nake fata kenan dijamata."
Ta karkace kai tace "kasan bak'on da yazo gidanmu?"
Buba yace "mahmud kike nufi?"
Tace "kwarai kuwa,