Showing 9001 words to 12000 words out of 38424 words

Chapter 4 - Surbajo Book Complete document by Zahra Muhammad Mahmud .txt

santafa
faraace takaru afuskokinsu inda daddy yace Kai alhdllh
wacece
surbajo yabasu amsa gabadaya sukasamasa dariya
mommy tace ikon Allah tagida ma kana fama ina zaka iya da
shirmen surbajo ban hanakaba amma Allah yasanya alkhairi
Kai kaji kagani
daddy da tun dazu dariya yake seyanzu yace aminullahi na yar
fillo to iyayenta sunsan dazancan
aa yabasu amsa inade so daddy kaje kanemarmin aurannata
badamuwa aminullahi daddy yafadi yana dariya
sallama yamusu yatafi Dan dama yakosa sugama magana
yatafi Dan surbajo yakeson gani
yana fitowa yadauki hanyar makarfi shikadai dan bako inane
yakeson excode Dinshi subishiba bare irin wannan tafiyar
tazuwa yada manufa 😜
da azahar yaiso garin makarfi lokacin surbajo taje yo icce
parking yayi akofar gidan dayake yau larabace mazan gidan
suntafi cin kasuwa Dan kasuwar makarfi ranar laraba take ci
surbajo ce tashawo kwana da iccen datayo akanta kamar
amafarki taganshi atsaye ajikin motarshi
habawa xubar da iccen tayi ta runtuma da gudu gurinshi Tana
zuwa rigarshi takama Tana fadin yauwa wana Kama ay dama
nafadi aradu nakamaka sekaji jiki gashiko yau kaida kanka ka
kawo kanka har gida tabadi Tana kokarin gyara damararta da
hannunta daya daya kuma Tana rike dashi Dan kar yagudu
shiko alameen dariya abun yabashi Dan yasan zaa rina
surbajo dataga yana dariya naushi ta dirka masa aciki sannan
tacigaba da kaimishi duka takoina ba abinda keba alameen
dariya seganin itace ke dukan Amman itace ke kuka Tana
aradu Seka bani kudina bazan yardaba gashi dukan datakeyi
ko zafi babu kamar badukannasa takeyiba
be hanataba seda tagaji Dan kanta sannan takyaleshi Tana
haki
sannu alameen yamata yana dariya yace ammafa kinsha ayki
dagowa tayi da jajayen idanuwanta datasha kuka tace jiki
kamar karfe dukanka nakeyi amma ninakejin zafi aradu
senamaka abinda koda wasa akace ka kuma yimin rashin
kunya bazaka kumaba tafadi harda nunashi da hannu shide
binta kawai yake da ido yayinda gefe daya kuma yana
daukarta awayarshi
shigewa gida tayi Takai iccen sannan tadawo ga mamakinsa
tsugunnawa tayi agabanshi tanacewa Dan Allah kado kayi
hakuri kabani kudina aradu nasha kuka sabida kudina daka
gudu dashi danhaka seka karamin akan nera gomata kaji
kado
murmushi yayi sannan yace naji zanbaki kuma zan karamiki
akan nakin tonikuma dukan dakikamin anawa dannima biyana
zakiyi inba hakaba inje inkiramiki sojoji sukamaki
akidime surbajo tamike Tana shirin guduwa jin yaambaci
sojoji rukota yayi dasauri yace ina zaki muna magana kuma
cikin barin jiki tace aradu nayafemaka kudin kuma Don Allah
karka kiramin wainnan mugayen mutanan niko ganinsu
banaso yin sabida nataba ganin yadda sukayiwa wani mutumi
dukan tsiya akasuwa suka ciremishi kaya aradu mutumin
yabani tausayi Danhaka kayafemin aradu bazan kumaba
ganin ta tsoratane yasa alameen kwantar mata da hankali
tahanyar cewa haba surbajo ayko nakirasu bazasu iya yimiki
komaiba sabida kyanki
ay surbajo najin haka tahau dariya sannan tace dagaske
kakeyi basa Kama mekyau
ehmana dagaske nakeyi
kwace hannunta tayi daga rukon dayamata sannan tace to
aradu nafasa yafemaka kudina seka bayani
dariya alameen yayi yace ayko bazan bakiba sabida ke kikace
kin yafemin
kallonshi surbajo tayi sannan tace zaka biyanine tun biya nada
dadi
sunanan Ardo yadawo dafaraarsa ya tarbi alameen Yayinda
yarufe surbajo da fadan meyasa bata kawomasa ruwa da
shimfidaba alameen ne yace nine nace tabarshi base
takawoba
sannan Ardo yadena fadan
mamakine yarufe surbajo tace a zuciyarta hoddijan aradu
kado ko a makaryata shinadabanne kato dashi amma baya
kunyar karya
cikin gida ardo yaja alameen suka zauna suna hira
sato jiki surbajo tayi tafito inda motarshi take tsinke tasa
acikin tayoyin tasacemusu iska gabadaya Tana gamawa ta
ruga gidansu arera Tana dariyar mugunta ita atunaninta hakan
datayi baze Hana. motor tafiyaba sede yahanata yin sauri
dalilin dayasa tasacemishi iskar kenan
alameen hira tayi dadi Shina Shida Ardo besan magaruba
takusaba seda yakalli agogon hannunshi mikewa yayi domin
tafiya ardo nata samishi albarka kyauta yayiwa ardo metsoka
sannan yafito daga gidan tsayawa yayi yana waigen ta ina ze
hango cartoon dinsa tazo suyi sallama amma be hangotaba
ardo yace aykawai kayi tafiyarka inde surbajoce takai takwas
nadare bata dawoba tanacan suna wasa da saointa
bahaka alameen yasoba Amman bashida zabin dayawuce
yatafi sabida dare yafara Yi ga hadari yahadu sosai
shiga motarsa yayi batare daya Lura da barnar da surbajo
tamasaba seda yakunna motar security dake jikin motar
yafara kara alamun akwai Matsala amotar fitowa yayi
danganin meyasami motar
innalillahi wainna ilaihi rajuun ita kawai yake maimaitawa
ganin tayoyin motarshi a sace kobaa fada masaba yasan
aykin surbajone dafe kanshi kawai yayi yana kallon motar
yama rasa abinyi dama daya tasace dase yadauko spare din
tayar dake boot yasa to duka hudunne gashi garin ko mashin
babu me ita bare asamu Mesa iska wayarsa yadauko babu
network sam
kamin yagama yanke abinyi ruwan sama yafara sakkowa
ardone yakaraso kusa dashi yace Aminu akwai matsalane
kai yadagamasa sannan yamasa bayanin abinda yafaru da
motar amma befada masa surbajo ce tamasa ba Dan yasan
tsaf ze iya Zaneta
suna nan tsaye ruwan yakarasa tsugewa kamar da bakin
kwarya dasauri ardo yajashi zuwa wata bukka wacce dama
anyitane sabida baki
zama yayi akan gadon karan dake ajiye adakin ardone yajawo
kofar bukkar yakare wacce take ajiye agefe itama takarace
sunanan zaune ruwan betsayaba se misalin bakwai da Rabi
nadare
ruwan alwala ardo yaje yakawomasa yayi alwala yay sallah
sannan ardo yakawomasa barguna guda biyu da fitilar aci
balbal yace gashi yashimfida daya yarufa da daya yayi hkr
yakwana anan inyaso gobe da safe ardon zeje cikin gari yakira
mesa iskar yasamasa
alameen bakinciki yagama rufeshi bakomai yake bashi
haushiba se irin yadda ze kwana Abukka batare da wani
tsaroba ko kofar arziki babu ga sanyi daaka fara kamar jaura
tawuce shiyama zeyine gurin bacci akan gadon kara amma ya
yaiya bashida zabin daya wuce hakan
komawa motarshi yayi yadauko bindigarshi da touch light
Wanda yaajiye amotar sabida tsaro
surbajo se takwas tanufo gida itadasu arera dasuka rakota
tabayan gida tashigo gidan Dan haka batasan alameen
betafiba alwala tayi sallah sannan tafara tunanin oh kado
koyaje gida yanzu oho sumayece takirata tace tazo takaiwa
bako abinci yana dakin baki mamakine yakamata nayaushe
sukayi bakon daukar abinci tayi tuwan dawane da miyar kuka
danya yasha manshanu Wanda aka zuba a akushi na
musamman tanufi bukkar bakin dayake motor alameen
bakace kuma akasan bishiyar mangwaro yayi parking dinta
surbajo bata Lura da itaba sallama tayi kofar bukkar daga ciki
aka amsa shiga tayi taajiye kwanon abincin tajuya zata fito
fisgota yayi da karfi tafada jikinshi zata samasa ihu yarufe
bakin da hannunshi haska Mata fuskarshi yayi sannan
yasakarmata baki arude tace kado meya hanaka tafiya gida
kallonta yayi sannan yace haba surbajo meyasa Zaki sacemin
iskar tayakinsan motar kuma bazata tafiba inba iska
tausayinsane yakamata hawayene suka fara zubowa daga
idonta cikin kuka tace Dan Allah kado kayi hkr aradu bansan
motor bazata tafiba nadauka saurine bazatayiba Dan Allah
kayafemin nasa Zaka kwana a inda baka saba
tausayinta alameen yaji amma hakan baze hanashi hukuntata
ba danyayi alkawarin yimata hukunci bindigarsa yazaro ya
saitata kan surbajo
Maman Yusuf
[3/18, 14:09] Zahra muhd mahmudπŸ’ƒ: πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
*SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
Zahra Muhammad mahmud
*ina barar adduarku gobe in Allah yakaimu zanyi tafiya so
atayani da addua inje Lafiya in dawo Lfy Wanda nataba
batawa rai pls agafarceni nima nayafema kowa ngd*
*page 19-20*
Surbajo idanuwantane suka fito kurukuru ganin bindigar datayi
jikinta sebari yake
Alameen yace umarni zanbaki inkika kuskura kika ki bi sena
harbeki yafada in a serious talk
Girgizamasa kai yakeyi alamar tayarda
Cigaba yayi da magana yace surbajo yau kinbatamin raina
sosai so dole ne nahukuntaki Dede da iri laifin dakikamin
Don Allah kado kayi hakuri aradu bazansakeba
Tsawa yadakamata wacce ta tilastata yin shuru jikinta nabari
Kara matso da bindigar alameen yayi dede goshinta aytuni
fitsarin datake rikewa ya kubce alameen seji yayi yajike da
fitsari bedamuba yacigaba da cewa
umarnina shine zan aureki ko kinaso kobakyaso kuma idan
kika sake kika nuna cewa nina tilasta miki aurena harbeki
zanyi
surbajo wacce tunda yafara magana numfashinta ke
barazanar daukewa dakyar tace Don Allah kado kayi hkr inada
Wanda nakeso kumashi zan aura
Bigemata baki yayi yace ay ba raayinki nakeson jiba umarni
nabaki kuma dole kibi inkinki ko dagake har Jaen sena
harbeku
Jikintane yakama Bari kamar mejin sanyi tace kayi hkr Don
Allah karka kashemini jae aradu naamince zan aureka
Wani malalacin murmushi alameen yasaki alamun samun
nasara cikin ruwan sanyi
alameen bekyale surbajo tatafiba seda yagama tsoratata
sannan yace tawuce
da gudu tafito tayi cikin gida kamin takai cikin gidan tafadi
yafi so uku sabida agigice take koda tashigo Kowa yashige
dakinsa sabida sanyin daakeyi itama nata dakin tashige
wutar jin dumi ta tarar sumaye takaimata dakin ga kuma
abincinta a akushi
Gaban wutar taje tazauna bayan ta karo kofar dakin
kuka tashigayi Mara sauti duk da tabon daya bata mata kaya
bata damu taciresuba
ita kawai tunaninta alameen Dan fashine Dan inba Dan fashiba
baabinda zekawo bindiga gurinsa itayau yazatayi da rayuwarta
Ashe Dama basuda rabon aure da jae gaskiya kado mugune
Allah seya sakamana tafadi Tana cigaba dakukanta
Wanda babu mesharemata
ranar azaune surbajo takwana kowanne motsi akunnanta Dan
tsoro takeji takwanta kado yazo ya harbeta
Shima alameen Tana fita ruwa yadiba yasa ajikinsa inda
fitsarinta yashafa sannan yaci abinci data kawomasa gaskiya
yaji dadin abincin ruwa yasha sannan yakwanta badan yayi
bacciba seda yaji dadin tuno dramarsa da surbajo juyi kawai
yake yana murmushin jindadin gano surbajo nada tsoro dayayi
ayko yasamu abinyi shima ranar beyi bacciba
da sassafe ardo yaje cikin gari nemo mesa iska yaci wuya
kamin yasamu Wanda yaamice zebiyoshi zuwa rugarsu
suna zuwa yasa iskar alameen Wanda tuni yashirya yabiya
mutumin kudinsa sannan yakarasa gurin ardo domin suyi
sallama sosai ardo yadunga kara bashi hkr abisa tsautsayin
dayafaru sallama yamasa yanufi gurin motarshi kamar
anjefota yahango surbajo tafito daga gidan dauke da tulu Zata
dibar ruwa tsayawa yayi harta karaso
ko kallonshi batayiba Tana kokarin wuceshi Dan ita yanzu
tsoronshi takeji
kiran sunanta yayi arude tajuyo Dan tunda take babu Wanda
yataba kiranta da sunanta taji dadin sunan kamarshi
tsayawa tayi ainda take
ba gaisuwa yatambaya
kayi hkr ina kwana murmushi yayi sannan yaamsa da Lfy
yakara da ina Zaki ruwa zan debo tabashi amsa
muje inrage miki hanya yafadi sannan yajuya yashige motarshi
bude mata gaban motar yayi tsayawa tayi kamar da karta
shiga sekuma ta tuno bindinga dagudu taje tashige yarufe
kofar yatada motor suka tafi
afuwan
akwai tafiya agabana maassalam
maman yusuf
[3/18, 14:11] Zahra muhd mahmudπŸ’ƒ: πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
*SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
Zahra Muhammad mahmud
*page 21-22*
Tafe suke yana janta da hira har suka iso bakin rafin yana
parking Ta bude motar tafice
Tanufi rafin ko sallama bata masa ba
Murmushi yayi sannan yace halin surbajo se ita shima bedamu
ba yaja motarshi yawuce yana fita agarin wayarshi tafara
ringing abokinshine Usman bayan sungaisa yace yanemi wayar
alameen din besamuba ko Lfy
Dariya yayi sannan yabashi labarin abinda yafaru tsakaninshi
da surbajo dariya shima Usman din yayi yace shege
mutumina wlh dukanku kunburgeni kunyi dede Allah de
yanuna mana ranar bikinnan
Hakade suka Dan jima suna hira daga baya sukayi sallama
Alameen gidansu yasauka yaci abinci anan abba yake
shaidamishi sati mezuwa zasuje nemarmasa auran surbajo
.sosai alameen yanuna jin dadinsa dajin zancan godiya
yamusu sosai sannan yanufi gidanshi fuskarsa dauke da faraa
Koda isarsa Kai tsaye cikin gidan yanufa bayan yagama
gaisawa da masu tsaron Lafiyarsa
Yana shiga falon Aisha ta taso afusace ta kama kwalar rigarsa
tarike sannan tace daga ina Kake kuma agurin wacce
shegiyar ka kwana batare daka sanar daniba tafadi cike da
rashin kunya
ran alameen tuni yafara zafi jin takira surbajo da shegiya
Dagowa yayi yace sakeni inwuce Aisha banason rigima yanzu
shewa tayi sannan tace ay Wlh inkaga nasakeka kafadamin
gurin wacce ka kwana ko anfadamaka bansan taketakenka ba
ay Tunda kafara zama bunsuru nagane to Wlh baka isaba
bade agidannanba
Tass yadauketa da Mari kamin tawatsake yasake Kai mata
wani daga bisani yarufeta da duka ihu take Tana neman agaji
seda yamata dukan dashi kanshi besan iya adadinsaba
sannan yakyaleta tuni tajima da sumewa
Ko ajikinshi ya dauko ruwa yasheka mata tafarko
sannan yabata amsa dacewa
Aisha Tunda nake bantaba ganin jaka kamarkiba dakikiya
kawai mahaukaciya
Wai kindauka tsaron ki nakeji to Wlh ko daya tausayinki nakeji
amma Tunda kin nunamin kedin dabba ce Wlh sena baki
mamaki kuma dakikace daga ina nake daga gidan matar
dazan Aura nake kisama ranki Wlh aure zanyi nanda sati guda
kuma it doesn't matter to me kome nene ze faru yafaru banza
tinkiya kawai ko kigyara halinki ko kada ki gyara damuwarkine
ko tablet nahana haihuwa dakike sha keze cutar baniba Danni
wuyarta nayi auran
ya ingijeta tafadi akan tiles sannan yawuce yabarta da
faasshen jiki se kuka takeyi
********
Surbajo Tunda alameen yatafi kullum da tunaninsa take kwana
take tashi sosai take kewarsa sakamakon so da kaunarsa
dasuka addabi zuciyarta tabbas yanzu tana sonshi dari bisa
dari zuwa yanzu sunfara samun sabani da jae ganin yanzu
batashi takeyiba shiyasa yaja baya shima da ita duk da
yanasonta amma baze jure tadunga shareshiba
su daddy sunje nemama alameen auranta inda ardo yay
matukar murna da afkuwar hakan badan komaiba
sedamutuncin iyayensa
kamar yadda alammeen yafadawa mahaifinsa daga baya
cewa shima bayason bikin yawuce sati guda tokoda suka
sanar da ardo bemusamusuba aka tsaida ranar auran sati
mezuwa bayan an tambayi surbajo shin kotana sonshi ta amsa
da eh tanasonshi
Ayimin afuwa nayi tafiyane
maman yusuf
[3/18, 14:12] Zahra muhd mahmudπŸ’ƒ: πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
*SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
Zahra Muhammad mahmud
*page 23-24*
Acikin satin aka soma shirye shiryen biki dan ranar asabar zaa
daura auren
Aisha Data fuskanci dagaske aure alameen zeyi hankalinta
vakaramin tashi yayiba Dan haka tanufi kawayenta subata
shawara
Koda isarta gidansu zuly kuka tasa mata tace kawata nashiga
uku alameen aure zeyi Dan Allah kitaimakeni narasa abinyi
Wani dadine yarufe zuly Dan Dama sun jima suna jiran wannan
ranar Amman afili kukan tasa itama suka rungume juna
dakyar sukayi shuru zuly tace wannan tashin hankali dame yay
Kama wallahi bazamu zuba ido muna kalloba semun dauki
mataki ki kwantar da hankalinki
Gobe in Allah ya kaimu zamuje gidan wani malaminmu yaiya
ayki sosai zeshare miki hawayenki sosai Aisha tayi murna da
shawarar aminiyartata Dan bata bar gidanba se dare
Alameen murna yake sosai Badan komaiba sedan auren
cartoon dinshi dazeyi
Usman dariya kawai yakeyi dazaran yaji alameen yakira
surbajo da cartoon Dan yana da tabbacin alameen dinne
zekoma cartoon din
Shiri suke sosai musamman gidansu alameen Dan sunfi kowa
murna da auren da alameen zeyi
Dubai mommy taje tahadowa surbajo kayan lefe da kayan
daki sabida sunce ardo base yayiwa surbajo kayan dakiba su
zasuyi
Dakuna biyu dake falon kasa nagidan alameen aka shiryawa
surbajo kayanta aka kulle dakin yayinda kayan lefenta aka
ajiye gidan su alameen sabida ardo yace a ajiyemata acan
**********
jae dayasamu labarin surbajo aure zatayi har gida yaje
yasameta koda tazo
jae rufe idonsa yayi ya zazzagamata masifa har yana cewa
auran kwadayi zatayi kuma insha allahu se an sakota kuka
surbajo tasa Tana rokonsa ya yafemata Dan tasan bata kyauta
mishiba amma bata da iko da zuciyarta takamu da son
alameen me tsanani Wanda tanajin bazata iya rabuwa
dashiba kuma ita badan kudinsa takesonsaba sedan Allah
Jae shima kukan yakeyi Dan kukan surbajo yadagamasa
hankali cikin kuka yace ya yafemata Allah kuma yabasu
zaman Lafiya da mijinta daganan yawuce yatafi yabarta Tana
Ta kuka
alameen shida Usman suka dauko hanyar makarfi Dan
sunason ganawa da Amarya suji shirye shiryenta
da isarsu ardo yasaukesu a dakin saukar baki yasa aka kawo
musu fura da nono me kyau sosai Usman yasha furar sabanin
alameen dashi ba cimarshi bace
seda suka Dan jima dazuwa sannan aka turo surbajo wacce ta
yafo mayafi tarufe fuskarta sabida jin kunya sallama tayi
tashigo dakin tasami guri tazauna daga nesa dasu dakyar ta
iya gaishesu suka amsa cike da barkwanci
Usman yace amaryarmu kunyarmu kuma kike Yi haka
Ko fuskar bazaki budeba
Ay surbajo jitayi wata kunyar tasake kamata Dan haka Kara
Rufe idonta tayi Tana murmushi daga cikin mayafinnata
hakade Usman yay tajanta da hira amma takasa bashi amsa
sabida kunya
mikewa Usman yayi yafice daga dakin Dan yabasu guri su
tattauna
shuru ne yabiyo bayan fitar Usman
jin shurun yayi yawa ne yasa surbajo zaton sun fitane daga
dakin ne dukansu yaye rufar datayi tayi carab idonta yasauka
akan na alameen da tun tuni ita yake kallo dasauri tamaida
rufar
matsowa alameen yayi gab da ita har jikinsu na gogar juna
lullubin ya bude surbajo kankame hannunta tayi a kirjinta
sabida batason yakalleta murmushi yayi Dan yafahimci me
take boyewa hannuwanta yakamo yaruke anasa sannan yabita
da ido yana karewa halittarta kallo ba laifi duk da kankantar
shekarun surbajo hakan be hanata mallakar duk wani Abu da
yamace ke daukar hankalin da namiji dashiba
surbajo duk Ta takura da irin kallon da alameen yake mata
kokarin kwace hannunta takeyi amma takasa cikin siririyar
muryarta tace kado Don Allah kasakarmin hannuna Wlh
kunyarka nakeji tafadi Tana runtse idonta
akasalance alameen yafara magana sabida kallon kirjin
surbajo dayayi yahaifar masa da damuwa sabida surbajo
batasa bresiar ba hasalima bata da ita garigar jikinta me
budadden wuyane irin na Fulani shiya Kara bayyanar da
halittar dukiyar fulaninta ganin hakanne yasa hankalinsa
yasoma tashi
dakyar yace surbajo kunyata kuma yanzu kikeji ko kinmanta
saura kwana biyu yarage kizamo mallakina Toni banason
kunyar nan taki kinji ko kai tadaga masa
yaci gaba ko bakyasona ne
dasauri tace kado aradu ina sonka kawai inajin kunyarkane
kunnenta yaja da Dan karfi Wanda hakanne yasa ta samishi
kukan shagwaba Dan dama surbajo gwanace gurin kukan
banza bare yanzu dame dalili yasamu
alameen yace daga yau nasauke sunan kado inkika kuma
kirana dashi kuma zanyi Maganin bakin daya kirani da sunan
kadon
cikin kuka surbajo tace aradu kado bazan Kuma........bata
karasa fadin abinda zata fadaba yahada bakinshi da nata
yashiga kissing kamar yasamu sweet
hankalin surbajo kusan barin jikinta yayi asakamako fadawa
duniyar dabata taba sanin akwaitaba arayuwarta
seda yajita jikinta yagama mutuwa sannan yakyaleta surbajo
dasauri ta janyo mayafinta tarufe jikinta har fuskarta jikinta se
rawa yakeyi ita bata san sunan abinda yamataba jikinta duk
yamutu
ga wata matsananciar kunyarshi data kamata shima daurewa
kawai yayi amma Allah kadai yasan yanayin dayakejin kansa
hira yay tajanta da ita amma bata bashi amsa hakanne yasa
yamike yace tosu zasu tafi dubu dari yabata akan kozatayi
amfani dasu dakyar taamsa sannan tayomasa rakiya inda
Usman yake jiranshi ajikin motarshi dakyar surbajo tayima
UsmUsman sallama sannan tacewa alameen kado kugaida
Gid.......bata karasaba tasa hannunta tarufe bakinta sannan
takwasa da gudu tayi cikin gida
dariya alameen yayi Dan yasan me yasa surbajo guduwa
mota suka shige bayan sunyiwa ardo sallama suka dauki
hanyar kaduna
Usman se tsokanarshi yakeyi
Maman Yusuf
[3/18, 14:13] Zahra muhd mahmudπŸ’ƒ: πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
*SURBAJO*
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
Zahra Muhammad mahmud
*page 25-26*
Abangaren uwargida Aisha kuwa jitake kamar takashe kanta
dan bakinciki sabida koda sukaje gurin bokan su Zuly cemusu
yayi kawai suyi hkr Dan aure ba fashi se anyishi shiyasa
gabadaya tarasa natsuwarta ga alameen yanzu yayi wuyar
gani sabida shirye shiryen bikin
Ganin tadamune yasa su Ruky kwantar mata da hankali
dacewa tabari akawo Amaryar bayan kwana biyu sumata
dukan tsiya hakanne yasa Zuciyart yin Sanyi danko kayan
fadan kishiya daaka bata batabi takansuba kawayentane suka
dau na dauka itama suka zabarmata Wanda zata sa in amfara
bikin
**********
Surbajo Tunda alameen yatafi yabarta kullum cikin tuno
abinda yamata takeyi itade batasan sunan abunba amma in
tatuno abun namata dadi har addua take Allah yasa yakara
yimata πŸ˜€
Ardo sosai yake shiri shima Dan tun ana sauran sati guda
bikin kullum se an kwantar da sa anyanka dangin maman
surbajo suma baa barsu abayaba sunzo bikin kwansu da
kwarkwatarsu suma sunyma surbajo shatara ta arziki
*RANAR BIKI*
ranar asabar 31-12-2011 dubban jamaa suka shaida daurin
auran Zahra Muhammad mahmud (wato surbajo)tare da
angonta alameen jibrin sulaiman daurin auran dayasami
halattar manyan shuwagabanni da yankasuwa uwauba sojoji
manyansu da kanana
Ko ina kakai dubanka alummane tako ina ranar garin makarfi
bamasaka tsinke sabida yawan alumma ga jiniya takoina
natashi kowa mamaki yakeyi me alameen zeyi da surbajo yar
kauye kamar haka hakade akagama taron daurin auren jamaa
suka fara watsewa
Dayake tare zaa wuce da Amarya tuni motocin daukar
Amarya sunfara dibar jamaa
Inda yawancinsu mutanen kaduna ne sabida ardo yace yana
gudun kauyancin yan rigarsa shiyasa masu natsuwar kawai
aka dauka
Amarya survajo wacce ke nade cikin wata lafaya Medan
karan Kyau da tsada se kuka takeyi sabida rabuwa da gida
dazatayi ammafa tayi kyau sabida wata yarinyar yayan
mamanta me suna Bilkisu dasuka zo daga kaduna itace
tayima surbajo Kwalliyar duk da ita surbajon bataso Amman
seda akayimata kuma tayi kyau farinta yafito sosai
Sumaye tajima Tana yiwa surbajo fada akan zama da miji
haka yan uwan mamantama sunmata fadan sabanin ardo da
kukan da surbajo takeyi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login