Showing 30001 words to 33000 words out of 224143 words

Chapter 11 - DAN MACE COMPLETED Romantic Book .txt

yasa shi yin fushi,kuma idan baka manta ba na fada maka a baya babanmu mutim ne mai saurin yarda da magana,ba tare da ya tsaya binciken ainihin abunda ya faru ba,ya d'aukar ma kansa alk'awarin ba zai zauna da ita ba,yanatunanin zamanta tare da shi zai b'ata masa maganar takarar d'an majalisa da ya fito bcos a lokacin harka ta bud'e,,tun kafin ma tayi tunanin dawowa gida kenan ya aika mata sak'on idan ta tashi daga can gidan surukanta kada ta kuskura ta dawo masa gida ya yafe ta a duniya,yahada mu kaf ya fad'a mana duk wanda yake jin k'aramin iskancinsa a cikinmu ko ya goyi bayanta to shima a shirye yake ya sallama shi ko da zai rage shi kad'ai,zai iya hak'ura da gaba d'ayan y'ay'an daya mallaka tunda mu bamu san yana son mu ba,shi yasa muke neman tozarta shi,shi ya gaji da rik'on mu muna azabtar da shi,muna sa shi yana ta aure²,sai tarin y'ay'a kawai yake da arzik'in da yake nema ya gagara samunsa.


Cikin k'ank'anin lokaci rayuwa ta sake yiwa Hauwa zafi kaima da ake kaika gida gurina Baba yace kada a kuma kawo ka,idan so nake na zauna tare da ku hanya a bud'e take,,tafiyar su Hajiya dai² sun cika sati biyu Rafeek yasa Maimunatu ta shirya kayanta kaf,tare da maidservant d'insu yayi musu Visa zasu bar k'asar,mai gadinsu kad'ai za su bari a nan bcos yayi shirin gyara gidan,saboda yana so ne ko da zasu zo k'asar ya kasance suna da gidan da zasu sauka a cikin gari duk da a d'an zuwansa ya mallaki manyan kadarori sosai,Hauwa bata tashi sanin abunda yake faruwa ba sai a ranar da su Maimunatu zasu bar k'asar,da safe wajen k'arfe 9 taga ana fita da kayansu,cikin damuwa ta samu Maimunatu da tambayar lafiya taga ana fita da kaya.?
Maimunatu cike da damuwa ta kalleta kamar za tayi kuka tace "wollahi nima ban sani ba yanzun dai yah Rafeek yake fad'a min wai zamu yi tafiya.."
A tsorace Hauwa tace "to su Hajiya fa,yaushe zasu dawo.?"
Maimunatu ta kad'a kai tace "Ban sani ba wollahi,munyi waya da su dai Hajiya tace min wai suna U.S."
Hawaye taji suna shirin sakko mata cikin damuwa tace "Me ya kaisu can to.!? Su da suka tafi Saudiyya.!?"
Maimunatu tace "Wollahi nima bai fad'a min ba"
Sauke kanta k'asa Hauwa tayi hawaye suna bin fuskarta ta had'e kai da guiwa a hankali ta fara rera kuka,damuwarta duka a lokacin ba akan tafiyar su Hajiya bane,illa kawai tana tunanin inda zata nufa idan ya zama dole sai tabar gidan,Maimunatu ta dafata tace "kiyi hak'uri sister in-law in sha Allah nasan ko mun tafi Hajiya da Abba zasu yiwa yah Rafeek maganarki,in sha Allah tare zamu zauna dake a can"
Cikin kuka ta d'ago kanta tace "Dama idan kun tafi can zaku koma da zama.?"
Maimunatu tana share hawayenta tace "Haka dai nake tunani,kamar idan mun tafi sai dai muzo da yawo k'asar nan"
Sake kife kai Hauwa tayi taci gaba da kuka kamar an aiko ta,Rafeek ya shigo ya tarar da Maimunatu tana aikin rarrashin Hauwa,ya tab'e baki daga inda yake tsaye yace
"Kizo ku wuce kina b'ata muku lokaci,kinsan lokacin daya rage flight d'inku ya tashi bashi da yawa ko.?"
A hankali Maimunatu ta kalleshi ta girgiza kai,tana rik'e da hannun Hauwa tace "Toh sister sai munyi waya.. Zamu tafi.?"
Hauwa tana jin haka ta sake fashewa da kuka ta rik'e ta sosai tana cewa
"Sister kada ki tafi ki barni,kice su Hajiya suma su dawo dan Allah,wallahi ban san ina zani ba yanzun,Baba yace kada na koma masa gida saboda abunda ya faru,,idan kuka barni rayuwata tana cikin garari wallahi bani da kowa ban san ina zan nufa ba"
Maimunatu ta sake goge hawayenta tace "kiyi hak'uri in-law idan na tafi zan sanar da Hajiya in sha Allah kema zaki biyo mu,ki kwantar da hankalinki,kuma ai naga ga nan gidan me zai sa baza ki zauna ba,zuwa sanda Abba zai turo miki kud'in jirgi.? Kada ki damu please in sha Allah zaki biyo mu"
Rafeek yana daga tsaye ya had'e rai yace
"Wai ke ba magana nayi miki ba,i told u zaku yi missing flight idan baku yi sauri ba,kin zauna nan kina kuka kamar wata matar mamaci,idan baza kije ba ki zauna.."
Yayi wucewarsa ciki,kusan mintuna biyar ya sake dawowa,still yaga Maimunatu tana ta aikin lallab'a ta,ransa a had'e ya taso kansu duka a masife,sai da yayi son ransa sannan yayi shiru yasa Maimunatu gaba suka fita,bayan yaga tafiyarta sannan ya dawo,ya shigo parlor da tunanin samunta a nan ya k'arasa zazzage mata rashin mutunci ya tarar bata nan,cije lips yayi ya wuce yana fad'in
"Me yasa baki jira ba kika tashi.!?"

D'akin Hajiya ta koma data bar mata a bud'e ta kulle kanta,tayi kuka sosai as if her life were just come to an end,daga nan bacci ya fizgeta bata farka ba sai tsakiyar rana wajen azhar shima a firgice ta mik'e sakamakon mummunan mafarkin da tayi,tana ta kallon d'akin ta sauka tana dube² kafin ta wuce bathroom ta d'auro alwala,sallah ta fara yi kafin ta had'e kai da guiwa taci gaba da tunanin inda ya kamata ta nufa idan su Maimunatu basu dawo ba,tayi nisa cikin tunanin ta jiyo ana knocking door d'in d'akin,zazzare idanu tayi tana kallon k'ofar a ranta tana jin kamar kada taje ta duba,ta daure ta mik'e bayan ta ajiye hijab d'in jikinta a sad'ad'e taje bud'e k'ofar lokacin ta yi zaton mai bugun ya tafi,Rafeek ta gani tsaye fuskarsa kamar an aiko masa sak'on mutuwa,da sauri ta juya zata rufe k'ofar ya rigata turawa ciki,sakin masa k'ofar tayi ta fara komawa baya,cikin takunsa mai cike da nutsuwa ya fara biyo ta har suka yi rabin d'akin sannan ya tsaya yana jifanta da mugayen kallo,a hankali ya ajiye mata ledojin hannunsa,daga haka bai ce komai ba ya juya ya fita,har ya fita ya barta k'irjinta bai daina bugawa ba,tana ganin ya bar d'akin a 360 taje ta rufe k'ofa ta dawo ta zauna bakin gado tana maida numfashi,har aka yi la'asar bata sake bud'e k'ofa ba,kuma bata d'auki ledojin daya shigo da su ba,yinin ranar har akayi isha ita kad'ai ce a cikin gidan sai yaronta da yake ta wani irin bacci kamar wanda ya gamu da cutar bacci,da ya farka babu jimawa yake sake komawa,tsananin damuwa da suka had'e mata yasa ko yunwa bata ji ta dameta ba,sai can tsakar dare data kasa bacci ta fito cikin sand'a da nufin samun ko yoghurt ne ta sha ko Allah zaisa yaronta ya samu abunda zai tsotsa,ta shiga kitchen ta bud'e fridge ta d'auko,tun a nan ta bud'e ta kafa kanta bakin babban goran yoghurt d'in L&Z,ta sha kusan da d'an yawa sannan ta rufe ta mayar ta sha ruwa kad'an ta fito tana tafiya da kyar kanta yana tsananta ciwo,ta kusa rabin parlor kamar ance ta d'aga kai taga Rafeek tsaye a gabanta daga shi sai short,jikinsa duk a bud'e babu ko d'an sleeveless bare robe,kaucewa tayi zata wuce tana jin fad'uwar gaba ya fizgota ta dawo yana kallonta da wani irin yanayi mai wuyar fassara ya sauke idanunsa saman k'irjinta,teat d'inta da suka bayyana ta cikin nighty dake jikinta suka fara fizgarsa saboda rigar slick ce and bata sa komai ba a ciki,ta san yaronta yana farkawa cikin dare,ba ta son sai tazo tana kokawar cire bra,ya daure ya had'iye saliva's still yana kallonta cikin kame² yace
"Yaushe zaki tafi ne.!?"


Ta daure tace "Ina.!?"


Yace "gidanku ko nan zaki yi ta zama.!?"


A hankali ta girgiza kai tace "babu inda zanje",wani irin kallo yayi mata yace "really.!?"


Ta gyad'a masa kai,yace "dole ki tafi.."

A hankali ta motsa tana son k'wacewa daga rik'on da yayi mata,yak'i sakinta ganin bata yi magana ba sai dai fuskarta dake nuna alamun tana son yin kuka ya sake matsarta yace "ko baki ji ba ina magana.!?"
A hankali ta had'iye hawayenta tace "Ni fa bani da inda zan zauna idan kace na bar muku gidan ku,kuma ka sani Babana yace kada naje masa gida ya yafe ni.."
Cikin sheshshek'ar kuka ta k'arasa fad'a hawayenta na ci gaba da sauka,a tunaninta idan ta fad'a masa matsalar ta zai ji tausayinta ya kyaleta,tana fad'a taci gaba da rera kuka,dariya Rafeek ya fashe da ita kafin yace "Auu! Haba.??"
Sai ya sake kyalkyalewa da dariya,sai da yayi mai isarsa kafin ya dakata still yana rik'e da ita,cikin salon tafiya da hankali yana lumshe idanunsa ya fara shafa kwantaccen gashin dake saman k'irjinsa yace
"Toh yanzun ina za ki tafi kenan.!?" Kamar ya damu da sani al'halin fuskarsa murmushi kawai yake saki,ta d'ago bayan ta share hawayenta tace
"Nima ban sani ba"
Y'ar dariyar yak'e yayi yana kallon jikinta da yake jin yayinsa ya fara sauyawa kunsancin da suka samu bayan tsayin lokaci kamar mayen k'arfe yana fizgarsa ya daure yace
"Okay! Bari to zuwa da safe kafin na tafi nayi tunani,idan zan iya barinki kici gaba da zama to,idan ma bazan iya ba dai zuwa lokacin i will let u know.!"
Sheshshek'ar kuka ta sake yi mai had'e da jan zuciya,hakan yayi sanadiyyar d'agawar k'irjinta,incidentally boobs d'inta suka yi rawa,idanun rafeek akanta lokacin da al'amarin ya faru,hakan sai ya sake jefa zuciyarsa cikin zullumin da har bai san lokacin daya kai hannunsa wajen ya matsasu a hankali ba,saurin doke masa hannu tayi tana zabga masa harara tace "Sake ni!" In an commendable way,yayi murmushi ya sake matso da ita jikinsa yace "idan na k'i fa.!?"
Tace "sai na maka Allah ya isa,saboda kasan tab'a ni haramun alaika."


Yayi dariya yace "really.!?"


Ta gyad'a kai,dariyar mugunta ya sake yi yace "Da gaske zaki yi Allah ya isa idan na tab'a ki.!?"
Ta sake gyad'a masa kai,tana shirin yin magana yayi saurin d'aukarta yayi gaba yana fad'in "kiyi min babbar Allah ya isa yanzun.."
Ya shige bedroom d'insa da ita,tana fizgewa tana komai sai da ya shiga da ita ya maida k'ofa ya murza key,ta tsure tana kai masa duka tace "Ni ka sake ni na tafi,kaga bana son iskanci" dariya yayi ya jefata saman bed,yana kallon ta yunk'ura zata tashi yayi maza ya danneta yana fad'in
"Ni dai kike cewa d'an iska ko.??"


Bakinta still bai mutu ba tace "na fad'a d'in d'an iska ne kaaaa.."
Saurin rufe mata baki yayi da nasa cike da mugunta ya shiga sarrafa ta yadda ransa yaso,tutturashi ta ci gaba da yi a tsorace tana son tashi,ya sauke mata nauyinsa yana ci gaba da kissing d'inta any where,ta ci gaba da dukansa tana hawaye,ganin zata bashi matsala yasa shi damk'e hannayenta ya ware su gefe yaci gaba da murzarta kamar wanda aka aiko,,a wannan daren sai da Rafeek ya tabbatar yayi mata abunda baza ta tab'a mantawa da shi ba kafin ya kyaleta ya koma gefe ya kwanta yana maida numfashi,jikinta yayi mugun laushi saboda tsabar gurzar da yayi mata,kwakwkwaran motsi kasawa take,a nan baccin azaba da tsabar gajiya mai cike da firgici ya d'auke ta,ba ita ta farka ba sai gabannin ketowar fajr,ta mik'e da kyar tana duba jikinta da inda take a tunaninta mafarki tayi,ta ganta a d'akinsa,saurin sauka tayi daga saman bed d'in ta maida kayanta tayi hanyar fita tana kukan zuci da yiwa Rafeek Allah ya isa,har ta tsarkake jikinta tayi sallah bata bar kukan zuci ba,da safe misalin 8 Rafeek ya fito cikin suit grey colour yana ta baza k'amshi,a bakin door d'in ya tsaya yayi knocking,tana ji ta san shine ta basar bata tashi ba,sai da ya b'ata almost twenty minutes yana jira ta bud'e tayi masa shiru,daurewa yayi duk da b'acin ran da yake ji na share shin da tayi ya sake knocking,still yaji babu alamun motsinta,yayi k'wafa muryarsa da fad'a² yace.....




#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*


*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥



*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2


*Wah! My dear people,i really appreciate ur comment,thank u² 💓 Bahot² khushu.💃🏻💃🏻*


Pᴀɢᴇ 10.
#Lᴏɴᴇʟɪɴᴇꜱꜱ

"Na san kina jina,idan kinga dama kuma kin shirya ki fito muyi magana,bana son ki b'atamin lokaci zan wuce ne i'm in a hurry."
Tana zaune still sai dai idanunta suna kan k'ofar,tuno irin wulak'ancin da yayi mata da dare a hankali hawaye suka samu damar sauka saman fuskarta,ta goge tana jin damuwa na taso mata tace


"Take ur journey,there's no need to talk."


Yana daga wajen yace "kamar yaya na tafi.? Bayan kin san na fad'a miki gidanku zaki tafi,nan zansa ayi aikin rusa shi."
Gabanta ya fad'i da sauri ta mik'e da hijab d'in a jikinta tana hawaye taje ta bud'e k'ofar,yana kallonta yayi murmushin gefen baki,saurin kawar da kanta tayi muryarta na trembling tace
"Mene ne wannan gidan yayi da zaka sa a rushe shi..??"

Kai tsaye yace "ra'ayi na kenan"


Ta daure tace "ba haka bane"


Saurin kallonta yayi yace "kamar ya.!?"


Tace "Ehh! Nasan kawai kana yi min kora da hali ne,kana so ko ta wane hali sai ka raba ni da gidanku shi ne kawai nufinka."


Murmushi yayi yace "really.!?"


Tace "ehh! Kuma idan ba haka bane ka k'aryata maganata" girgiza kai yayi yace "sure.! ur words are truth"
Kuka ta saki mai sauti ta durk'ushe a gurin taci gaba da rerawa,tsayin lokaci suka d'iba a haka yayi shiru bai sake magana ba sai da yaga bata da niyyar dainawa sannan yace
"If u finish crying let me tell u the result,,bcos i'm in a hurry.."


Tana kuka a masife tace "ka fad'a ai ina saurarenka"


Yace "saboda na ji bazan iya barinki kici gaba da zama a nan ba,shi yasa na yanke shawaran korarki ko ta wane hali,though Allah yasa kin fahimci abunda nayi niyya,but akwai favour guda biyu da nayi niyyar yi miki,ba kuma saboda ke bane,zanyi ne just bcos of ur innocent kid.."


Da gaggawa ta d'ago ta k'urawa bakinsa ido tace "Fad'a min mene ne.!?"


A tunaninta still zaice ya fasa rusa gidan ta zauna sai taji yace "Saboda soyayyar da ahalina suke miki,naji ina son yi miki alfarma na baki gurin zama,and k'arin alfarma daga zuciyata zan taimaka miki da capital da zaki taimaki kanki da shi cos bana so kiyi bara,a matsayi na bana son wani lokaci a ganki ace Laaa! Kunga tsohuwar matar Rafeek,but sai kin yi min alk'awarin ko da na tafi baki gama had'a muku kayanku ba zaki tafi and u will stay away from my family,ba zaki sake neman inda suke ba,sannan ne zan amince na baki duk abunda nayi niyya."


A hankali ta gyad'a masa kai saboda rashin sanin mafita tace "Na amince"


Yayi murmushi yace "better" Sannan ya wuce yana sake cewa "jira ni ina zuwa"


A sanyaye tace "toh" taci gaba da tsaiwa har yaje d'akinsa ya dawo bata matsa daga inda ya barta ba,ya tarar da ita tana ta share hawayen dake mata zarya,yana zuwa bai yi magana ba ya mik'a mata envelope d'in daya fito da shi,kallonsa tayi ta kalli takardun bata karb'a ba tace "Na mene ne.!?"


Wani irin banzan kallo ya jefeta da shi yace "wane magana muka yi dake yanzun.!?"


Bata ce komai ba tasa hannu ta karb'a,tana sake share hawayen da suka k'i tsayawa tace "Na gode sosai" daga haka ta juya ciki tana sakin marayan kuka,lokaci guda jikin Rafeek yayi sanyi da yaga ta d'auki Yaronta da har lokacin baisan wane iri bane bak'i.? Fari.? Kore.? Shud'i? Ko kuma yellow.? Duk bai san yaya kamanninsa suke ba,ta gama goya shi sannan ta fara fito musu kayansu tana had'awa tana kuka,kamar zai yi magana ya kalleta idanunsa sun sauya launi,kome ya hana shi kuma sai yayi tsaki ya juya ya bar gurin da sauri,kafin k'arfe 10am ta had'a komai nasu ta fita da shi daga gidan da taimakon mai gadinsu,Rafeek kuwa zuwa lokacin tuni yayi bankwana da k'asar,,misalin k'arfe goma da mintuna goma 10:10pm ta tsaya k'ofar gidanmu tana tunanin ta shiga ko A'a,sai ga baba ya dawo zai wuce ciki,ta gaishe shi har k'asa,ba tare daya amsa taba yayi wucewarsa cikin gida ya barta,tana ta tsaye a waje da kaya a gabanta ta samu yaro tace yayi mata magana da ni,d'an aike babu sirri yana zuwa ya k'walla kiran "Wai ana magana da Adda Maryam",daga d'aki babanmu ya fito da sauri yace da yaron

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login