Showing 78001 words to 81000 words out of 224143 words

Chapter 27 - DAN MACE COMPLETED Romantic Book .txt

janyo,dama sai da aka fad'a maka ka bi komai a sannu ka nuna kai ba haka ba,ga shi nan yanzun kana neman kashe kanka,ance kaje hospital kak'i,ni banga ranar da za ka daina taurin kai ba wollahi,Allah ya halicci mutum yace shi a duniya abunda yaga dama zai yi,to kowa ma ai yana da na gaba da shi,kuma ko mene ne zai faru kai ka janyowa kanka,idan sun nuna basa son ka rab'e su ni bazan ga laifinsu ba,28 years u don't know where they are,how they live,and no body knows yaya suke rayuwa duk babu ruwanka,kuma babu wanda ka bari ya sani sai yau rana a sama kace ka biyo sahun d'anka,yo ko ni ce ai wollahi bazan kulaka ba,idan ka takura min na kaika court saboda tozarcin yayi yawa" ya zuba mata ido yadda take masa masifa kamar wata yayarsa ko uwarsa,ya tsuke fuska yana kallon Hajiya kamar k'aramin Yaro yace "Hajiya kice tayi shiru dan Allah,surutun ta yana hawamin kai" ta tab'e baki tace "Dan na fad'i gaskiya shi ne zaka ce ina maka surutu.!?" Ya juyar da kansa bai sake magana ba ya lumshe ido,ta mik'e a fusace tana kiran d'anta namijin mai sunan Alhaji zakar da suke kira *Aryaan* ya matso kusa da ita da ladabi yaro d'an shekaru 22 yace "Here i am mom" tace "Je ka kira min wannan Clark yake ko waye ne oho.!" Ya juya da sauri yana amsawa,babu jimawa suka dawo tare da Clark,bata kalleshi ba tana had'e rai cikin harshen nasara tace "gidan da yake aikenka za ka kai ni yanzun da sauri" yayi saurin kallon uban gidansa kafin ya kalleta,ta sake b'ata rai tace "Da kai nake kake kallonsa,idan ba zaka je ba ba ni address sai naje da kaina" ya sunkuyar da kai ya amsa a tsorace da yaji boss d'in nasa bai masa magana ba,ta zari vail d'inta ta rufa ta wuce a fusace tana fad'in "Hajiya na tafi sai na dawo" Hajiya ta saki baki tana kallonta kafin tace "Wai da gaske zuwa za kiyi yanzun,bakya ganin dare yayi.!?" Ta girgiza kai tana wucewa,Rafeek ya bud'e idonsa a karo na biyu yana kallonta har ta fice bai samu damar yin magana ba.


Direct Albert street suka nufa,tana back seat sai kallon arean take har suka tsaya bakin apartment d'in,ya fito ya bud'e mata k'ofa ta fita tace "Ina ne gidan.!?" Ya nuna mata da hannunsa,ta wuce ta barshi a tsaye a gurin,tana k'arasawa dai² entrance ta danna door bell,Bareerah ta bud'e ta bata umarnin shiga ciki,ta shigo idanunta suna rolling cikin apartment d'in da tunanuka iri² a ranta,on the other hand Bareerah followed her tana sanarwa Annie sun yi bak'uwa,they turned around da tunanin wace ce.!?,Hauwa tayi tsaye tana nuna ta da hannu cikin tsantsar mamaki but she could not even mention her name until Annie call her out "Maimunatu!" hurriedly Nuraz ya d'ago kansa daga tunanin neman mafitar daya tafi ya sauke akan matar with the memories of mene ne ya kawo ta gidan su.?


Maimunatu was standing where she was Annie ma haka,lolly kam tuni ta sulale tayi k'asa a sume,za ta fad'i a 360 Nuraz ya tare ta yana kiranta da k'arfi cikin tashin hankali,Nusrah ta k'araso a 180 tana kiran "Aunty" Bareerah drew her eyes outward tana lek'en fuskar Lollyn,kwantar da ita yayi saman armchair ya shiga murza tafin hannunta ganin lokaci guda ta d'auke,Nusrah ta kama d'ayan tana tab'a jijiyar dake gwada heartbeat d'inta,bayan ta tabbatar numfashin yana nan ta saki ajiyar zuciya ta d'ago suka had'a ido da Nuraz,ta masa alama da ido ya kwantar da hankalinsa,shi duka hankalinsa ya tashi ko tunanin auna tafiyar bugun zuciyarta bai yi ba,,Annie taja doguwar ajiyar zuciya tace "K'araso Maimunatu ki zauna" jikinta duk yayi sanyi sai kallon sashin da Hauwa take kwance take yi,ta fara takawa a hankali zata k'araso Bareerah ta zo da ruwa mai sanyi suka shafa mata,sanyayyar ajiyar zuciya tayi tafin ta fara motsawa,ta bud'e ido a hankali tana kallonsu,idanunta suka sauka kan Maimunatu dake tahowa a hankali inda suke,babu wanda yace mata ci kanki har ta k'araso,sun kafe juna da ido kowanne sai kallon d'an uwansa yake fuskokinsu d'auke da wasu irin manyan sak'onni,Maimunatu ta k'araso gabanta tana niyyar rik'e hannunta a fusace Nuraz ya daka mata tsawar da ba ita kad'ai ba hatta Annie sai da taji ta,fuskarsa a d'aure tamkar bak'in hadari yana kallonta with his coloured eyes yana cije hak'oransa yace "Me kika zo yi mana ne Malama.!?" Ta kalleshi a tsanake yadda ya tsaya gabanta kamar wani bijimin zaki yana huci,hak'oransa banda had'uwa da fitar da sauti babu abunda suke,da ganinsa ba sai ka tambaye shi dalili ba ya riga ya gane ko wace ce ita da matsayinta,ta kalleshi ta sake kallonsa ta juya tana kallon Annie tana nunasa tace "Adda Maryam.. Wan..na.n Nuraz ne ko Hauwa ta yi wani auren ta haihu.!?" Jikin Annie a mace ta girgiza mata da kai da kyar tace "Babu auren da tayi,shi ne dai Yaron nan Ubangiji ya raya mana shi" a mamakance ta kalleshi sosai tace "Ikon Allah,,ubangiji mai yadda yaso a lokacin da yaso" Wani mugun tsakin daya ja yasa duka hankulansu ya sake komawa kansa yana sake tsuke fuska yana kallon Maimunatu yace "Hajiya if this is what really bring u here,i hope u can go" ya fad'a yana nuna mata hanyar data biyo ta shigo,tayi ajiyar zuciya za tayi magana ya daka mata tsawa "I said leave.. We don't want to see u here.!"


"Nuraz.!" Annie begins to call him out da muryar fad'a idanunta har sun fara sauya kala saboda b'acin rai ta ci baga da fad'a "I don't like disrespect,ita wannan d'in ba kanwar mahaifinka bace kake mata tsawa" datse hak'oransa yayi cikin k'arajin masifa yace "Ni Annie ki daina cewa mahaifina,ni kad'ai ne ba ni da wani baba,mutumin daya sheganta ni shi zan kira da sunan mahaifi.? Mahaifiyata ta ishe ni rayuwa ko da uba ko babu zan rayu,ubangiji ya halliceni zai ci gaba da bani kariya"
"Silence right here before i hurt u" yayi shiru sai huci yake cikin ladabi ya sauke idanunsa k'asa,Annie ta juya ta kalli Maimunatu da jikinta yayi sanyi tace "sit down Maimunatu" ya sake d'agowa a fusace "A ina za ta zauna.!? Wollahi Annie sai ta bar gidan nan" ran Annie a b'ace tace "Ka ji na kama sunanka.??" Yace "Nifa Annie i don't care da duk abunda za kuyi but billahillaziiy she most be out not for a while" Annie tana huci tace "What if i said she won't leave.!?" Ya d'ago yana kallonta his eyes twinkling again because of the trauma yace "Shi kenan Annie I'll leave the house sai ta zauna" yana fad'a ya wuce bedroom d'insa Annie ta kalli Maimunatu tana fad'in "Zauna mana" ta girgiza kai tace "A'a Adda Maryam,bcos of my brother's fault bai kamata na haddasa muku fitina ba,tunda har yayi rantsuwa zan tafi but in sha Allah zan dawo."


Yana shiga bedroom he took nothing but his car keys,the nerves in his forehead duk sunyi bar'o bar'o,ya fito a fusace had'e da banging door d'in ya kama hanyar fita,Nusrah tayi saurin tashi ganin zai fita and begins to run after him cikin tashin hankali tana masa magana,babu wanda ya kula yayi ficewarsa,ta dafo masa baya har waje,ya bud'e front seat ta side d'in driver ya shiga ya kulle yana k'ok'arin tada motar tayi saurin bud'e d'ayan side d'in ta shiga,mukullin tayi saurin cirewa ya d'ago idanunsa ya sauke akanta cikin hayaniya yace "give it to me.!" Yana mik'a mata hannu,ta girgiza kai tace "A'ah" yace "Ba ni ki fita nace.!" Ta sake girgiza masa kai tace "Ba zan bayar ba" cikin k'arfin hali,wata uwar tsawa ya buga mata yace "Za ki bani ko saina shak'e ki kin rasa numfashi.??" Ta d'auke kai gefe tace "will u try.!?" Tana turo masa wuyanta,yayi k'wafa yana jijjiga kai bai ce komai ba,ta koma ta zauna sosai tana kallonsa tace "Wane irin zafin zuciya ne haka.!? Daga zuwan mata baka jira ka ji abunda ya kawo ta ba kawai ka hauta da masifa,dama laifin wani yana shafar wani ne.?" Ya juyo a fusace ya fizgota ta fad'o jikinsa a firgice,yana zare idanunsa da suka koma ciki,da wata irin kakkausar murya yace "Give me my key and then hurry to get out from my sight" duk da ta tsorata da shi hakan bai sa ta fasa ba tace "Bazan bayar ba" ya daka mata tsawa yace "Ke bani nace" ta gyara bakinta tace "Sai kayi kuma" hannunta ya dank'o zai b'amb'are ya kwace key d'in tayi maza ta tura shi cikin riga,he lifted his red eyes over her yayi k'wafa angrily pushed her back ta koma ta zauna,her head hitting the car's cover ta saki k'arar azaba,da sauri ya rik'o ta bakinsa har b'ari yake wajen fad'in "Sannu! Baki ji ciwo ba.!?" Ta d'ago idanunta ta sauke a kansa,ya janye hannunsa daga jikinta da sauri ya harareta,ta tab'e baki kad'an tace "Idan naji ciwo ma ai kai ka janyo" ya tab'e baki yana kallon waje "Ko kuma ke ba,ni na shiga sabgar ki ko ke kika shigo nawa.!?" Ta juya tana kallonsa tace "Mu duka muka shiga harkar juna,amma kaine ka fara" ya juyo da kansa yana kallonta "Kada ki rainawa kanki hankali ni na biyo ki ko ke kika biyo ni.!?" Bata yi magana ba tace "Sai kuma kayi" yace "Sai muyi dai" ta tab'e baki tace "Wai daka fito ma ina zaka je da.!?" Yace "Ina ruwanki da inda zanje.!?" Tace "Ruwan nawa dana gani shi yasa nayi tambayar ai" yayi siririn tsaki bai kulata ba,ta sake juyowa tana kallonsa,yadda yayi kicin² kamar wanda aka aikawa sak'on mutuwa ta tab'e baki k'asa² tace "Mutum sai miskilanci" yayi saurin juyowa yace "Me kika ce.!?" Tace "Ina ruwanka ko kaji nace kai.!?" A fusace ya dank'o ta cikin fushi yace "Maimaita abunda kika fad'a yanzun" tace "To ina ruwanka ne wai ko da kai nake.??" Ya kalli k'wayar idonta dake k'ik'k'iftawa ya saketa yace "Mutum sai shegen tsoro" ta tab'e baki bata ce komai ba sai tambayar da ta sake yi masa "Where do u think to go.!?" Ya d'auke kai yana kallon waje yace "Bar!" A sukwane ta juyo idonta a wajen tace "What are u going to do.!?" He didn't bother yace "Me ake zuwa yi.!?" She carefully stared at him tace "Dama kana sha ne.!?" Ya d'age shoulder's yace "I'm going to start today" hankalinta a tashe ta juyo dukanta ta fuskance shi tace "Pleasee don't go" ya juyo yayi mata wani irin kallo yace "Why not.!?" Tace "Dan girman Allah ba don ni ba" ya tab'e baki yace "I haven't made a promise to u bazan je ba ko bazan sha ba" tayi shiru tana kallonsa ta rasa abunda zata fad'a,can tace "To wai duk mene ne ya janyo.!?" Kai tsaye yace "B'acin rai" tace "Saboda b'acin rai then u rebel against ur Lord ko.!?" Ya juyo ya kalleta ya d'auke kai yace "Kinga Malama first give me the key and then naje na dawo sai ki min lecture" ta marairaice tace "Dan Allah ba don ni ba kace ka fasa zuwa,babu kyaufa kaima ka sani,sannan idan ka sha ka san nau'in sab'on da zaka aikata kana cikin maye.!?" Ya juyo yana kallonta ya tab'e baki "Ina ruwanki da sab'on da zanyi,naga dai kaina zan d'aukarwa nauyin zunubin ko.!? Besides iyaka ace bayan giya na nemi mace,shi kenan fa" hawayen idonta tayi k'ok'arin mayarwa tace "That's not it" yace "So what.!?" Tace "The sin and the severity of guilt will continue to spill over ur family" yace "by then i will repent" cikin hayaniya tace "U will repent.! Daga baya kenan ko.!? Are u sure ma ubangiji zai barka har ka gama aikatawa sannan ka tuba.!? Ko kana da grantee idan ka tuba he will forgive u.!?" Yace "Of course he will forgive me" a fusace ta juyo hawaye suna sakkowa a idonta tace "well.! Tunda kace haka" keys d'in ta ciro ta mik'a masa tace "Ja motar muje" ya juyo yana kallonta yace "where are we going.!?" Tace "Inda zaka je" yayi murmushi ya tada motar suka fara tafiya,a bakin *Round 6 bar & night club* yayi parking bata kula shi ba ta bud'e motar ta fice,ya juya zai mata maganar shi da wasa yake mata dan baya so ta dame shi ne,yaga har ta fice ya fito da sauri a tunaninsa idan sun zo ba zata iya fita ba,shi tunda yake bai tab'a zuwa ba sai dai ya wuce yana yiwa masu shiga fatan shiriya,ya biyota da sauri yana kira tak'i tsayawa sai da ta jashi har ciki,da kyar ya risketa a bakin bar d'in ta haye saman stool tayi d'are² ya tsaya kusa da ita yana haki,ya sunkuya dai² kunnenta saboda sautin music da aka k'ure yace "What are u doing.? Did i told u to come in.!?" Bata kulashi ba tayi oder cup biyu na veer,ya zaro ido yana kallonta yace "Ki bari bana son abunda kike yi" ta d'ago ta kalleshi lokacin da me kula da gurin ya mik'o mata yana murmushi yace "A sha lafiya" She smiled at him ta d'auki cup za ta kai bakinta,quickly he twisted her arm ta dago ta kalleshi tace "What's that.?!" Yace "Ba ki da hankali za ki sha.!?" Tace "u don't mind ka sha kawai" tana sakin wani mugun smiling as she took the other cup tana mik'a masa "Karb'i ka sha kaima dama abunda ya kawo mu kenan" ya k'wace cup d'aya a hannunta ya ajiye,yace "Kina hauka zaki ce na sha" tayi dariya tace "A'a na ji kace ne zaka sha,shi yasa nima zan sha" ya kamo hannunta zai kwace d'ayan cup d'in ta sake d'auko d'ayan yana kallonta da b'acin rai yace "Wai ke me yasa kike haka,daga fad'a miki zan sha shi ne saboda kin fini rashin hankali sai ki d'auka za ki sha.!?" Tace "Gani nayi kai fad'a kayi,ni kuma shi yasa zan aikata" yace "ajiye mu tafi to",ta d'ago tana kallonsa tace "A'a saina sha,kaima ka sha ga shi" tana mik'a masa kofin trying to put it in his mouth,a fusace ganin tana neman d'ura masa abaki ya doke kofin ya fad'i ya fashe,the explosion of the glass cup had to stop the music dake tashi hankulan turawan ya dawo kansu,hannunta ya dank'a a fusace yana k'ok'arin kwace d'ayan cup d'in tak'i saki yace "Saki" tak'i,juyin duniya yayi da ita ta saki tak'i data fusata shi bai san sanda ya kwasheta da mari ba babu shiri ta saki ya ajiye musu,ya zaro wallet d'insa ya cire kud'in da bai san nawa bane ya ajiye musu ya kamo hannunta ya shiga janta,tana dafe da kuncinta saboda shigar ta da marin yayi,yayi ta janta sai da suka fito some of the onlookers were stepped behind him yana fitowa ya bud'e mota ya jefata,ya zagaya d'ayan side d'in ya shiga ya tada motar,da mugun gudu ya bar gurin yana dana sanin ambaton zai sha da yayi da jan istigfari a zuci,har suka shigo line bai kalleta ba,itama bata fasa kuka ba,ya gyara parking bai kalleta ba yace "get out" bata kalleshi ba tace "Mari na fa kayi" ya juyo a fusace yace "Na mare ki,za ki rama ne.!?" Ta sake fashewa da kuka,cikin kuka tace "To kawai daga cewa zan sha sai ka mare ni,tun farko kai me yasa ba'a dake ka ba da kace zaka sha ka nemi mata.!?" Ya tsaya kallonta da sakakken baki yace "Da nace haka ina ruwanki.!?" As she added the volume of her cries tace "To ni da nayi ina ruwanka da ni.!?" Ya matse forehead a masife yace "Be quiet.! Don't let me feel too bad yanzun ki janyo na zane ki" tana kuka tace "Allah nima saina fad'awa Annie abunda ka yi" yace "kada ki fasa maza go and tell her,but ki tabbata from the time kika fad'a from that time i will begin to do what i didn't intend to" ta juyo da sauri tana tsayar da kukan tace "What are u going to do.!? Giyar za kaje kasha ka nemi matan.!?"
A fusace yana mata tsawa yace "Ehh! Su d'in zanyi ina ruwanki idan na yi.!?" Ta sake fashewa da kuka tace "Allah ba zaka jeba,kuma duk wacce ka nema Allah saina.." Bata k'arasa ba yace "Sai kin yi me.!?" Cikin hayaniya tace "Ina ruwanka da abunda zanyi.!?" Ya jinjina kai yace "get down" tace "bazan fita ba wollahi sai dai mu fita tare" yayi shiru yana kallonta yace "ke fita nace,komawa zanyi tunda ke baki da hankali" tace "Rashin hankalin yasa nace zan sha beer d'in,if u want by then u can took me as ur prostitute.." Ya juyo a firgice "do u know what u're saying.!? Ba ki da hankali ko.!?" Tace "u don't care! Since i have no value da za'a iya aure na a zauna da ni,na yanke shawaran zame maka karuw..!" Bata karasa ba ya shak'o wuyanta cikin masifar zafin rai yace "If u repeat it again wollahi sai na ji miki ciwo,baki da hankali baki da tunani kike kiran kanki da wannan sunan.!? Ko su karuwan da suka tsallake gaban iyayensu suke zaman kansu suna gudun a kira su da sunan shi ne ke dan baki da lissafi kike neman sawa kanki.!?" Ya tura ta baya ya daki steering wheel a zafafe ya furta "Tur da wannan furucin,fita ki bani guri,,fita nace" ya k'arasa yana mata tsawa,ta had'e kai da guiwa ta sake fashewa da kuka mai tsanani,ya dafe kai he felt himself regretting akan maganarsa,sun jima a haka idanunsa a lumshe banda neman gafarar Ubangiji babu abunda yake yi,ta sassauta kukan a hankali in a frightful voice ta fara magana.....


#Kuji iya shege.! 😨😨😨




#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login