Showing 24001 words to 27000 words out of 224143 words

Chapter 9 - DAN MACE COMPLETED Romantic Book .txt

taimaka mata suka je tayi fitsari ta wanke bakinta suka dawo,saman gadon ta sake zama bayanta jingine jikin pillow Hajiya ta fita ta dawo da nurse ta dubata ta fita,sannan ta had'a mata tea ta bata,tana gama sha muryarta har lokacin bata fita sosai tace
"Hajiya me muke yi a hospital.!? Mene ne ya same ni a ciki na naga anyi min d'inki.!?"
Hajiya tace "haihuwa kika yi,amma aiki suka yi miki." Idonta ta d'an bud'e sosai ba kamar da farko ba data tashi da suke a shanye tana kalle² a d'akin,ganin babu jaririnta da aka ce an ciro mata a hankali ta sauke idanunta hawaye suna gangarowa cikin muryar kuka tace
"Hajiya ya mutu ko.!?" Ido Hajiya ta zaro tana kallonta tace "waye ya fad'a miki haka.!?" Tace "Hajiya ai to ban ganshi ba.!"
D'an murmushi Hajiya tayi tana dafa hannunta tace "kada ki damu daughter yaron ki yana nan a raye,an sashi dai a na'ura ne saboda yazo da rashin kuzari,an jima kad'an idan Allah ya kaimu zaki je kiga abunki kinji.!? Ki kwantar da hankali."
Sai lokacin taji wani irin nutsuwa ya saukar mata duk da nauyin da har lokacin take ji a k'irjinta a hankali ta zame jikinta ta amsa ta koma ta kwanta,bayan an fito a masjeed Hajiya ta kira wata nurse d'in ta sake zuwa ta duba jikin nata kafin Dr yazo,da safe Dr Fahad ya shigo duba jikin cos tun tun kafin ya k'araso hospital aka sanar da shi ta farka,yana zuwa ko zama baiyi ba a office ya shiga duba jikin,komai nata yana lafiya sai ciwon da ba'a rasa ba,hajiya ta tambaye shi ko za'a iya bata abinci kuma cos tunda ta farka tea kad'ai ne a cikinta,Dr Fahad yace "Ehh!" Za'a iya bata but ya zama mai ruwa²,sai kuma fruits da za'a k'ara mata da su,saboda wajen yin bayan gida kada ta wahala su samu matsala a aikin nata,godiya Hajiya tayi masa sosai,Dr Fahad ya fita ya barsu tana lallab'a ta,,y'an gidanmu duk da bama zaman dad'i sun je duba Hauwa da yake tana cikin halin jinya sai bata sani ba,ni kuwa tunda aka yi mata aikin naso na zauna nayi jinyarta saboda duk duniya nice tata da ya kamata na zauna da ita bayan mahaifiyar mu,itan bata raye sai ni,ni d'in kuma dana nuna zan zauna da ita Hajiya tace kada na damu naje na kula da gida na ita zata zauna da Hauwa har zuwa lokacin da za'a basu sallama,a zahirin gaskiya mahaifan Rafeek mutanen kirki ne,sun yiwa Hauwa rik'on amana,ko dai ace su suka kawota duniya iya gatan da zasu bata kenan,bare ba su suka haifeta ba matsayin suruka kawai take a gurinsu,ranar da Hauwa ta farka ranar ne farkon da kaji d'umin mahaifiyar da tayi silar zuwanka duniya,lokacin shayar sa kai yayi ta tafi ganinka,yanayin d'akin da kake ciki da yadda yake fitar da hucin zafi saboda yawan na'urori yasa Hauwa ta shiga damuwa,bayan duk damuwar da ta shigo da shi the resemblance of Rafeek in ur face as if it were being torn apart ya sake jefa zuciyarta a damuwa a lokacin da aka ciroka daga incubator aka mik'a mata kai,zuciyarta a raunane take ta kallonka,tunda ta farka take tunanin dalilin da yasa take jin ciwuka sa yawa a ranan but bata iya gano dalilin zamanta a hospital ba,amma lokacin data d'auke ka a karo na farko da niyyar ta shayar da kai yadda al'amarin ya faru ya dawo mata kamar a lokacin ne komai yake occurring,ta daure ta shayar da kai tana kallonka cike da soyayya mai tattare da tausayi take zubar da hawaye,har ta gama shayar da kai bata iya tashi ta fita ba,kana jikinta kana bacci yayin da ita kuma tana ci gaba da kuka tuna yadda komai ya faru,kula da nurse d'in dake d'akin tayi da halin da take ciki yana neman sawa ka fad'o daga jikinta tayi saurin karb'e ka daga hannunta ta mayar cikin na'ura,bin nurse d'in tayi da ido,idanunta suka sauka kan takardar dake jikin na'urar mai d'auke da sunan *RAFEEK Son* a hankali ta kai hannu ta ciro hawaye na ci gaba da zuba a idonta,nurse d'in ta bita da kallon tausayi tana tambayarta ko lafiya,da kyar Hauwa tayi shiru tana kallon rutun har lokacin tace
"Dan Allah y'ar uwa zaki iya min wani taimako.!?"
Tace "fad'i kada ki damu in sha Allah idan ina da yadda zanyi na taimaka miki zanyi"
Godiya Hauwa tayi mata tace "sunan nan nake so ki canja min"
Nurse d'in tace "Ohh! An sawa baby'n suna.!?"
Hauwa tace "Ehh! Ansa masa" murmushi nurse d'in tayi tace "Masha Allah,mene ne sunan.!?" Ba tare da Hauwa tayi shawara da kowa ba tace *"NURAAZ.!"*

"Wow.! But dan Allah zan iya tambayar ki.!?" Nurse d'in ta fad'a tana kallon Hauwa da kanta ke k'asa tace "fad'i tambayarki",tace" Ma'anar sunan nan da kika fad'a dan Allah zaki fad'a min,na ji sunan yamin dad'i sosai",bata d'ago ba tace "Treasure of noor",tace "gaskiya na gode,but nace ba.. Za ki iya min kyautar baby'n ina sonsa sosai",murmushin k'arfin hali tayi ta d'ago kanta dake k'asa tace
"Wannan shi ne farin cikina,amma tunda kina sonsa na baki"
Murmushi nurse d'in tayi cikin jin dad'i tace "Kai amma gaskiya na gode sosai,kyautar baby sukutum,Allah dai ya k'ara muku lafiya Maman baby"
Hauwa tace "amin'',tana zaune nurse d'in tana mata hira tunda ta kula tana cikin damuwa,har ta rubuta sunan tace mata "kinga sunan yayi.!?"
Da kyar Hauwa ta sake d'aga kai ta kalli takardar,ganin *NURAZ RAFEEK* a jiki bar'o² wasu hawayen suka sake taho mata,da sauri ta girgiza kai tace "A'a" kasa fahimtar abunda take nufi nurse d'in tayi har ta matso kusa da ita tace "bai yiba kenan sunan.!?" Ta gyad'a mata kai "me za'a rubuta to.!?" Sai data share hawayenta tana sake kallon yaronta dake kwance cikin incubator jikinsa duk anyi connecting na'urori yana bacci tace
*"NURAZ BIN HAUWA."*




*#Posting abun so ga reader's,#Comments abincin writer's,mu daku kamar k'waryar sama dana k'asa ne,idan akwai d'aya babu d'aya al'amarin baya tafiya dai²,it's better ace mun faranta ran wad'anda suke k'aunar mu fisabilillah.!*




#Share.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*



*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥




*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2




Pᴀɢᴇ 8.
#Hᴜᴍɪʟɪᴀᴛɪɴɢ

Kallonta nurse d'in ta dunga yi kamar taga bak'uwar halitta,can da taga ba zata iya shiru ba ta janyo kujera ta zauna tana kallon Hauwa tace
"Dan Allah kiyi hak'uri y'ar uwa idan har maganata zata sa kiji babu dad'i" da kai Hauwa ta amsa mata saboda kukan da take har a lokacin yak'i bari tayi magana,nurse d'in tace "Idan babu damuwa can we be a sister's so that sai muyi maganar a matsayin y'an uwa ba mai kula da yaro ba.!?"
Hauwa ta sake kad'a mata kai,godiya tayi mata sannan tace "dan Allah mene ne dalilin da yasa kika ce asa masa sunanki al'halin na san yana da mahaifi.!?"
Sai da tayi k'ok'arin tsayar da sababbin hawayen dake sake taho mata sannan tayiwa nurse d'in tak'aitaccen bayani akan matsalolin da suka samu wanda sune silar da suka janyo musu fad'awa mawuyacin halin da suka tsinci kansu a ciki,da ta samu ta d'an fad'awa nurse d'in,wacce lokaci d'aya taji har zuciyarta ta aminta da ita,wani irin kuka take tunda ta samu ta fitar da maganar daga ranta,burinta kenan a lokacin yadda take ciki damuwa ta samu wanda zata fitarwa da maganar ko zata huta da rad'ad'in dake addabarta,tausayin Hauwa da baby yasa nurse bata gama jin labarinsu ba sai da tayi musu hawaye,tana kallon Hauwa bayan sun gama maganar tace "kada ki damu yar uwata,in sha Allah komai mai wucewa ne,,da yardar Allah lokaci zai zo da Rafeek zai neme ku duka,a lokacin zaiji kunyar wulak'anta kyautar da Allah yayi masa,in Allah ya yarda sai Yaron da nuna baya k'auna ya zame masa jigon da bazai tab'a samun kamarsa ba a rayuwa,,fatan da zan masa shi ne Allah ya nuna masa hanyar gaskiya komai tsayin lokaci..",sun jima sosai nurse d'in tana mata hira saboda tana son rage mata damuwa,da Hauwa zata tafi nurse d'in ta fad'a mata sunanta *AAEDAA* Hauwa ta mata sallama ta koma room d'in da take,da yake duka a ward d'aya suke,tana shiga d'akin su Hajiya suna zaune tun fitarta suna hira da Maimunatu,tayi sallama suka amsa ta wuce saman gado ta kwanta tayi shiru bata sake magana da kowa ba,,bayan wani lokaci Hajiya taje ganin Yaro ta tarar da abunda Hauwa tayi,tazo tana mata fad'an me yasa zata yi haka,al'halin kowa yasan Yaro nasu ne ita da Rafeek.? Babu kunya Hauwa ta fashe da kuka but ta kasa magana,Hajiya jikinta yayi sanyi ta matso ta rarrasheta,Hauwa tayi shiru cikin sanyi da lallami Hajiya ta tambayeta ko me yasa tayi hakan.? Bata b'oye ba ta sanar da Hajiya kaf abunda ya faru a ranar da incidence d'in ya faru,Hajiya taji bak'in cikin abunda ya faru musamman sakin da Rafeek yayi,amma da yake babu yadda za tayi tunda ya riga ya yanke hukunci tace "ai shi kenan,kansa ya cuta ba ni ba,Allah ya baki lafiya daughter,kiyi hak'uri da duk abunda zai faru,in sha Allah tunda yace baya son yaron nan sai ya zama mafi k'ololuwar alkhairi a rayuwarsa,da yardar Allah zai yi nadamar abunda ya aikata a nan gaba" a zuci hauwa tace "Allah yasa"
Hajiya dake rike da ita tace "maza kwanta ki huta kinji,Allah ya k'ara muku lafiya",da Alhaji yazo duba su shima lokacin da Hajiya ta fad'a masa ya ji bak'in ciki sosai,har yaji ina ma ace yana da wani d'an namiji,da a yau ya d'aura musu aure da Hauwa ko dan ya huce takaici da kunyar da Rafeek yasa shi ji,sai dai da yake y'ay'an duka guda biyu ne Allah ya azurta su da su bayan wanda suka binne guda uku,biyu b'ari d'ayan kuma an haifeshi rayuwar ce da Allah bai nufa zaiyi mai tsayi ba shi yasa tun yana jariri ya karb'i kayansa,Alhaji ya yiwa baby khud'ba da suna *NURAZ* kamar yadda Hauwa ta zab'a,,a kullum duk wanda zai d'auke ka tunda aka yi haihuwar duk da babu wanda ya san abunda yake faruwa har lokacin,addu'ah yake Allah yasa ka kasance haske ga mahaifiyarka kamar yadda ta ambaceka,,bayan shafe kwanaki da aka rik'e ku a hospital aka sallamo ku muka dawo gida,Hajiya taci gaba da kula da ku,kullum rana tunda kuka fito daga hospital na kasance ina tafe akan hanyar gidana da gidan kakanninka ba dan komai ba sai dan na duba yaya kuke,har Allah yasa duka kuka samu lafiya,kamar yadda kullum ake sake samun ci gaba,kana girmanka da wayo,Hauwa kuma ta koma shiru ta daina hira da kowa kullum cikin keb'e kanta take daga idanun mutane.


*Ina labarin RAFEEK..!??*


B'angaren Rafeek (mahaifinka) kam tun daga wannan tafiyar da ya bar gida cikin fushi,sai ya kasance bai sake waiwayen gida ba,a waya idan an kira babu wanda yake samunsa,shima kuma baya kiran kowa,,tun ranar da Hauwa ta haihu da Hajiya ta buga waya ta fad'a masa,ya daure yace "Allah ya raya" daga haka har ta gama maganar da zata yi bai sake cewa komai ba,lokacin da suka samu labarin abunda ya faru tsakaninsu a bakin Hauwa Alhaji zakar ya kirashi yayi masa tas,shi ne ya sake jin haushin Hauwa akan ta had'a shi fad'a da mahaifansa suna ganin laifinsa,suna gama waya a lokacin gaba d'aya ya cire sim cards d'in ya canja wasu,a cewarsa tunda sun zab'i zama da ita suje suyi ta sonta,shi ya hak'ura zai zauna a nan har zuwa sanda zasu gane gaskiyar abunda yake son su fahimta.
Zamansa a k'asar bayan y'an wattani ya kama aiki da yake lokacin ya kammala karatunsa,cikin hukuncin ubangiji tunda ya fara aiki da skul d'in da yaje karatun a matsayin lecturer a b'angaren Economics,ko shekara bai kai da farawa ba world bank suka yi sanarwar neman kwararru a b'angaren Economics,da yake harka ce ta kwakwalwa kuma Alhamdulillah Rafeek yana da k'ok'ari sosai tun kafin yaji labarin wasu abokansa da suke tare a k'asar suka shawarce ko zai gwada sa'ar sa,ya tura details d'insa through mail da suka bada,bayan turawa Rafeek ya duk'ufa addu'ah ba da wasa ba,tunda ya tura yake jiran amsar su still yana ci gaba da aikinsa,a weeks later da tura details suka masa replying idan ya shiryawa special exam d'insu ya tuntub'e su duk lokacin daya samu damar shigowa k'asar,cike da farin ciki lokacin da yaga sak'on ya tattara komansa a satin ya bar k'asar bcos dama zaman k'asar ya isheshi taurin kai ne yasa shi zama,ya tura takardar ban hak'uri ga hukumar collage d'in da yake aiki ya ajiye musu aikinsu,lokacin da jirginsu yayi arriving a babban birnin *WASHINGTON* charter taxi ya samu da zai kaishi masauki,ya samu hotel mafi kusa da 1818 street ya sauka,,kwana biyu da zuwansa k'asar bayan ya huta sannan yayi shirin tunkarar world bank headquarter,daga hotel d'in daya sauka zuwa headquarter babu wani nisa sosai,duka baifi mutum ya taka da k'afa ba,,a cikin sama da mutum d'ari daga k'asashen duniya mabambanta Rafeek becomes *CONQUEROR* bayan special exam da suka yi,ya samu damar zamowa d'aya daga cikin ma'aikatan su,,yanayin gogewarsa a b'angarensa cikin tak'aitaccen lokaci da kama aiki ya zamo wani jigo a gurinsu,tunda ya fara aiki ya rik'e aikinsa da gaskiya babu wasa,ci gaban rayuwa ya kasance yana zuwa masa a kowane yini like brightening burning light,a gefe guda tunanin gida da mahaifansa kullum yana mak'ale da zuciyarsa,but a ganinsa har lokacin tunaninsa shi ne ya basu lokaci da yake ganin idan har basu nemesa ba shi zai koma musu a lokacin da zai gama duk wasu shirye² na korar Hauwa daga gidan.


Har aka shekara guda da watanni da haihuwarka babu wanda yasan duniyar da Rafeek ya shiga,wayoyinsa idan an kira ba'a samu,anbi sahunsa k'asar ana tunanin ko wani abu ya same shi ba'a same shi ba sai labarin tafiyarsa birnin Washington aka tsinto,ran Alhaji zakar ya sake b'aci,a lokacin daya fahimci nufin Rafeek ya yanke hukuncin babu ruwansa da shi daga nan har zuwa ranar da zai dawo,,a wannan d'an tsakani da aka samu na haihuwarka al'amura suka yi ta faruwa,nima nawa gefen Allah ya karb'i rayuwar mai gidana,hatsari ya runtsa da su a hanyarsu ta zuwa lagos,,Hauwa da kai har lokacin kuna gidan kakanninka,duk da a farkon dawowa ta gida naso ku dawo gurina mu zauna tare a gidanmu tun bayan dana gama iddah,but yadda Alhaji zakar da iyalinsa suka tsaya kan al'amuran ku da kunya irin ta bafulatani yasa sai na kasa fitowa na fad'i abunda ke raina,haka nayi ta zuba ido kullum a gurina kake wuni,har Hauwa suka fara k'ok'arin yin exam zuwanta bai dai²ta ba sai Maimunatu kad'ai take zuwa wasu lokutan saboda damuwar da take ciki ya fara affecting tunaninta,,a wata ranar Talata da rana bayan sun dawo daga hospital suna zaune a parlor Maimunatu na bawa Hajiya labarin matsalar da doctor yace zata iya samunta nan gaba kad'an idan bata ragewa kanta damuwa ba,Hajiya tana mata nasihar ta maida komai ba komai ba,suka tsinkayi sallama daga bakin entrance,shiru duka suka d'auka Maimunatu na kallon Hajiya cikin tsananin mamaki tace
"Hajiya kamar muryar Yah Rafeek ko.?"
Kallonta Hajiya tayi tana had'e rai tace "ban sani ba,sai dai ki duba ki gani"
Hauwa ta shiga rud'ani da tunanin anya shi d'in ne da gaske tunda gaba d'aya lokaci ya tafi da tunanin baza ta sake ganinsa ba,Maimunatu ta daure ta amsa sallamar,tun kafin taje ta duba a bashi izinin shigowa ya bayyana,yana sanye cikin shiga ta alfarma d'an gayu da shi ya had'e cikin wani d'anyen suit mai matuk'ar tsada daya fito daga company'n armani,duk wanda ya kalleshi dole ya sake dan yadda ya dawo tun daga kan tsarin outfit da gyaran kansa sak bature,gaba d'ayansu kallonsa suke yi da wani irin mamakin dama yana raye a cikin duniyar,fuskarsa babu wanda ya kasa shaida ta tunda shi d'in ba bak'o bane bare ace sun kasa tantance shi,ya tsaya gaban Hajiya yana niyyar durk'usawa ya sake tabbatar msusu lallai Rafeek d'in ne da gaske,to amma yanayin sauyawar da yayi da irin tufafin da ke jikinsa yasa suke ta binsa da kallo,shi kam tunda ya shigo babu wanda ya kalla a cikinsu Maimunatu fuskarsa nan a d'aure kamar wanda yayi gamo da mutuwa,kansa a k'asa ya tunda ya durk'usa ya magana,yanayin yadda yayi shi zai tabbatarwa da duk wani mai ido lallai ya aikata gagarumin laifin da yake son neman yafiya,but kamar wanda ya rasa baki haka yayi ta zama da sunkuyayyen kai ya kasa d'agowa bare ya fuskance ta,Hajiya da duk wanda yake cikin parlor'n gaba d'aya sai kallonsa suke babu wanda ya iya magana har bayan wani lokaci sannan Hajiya tana jinjina kai tace
"Rafeek.! Idonka kenan ko.? Anya kana son gamawa da duniyar nan lafiya,kana buk'atar albarka kuwa.!?"
Ya sake sunkuyar da kai kamar zai tsaga k'asa ya shige cikin dauriya muryarsa na wani irin karkarwa yace
"Ki garfaceni Hajiya ta,wollahi ba'a son raina na aikata haka ba,,kiyi hak'uri ki yafe.."


Bai k'arasa ba ta dakatar da shi cikin fad'a² "Rafeek baka da bakin da zaka nemi yafiyata,tun da wuri kuma muna shaidar juna maza ka tashi ka fice min a gida kafin na sab'a maka."
Saurin rik'o k'afafunta yayi,Hajiya ta lumshe idanu ta bud'e tana d'an janye k'afafunta,ya sake rik'owa sosai muryarsa na ci gaba da rawa yace
"Dan Allah Hajiya ta ki gafarce ni,wollahi na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login