Showing 12001 words to 15000 words out of 46437 words

Chapter 5 - MIJIN MARAINIYA Book Complete BY Fadeela Lamido.txt

Advertisement

10 Jan 2025

9496

tausayin safna yakama jalal besan lokacin da yasata akirjishi ba itama lafewa tayi kamar karama yarinya yace safna kema suna sonki, nima kuma Ina matukar sonki dan haka karki kara cewa baki da kowa, mune dangin ki.
a,a yaya ummi bazata bari ka aure ni ba.
a hankali yace safna karki kara kiran sunan ummi akan wannan maganar ba runwan ki ,nidai kawai abinda nake so dake , idan daddy ya tambaye ki kice ni kike so , kinji?


suna cikin haka sukaji anturo kofar miryar ummi sukaji tace jalal.
zabura sukayi da sauri yasake ta.
ummi tace zoka wuce daddyn ka nakira, jalal wucewa yayi yana sosa kai yabar ummi adakin.




***********


safna bakin gadon tabi ta zauna, ummi ta harare ta, tace yar iska kawai zata koyawa yaro iskanci, in Allah ya yarda saikin bar gidan nan, baza kizo ki lalata mana yaro ba.


bayan kwana biyu hakalin jalal ya kara tashi dan yaga sai shirye shirye ake agidan ya sake koma wa wajan alhaji ya kara gayamai shifa babu wacce yake so sai safna
alhaji yace wai dama da gaske kake ne, aina dauka wasa kakeyi, to kabari zanyi shawara.
ran jalal beso haka ba amman yasan abinda zaiyi yace daddy yau gidan hajiya zani.
alhji yace ya kamata jalal inkaje ka gaida ta, yace tare da safna zantafi, kafin alhj yace wani abu ummi ta shigo Ina zaka da safnan kuma?
gidan hajiya zamu.
alhaji karma barshi ya tafi da ita ban yadda da jalal ba ,ya canza hali.
alhj yace wani irin magana ne wan kuma.
wlh alhaji rannan ganin jalal nayi rungume da safna kaga kuma be kamata suna fita waje tare ba.
alhaji ya kalli jalal, yace abduljalal haka ne?
shiro yayi ya dukar da Kai, alhji yace tashi ka bani waje. jalal yaso ya leka gurin su safna amman ya fasa ya wuce gidan hajiya.



hajiya mahaifiyar alhaji ce kakar jalal tana matukar son jalal dan duk cikin jikokinta shi kadai ne namiji sauran duk matane kuma kanana ne yayanta guda uku ne mahaifin abdul jalal shine babba sai kaninsa wadan yanzun ne ya samu haihuwa yarssa mace kusan garman su daya da kairat sai kanwar su mace anty nusaiba bata dade dayin aure ba tun lokacin da alhaji ya kawo zaliha amatsayin wacce zai aura, hajiya ta nuna batayi na am ba, amman daga baya taga ya matsa ta hakura akayi.
bayan ummi ta haifi jalal suka gane bata son mutane duk wanda yaje gidañ saita mai wula kanci, dan haka suka hakura da zuwa gidan.


jalal ya shiga gidan hajiya tun abakin falo yake fadin matassss.
ah,ah dan duniya saiyau ka tuna damu


daidai lokacin jalal ya shiga falo yaje kusa da ita ya zauna, yace wlh hajiya kina raina abubuwa ne suka min yawa, shiyasa baki ganni ba.
kai dai kace mahaifiyar ka ta hanaka zuwa koda yake harda laifin baban ka aishi kullum yana zuwa ai sai ya tasoka gaba, amman ku kuka sani, nidai kujera ce.
jalal yace hajiya kiyi hakuri ni bawan da ya hanani zuwa, ni yanzun ma akwai abinda ya kawoni.
toh ina jinka me ya kawo ka.
ya kwashe duk abinda yake faruwa ya gayawa hajiya.
dariya tayi tace jalal ai ina da lbrn komi baban ka yagaya min komai tsokanan ka yake amman har an tsai da ranar biki sati uku masu zuwa , karka kara tada hankalin ka , me yasa baka taho da safna ba, ko baka son naga kishiya ta.
hajiya wai dan Allah da gaske kike yi?
jalal na taba irin wannan wasan ne dakai?
hajiya bari naje gobe zan dawo
yana shiga gida yasamu alhaji afalo alhji yayi dariya yace jalal kadawo daga kai karar tawa ne?
jalal ya sosa kai yace ba haka bane daddy ni gai sheta naje .
jalal kana nufin ban san halin da kake ciki bane, nagane kana son safna tun ranar da naga kishinta karara a idon ka, amman sai kamin karya kace basan ta kake ba, kuma nama haka ne dan kar ka ga kasa meta asauki nan gaba kace zaka wulanta ta jalal safna itama mutun ce kamar kowa duk son da nake maka inhar ka wulakanta ta , zamu raba hanya dakai




kuma daga yau na haramta ma shiga dakin safna, inzaku yi hira kuyi afalo , suna cikin haka ummi ta fito , alhaji yace kafin kizauna kiramin safna.
ummi ta shiga ta kama kunnen safna ta rike sannan tace idan alhj ya tambaye ki kina son jalal kice a,a, idon safna cike da kwalla tace toh ummi.
suna zuwa safna ta zauna akasa, ummi ko tunkan ta fito tawashe fuska,
alhj ya kalli safna yayi murmushi yace yace safna ki fara shiri bikin ku nan da sati uku masu zuwa na zaba miki yayan ki jalal.
zufane ya fara karyo ma ummi tace alhj ita baka tambaye ta ko tana sonshi ba.
a,a basai na tambaye taba nasan ma tana sonshi ai dama tare muka gansu.
Jalal ya kalli safna yayi murmushi, itako safna kanta na kasa banda far gaba ba abin da yake damun ta.
alhj yace jalal naga kamar bakinka akwai magana?
daddy ranar ne naga kamar yayi yawa ko za ,a dan rage ne
ummi mikewa tayi ta buga tsaki tashige daki, tashiga tunani gakiya nayi kuskure dahar na bari wata alaka tashiga tsakin sultan da safna gashi aure yana neman shiga tsakanin ta da dana kuma zaiyi wuya ace sultan bashi da H.I .V
[7:02PM, 12/1/2016] Fadeela lamido: 💘💍💍MIJIN MARAINIYA💍💍💘






Story
&
Written by
Fadeela Lamido
Mmn Yazeed📝




35- 40




Ummi kwana tayi kuka ta shiga damuwa mutuka atake tunanin iyayan ta ya fado mata haka iyaye sukeji idan suga dan su zai shiga cikin wani hali, to yanzun wani hali iyayan ta suke ciki na rashin ta da sukayi, yau she rabon ta da ganin su, tun kusan shekara goma shatara da suka wuce lokacin jalal yana karami,
bazata manta ba tun lokacin da sukazo kawayen ta na gidan tace musu suyi sauri su koma gida kar kawayan ta sugan su tanan zuwa, suka tafi cikin bacin rai, suna fadin tunda baki son agan mu a matsayin iyayenki karki kara zuwa inda muke, taso washe gari tabisu tabasu hakuri amman tana cikin shirin tafiya saiga yayarta rabi tazo cikin kuka tana gaya mata cewa jiya dasu baffa suka zo gurinki sun taho da saudatu ba aganta ba taba ce, sanadi haka baffa yana cen ba lfy mama ma ba lfy ta cika ba, yan zon nazone kizo muje nemanta ko Allah zai sa adace,
ummi kin binta tayi ta dauko kudi ta mika mata tace kije ki duba ta nima ba lfyr gareni ba, in nashiga rana ciwona zai iya tashi kije duk halin da ake ciki kizo kisanar dani.
yaya rabi batayi musu ba ta wuce , haka yaya rabi tayi ta zaga gari har tsawon kwana uku tasake dawowa gurin ummi akarshe dai ummi koran kare ta mata tun daga ranar babu wanda ya sake zuwa gidan ayanzun haka ummi bata saniba ko anga saudatu ko ba,agan ta ba, amman ita tana ganin angan ta, haka ummi taita tunanin baya, tare da ganin wautan ta da ta bari har haka ya faru, yanzun ya zatayi ta shawo kan iyayen ta kilama alhakin iyayen tane gashi yanzun har ansa ranar auren jalal dan cikinta amman ba,ayi shawara da itaba, dan ba,a dauketa abakin komai ba alhj yanuna mata iyayen sa suna da mahim manci yaje yayi shawara dasu hakadai ummi taita tunani kafin gari ya waye idon ta yayi ja sunkun bura.




koda alhaji ya shiga dakin ummi da safe yasame ta cikin wannan hali yayi tunanin kin auren ne ya dame ta, bece komi akaiba yayi mata sallama ya fito.


alhj da jalal ne tafe amota alhji yace jalal kasan ina zamu ,jalal yace a,a


zan kaikane kaga wani abokin ka, tafiya sikayi sosai sannan suka isa wani gida dan madai daici mai kyau, suka shiga da sallama, wata tsohowa ya gani tana shara tana ganin alhaji ta sake tsin tsiyar cikin Fara,a , ta dauko tabarma ta fara kokarin shinfidawa sannu da zuwa alhaji bari na fadawa baban Ku, bayan wasu yan mituna baffa ya fito yana fadin sanu da zuwa kai dawa kake tafe yau kuma,
yace baffa jalal ne.
cikin bacin rai baffa yace ba munyi dakai daga mahaifiyar shi har shi bazaka nuna wa kowa nan ba.



alhaji yace baffa kayi hakuri ganinayi bayi da lefi kuma be dace muyi ta tafiya ahaka ba, yanzun gashi jalal har zaiyi aure, haka alhaji yayi ta jan hankalin baffa sannan ya kalli jalal yakama hannun shi yace kodan maihaifin ka ,bana kika ba, abduljalal maifinka yamin abinda 'yata da haifa ta kasa yi min, mahaifiyar ka kunya ma takeji ace mune muka haifeta saboda tayi kudi baffa kasa magana yayi ya fashe da kuka mama ma tana daga gefe tana share hawaye.
jalal da be gane suba dan rabon shi dasu tun yana karami sai a magan ganun sune ya fahimci kakannin shine iyayan ummi, tausayin su ya kama shi daman ba wuyar kuka gareshi ba, tuni hawaye suka fara ambaliya afuskar shi ya kama hannun tsohon ya shiga bashi hakuri sai da yaga hankalin su ya kwanta sannan yace yauwa baffa ina anty saudatu yanzu? nan danan suka kara barkewa da sabon kuka suna bawa jalal lbrn batan saudatu haka sukai ta kuka har jalal , jalal ji yayi ya tsani ummin sa kwata kwata ya dade yana tambayan ta su sai tace yabar maganar bata so.
haka sukawa su baffa wuni sai yamma suka taho bayan sun cika su da tsara ba, saidai sunce su ba wanda zaizo biki daga barayin su, saidai wata rana yakawo musu amarya su gani jalal yanata basu hakuri,
amman suka ki.



******




shirye sheryen biki nata tafiya gidan hajiya kamar cenne gidan bikin acan ake shirya komai .
ummi bata kara tada zancen auren ba illah hankalinta ba akwance yake ba, kulum cikin kuka take, tarasa yaya zatayi ta dakatar da wannan auran.
Jalal kuwa ayanzun gani yake mahaifin shi beyi dacen mata ba yakamata daddy ya kara aure dan koshi da ana cenza uwa da ya cenza ummi dan ko ganinta bayasan yi.




ana jibi daurin aure kanwar alhaji anty nusaiba da matar kanin alhaji hajiya fatima da wasu mata su hudu yan uwan hajiya, suka faka faka jibge giyar motan su a haraban gidan alhaji, rabon su da zuwa gidan sun dade, wata motar na biye da nasu,
direban motocin suka fara fito da akwatuna masu kyau daga cikin motar sukuwa matan tuni suka shiga gidan.


sunata sallama a falon har suka gaji ba,a amsa musuba suka nemi guri suka zauna , bayan anshigo da akwatunan ne , aka fara shigo da kayan abinci, anty nusaiba ce take nuna inda za,a ajiye komai, ummi dake kwance tana kuka taji mutsi yayi yawa ta share hawayen ta tafito, mutane ta gani cike da falon, nusaiba kawai ta shaida.


nusaiba ta fara mata bayani anty munshigo munata sallama gidan shiru.


eh wlh kaina ke cewo nadan kwanta.


nusaiba tace gakayan safna nan mun kawo ki duba ki gani.
ummi ta zauna suka fara budewa lallai alhaji ya kashe kudi wannan uban kayan duk na safna ne , aikowa safna bazata sasu ita daya ba,
bayan sun maida akwatin sun rufe, anty nusaiba tace mufa munzo kenan sai bayan baki.
ummi tayi yake tace ai yakamata tunda kune kirjin biki.
hajiya fatima tace ina amaryar tamu ko taje kunshi ne?
sai alokacin ummi ta tuna da wata safna, tace anya kuwa inajin tana daki.


anty nusaiba tamike tashiga dakin ta hango safna makure agado ta xata bacci take sai da ta taba ta taga ashe kuka takeyi.
itako safna ta zata ummi ce dan haka ta mike afirgece, da sauri anty nusaiba ta riketa suka kalli juna, nusaiba tace safna me yasame ki kike kuka, ko baki son auren ne? girgiza kai tayi.
to me yake damunki?
koda safna bata san anty nusaiba saita tsinci kanta da cewa tunanin iyayena nakeyi da kakata,
nusaiba ta tausaya mata tace safna ardua zakiyi musu ba kuka ba, tana buye hawayen ta sake cewa me yasa bakiyi kunshi ba, zo naga kan ki, ta bude kan taga tsohon kitsone, ta kwatar da safna akan cinyar ta tafara warware mata kitson , haye na zuba afuskar ta 😭😭😭




07014197556✍
[8:34PM, 12/2/2016] Fadeela lamido: 💘💍💍MIJIN MARAINIYA💍💍💘






Story
&
Written by
Fadeela Lamido
Mmn Yazeed




41-45




Anty nusaiba na tsefe wa safna kai tana tunanin ga yarinya me kyau amma gwanin ban tau sayi, bayan ta gama tsefe mata kai taji muryar jalal suna gaisawa da mutane afalo dan haka ta kwala mai kira, ya amsa ya mike ya nufi dakin safna ummi ce ta dakatar dashi yadawo tace ba alhaji ya hanaka shiga dakin safna ba?
eh amman yanzun bakiji anty na kira na bane.
rasa abin cewa tayi dan haka jalal ya juya ya shiga dakin lokacin da jalal ya shigo dakin safna tana bayi tana wanka.
Jalal yace dama ke kadai ce adakin?
anty tace nida safna ne yanzun ta shiga wanka, kai kuma haka ake yi baza ka ba amarya kudin lalleba ko haka kake son akai maka ita.
toh ni anty babu wadda yace na bada kudin lalle agidan nan nifah da daddy kawai muke shirye shiyen mu agidan nan kinga mu bamu san yadda akeyi ba, anty kinsa ma wani abu kuwa rabon da naga safna na man ta in na,aika kairat ta kirata sai tace ta cemin tayi bacci, ko kiranta nayi awaya bata dauka, ni ina tunanin ma babu wanda ta gaiyata katin ma dana aiki kairat takai mata dawo min dashi tayi wai bata da wanda zata bawa, dan haka na barta .


anty nusaiba ta nisa tace ai irin wannan da sai ka gayawa ummin ka ta mata fada.
wace ummi, ai ummi bason auren nan take ba, ni ina tunanin kamar ma itace take firgita, ta haka sukai ta tattanawa tsakani su, anty nusaiba tace wai safna har yanzun baki gama wanka bane?
safna dake tsaye abayi duk firan da suke tana jinsu tace nagama anty, namanta ne ban shigo da hajjab ba. anty tace au haka ne cikin dariya tace jalal tashi ka fita inta gama shirya wa sai kadawo.


jalal yace a,a anty ta fito kawai ni babu ruwana da ita ba kallonta zanyi ba.
anty tayi tayi jalal ya fita yaki fita, tashi da kanta ta dauko hijjab kato ta mikawa safna, tasa sannan ta fito kanta akasa dan yanzun wani irin kunyar jalal takeji, tashige cen longu ta zauna ta fara shafa mai, acikin hijjab take shafawa jalal Nata kallon ta, cen yace bazaki gaishe ni bane, kafin ya rufe baki tace ina wuni, shiru yayi sai cen yace bazan amsa ba, saida naroka, safna tace ina fa shirin gaisheka kayi magana.


toh nidai bazan amsa gaisuwa daga nesa ba, saikin matso kusa dani.
safna tana kokarin ajiye man shafawa tace inazuwa bari nasa kaya.
a,a kizo ahaka.


anty tana gefe ta jin su tace ke dauki kayanki kishiga bayi ki saka, wai dama jalal ashe baka da kunya haka, agaba na .
jalal yace to menayi kuma daga nace ta matso kusa dani.
safna bata saurari me suke cewaba tashiga bayi tasaka kaya dogowar riga tasaka na atamfa tayi kyau duk da bawani kwalliya tayi sosai ba, ta dora karami hijjab akai sannan ta fito, gurin jalal ta nufa tace ina wuni, mamayan ta yayi ya rike hunnuwan ta, yace tsorona kikeji kuma.
tsugunawa tayi tana boye fuskar ta cikin cinyoyinta shiko jalal yana rike da hannuwan ta yana kokarin daka kanta, ciki ciki suke sosai safna da jalal waishi dole sai yaga fuskarta itakuma taki bari ,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login