Showing 3001 words to 6000 words out of 21708 words
Chapter 2 - CELEBRITY FARASHIN TASIRI Book Complete by Mrs Sadauki .txt
da ta taɓa zuwa a haka har mu ka sauka.
“Ga lambar wayata in kin samu lokaci sai ki kira ni, wannan kuma ki sayi ƙaramar waya da su” wani ɗan ƙaramin kwali ne mai ɗauke da number ta sai 10k sabuwa dal.
Hannuna har rawa yake na karɓa, lokacin da hannuna suka samun contact da kuɗin nan tamkar wacce aka yi wa wankin ƙwalwa haka na ji burina ya ƙara bunƙasa.
Bayan mun sauka, Raheela ta ce “wai hirar mice ce kuke ta yi da hajiyar nan?”
“Labaran duniya,kin ga ki saki ƙafa mu yi sauri mu ƙarasa gida na matsu na ga Innata” na faɗa tare da canza akalar zancen.
Haka kuwa aka yi ba ta sake yi min zancen ba,mu na tafe ta na min hirar Hafiz abokin Sadiq yadda ya nuna ya na sonta kuma aurenta zai yi.
A bakin ƙofa na tarar da Inna da ƙaton bokitin kokon da take sayar wa.Mu ka rungume juna cikin murna bisanin ta ja ni zuwa cikin ruɓaɓen ɗakinmu wanda ina yin tozali da shi na ji raina ya ɓace don a ɗan zamana birni na saba cikin villa.
Bisa tabarmar kaba na zauna,Inna ta kawo min ruwa haka na daure na shan ruwan rijiya bisanin kuma na fita zuwa shagon ɗan Idi mai sayar da waya.Dubu shidda ya sayar min da wata ƙaramar waya sai kuma ya ban layin airtel kyauta.Shi ya daidaita min komai bisanin ya saka min ita a caji don gida ba mu da wuta.Kamar abun tsiya haka na zauna na yi ta zaman jira har sai da ta ida cika sannan na karɓa na nufi gida.
Lambar Hajiya na loda tare da kira,bugu biyu ta ɗaga ta na ƴar dariya “dama na san za ki kira....”
[31/08 à 12:51] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️
MRS SADAUKI 💫✍️
FCWA ☀️
Special gift fo my VIA FANS 🪷
*Masu buƙatar littataina na kuɗi ku zo na yi maku bonus maimakon 500 za ku iya biyan 300 domin samun littafi complete wacce ta shirya ta min magana ta WhatsApp* +22795045822
Page 3
“Eh Hajiya! Duk na kasa sukuni shine na je na sayi wayar”
“Dama na sani ai ! Yaushe za ki koma Maraɗi?”
“Hutun kwana goma ne ba zo yi” na bata amsa .
“Ayya! Ni kuwa ina cewa gobe za mu je kanti ki sayi kayan da kike so sai mu wuce wurin gyaran jiki.” Hajiya ta faɗa cikin wata irin murya mai jan hankalin mai muradi.
Cike da zumuɗi da kuma son banza na ce “ai zan iya zuwa in kin min sayayyar sai na dawo ko ya kika ce?”
“Har dai ki zo ɗin zan san yadda za mu tsara komai” ta furta.
“To Hajiya amma ya za a yi na gan ki”
“Kin ji wani shirme kuma,ke da kike da wayar hannu kawai kira na za ki yi sai na aiko direbana ya ɗauko ki”
Na washe baki jin an ambaci mota don ta na ɗaya daga cikin manyan burina.
“To Hajiya Allah saka da alkhairi ” na furta cikin jin daɗi.
“Amen! Sai an jima zan yi wani aiki” ba tare da ko ta jira abin da zan ce ba ta kashe kiran.
Na ja ajiyar zuciya bisanin na kwanta kan tabarma.Ina nan zaune Inna ta shigo da langa ,a gabana ta ajiye ta na mai cewa “ga alala nan ki ci,a zubo miki kokon?”
“A'a Inna alalar ma ta isa” na faɗa ina jawo langar na fara cin alalar a zuci kuma faɗi nake ina ƙari ‘ nan da wani lokaci za mu yi hannun riga da duk wani abincin tallakawa,mu rinƙa shan madara da ƙwai da haƙarkarin kaji’ sai kuma na yi dariyar kaina .
Gurbin zuciyata ya cika fam da dogon buri wanda a yanzu dab yake da cika.
Ina gama ci na sha ruwa sannan na jawo matashin kai na rungume,lambar Sadiq na kira wacce ta daɗe a kaina.
Ya na ɗagawa mu ka gaisa sai kuma kuɗin suka ida,shi ya sake kirana ya na mai cewa “Jameela ina kika samu waya?”
“Tawa ce,yau na saye ta” na basa amsa.
“Madallah! Na ji daɗi sosai yanzu kin ga sai mu yi ta shan hira kafin ki dawo.Da ina cewa Hafiz ya ban lambar Raheela sai mu rinƙa waya”
“Hum! Saurayinta ya saya mata waya kai kuma ka dinga yin hira da budurwarka ko?” na cikin jin haushi saboda satin can da ya wuce Hafiz ya saya wa Raheela ƙaramar waya.
“Jameela kin san da ina da kuɗi da tun tuni na saya miki,wlh ni ma ba a son raina ba ne.”
“Ba wani har ce min ka yi za ka bani tsohuwar taka muddin ka canza amma kuma daga ƙarshe ka ƙi”
“Jameela tun ranar nan na faɗa miki Mama ce ba ta ji daɗin jikinta ba shi yasa na sayar da ita na sayo mata magani ”
“Hum! Na ji masu Mama”
“Ke ma ai Mamar ki ce,ya ne ya ƴan gidan fatan kowa lafiya?”
Na amsa da “ alhamdullah! Abba ya tafi gona Inna kuma na waje ta na sayar da koko”
“Ke kuma ki na me?”
“Kwance ina huta wa!” na basa amsa.
“Hhh! My Jamee in kin samu gidan hutu sosai za ki ƙara kyau farin ki ya fito,shi yasa nake ta fafutukar neman kuɗin auren ki”
Dariya ya ban sosai,saboda bai wata sana'a sai shap-shap wani sa'in kuma ya kan taɓa kabu-kabu domin samun kuɗin da zai sa mai a babur ɗin.
“Kai da ke zaune gida shine za ka ce ka na fafutuka? Wai ina katin da kake sayarwa ne? A turo min na 200 ”
“Yanzu kuwa” ya faɗa tare da kashewa,500 ya turo min na yi masa text na godiya bisanin na fara kiran duk wanda na san ya na da waya.
Wuraren magrib Abba ya dawo gida.
“Ah su Jameela ƴan makaranta ,yanzu Innarki ke ce min kin zo hutu ”
“Eh wlh Abba ,sai kuma na samu kira daga can makaranta gobe za mu zana wata jarabawa dole zan koma” na faɗa ina mai shararo masa ƙarya.
“Allah taimaka,ya kika baro mutanen can ɗin?”
“Lafiyarsu lau Abba ,Alhaji ya ce ma a gaishe ka”
Nan mu ka soma yin hira bisanin na fita na yi alwalar sallar magrib,a bakin murhu na bar Inna ta na ta ƙoƙarin dafa Ganda.
Bayan na gama sallah na rakuɓe na lula duniyar tunanin in na yi kuɗi yadda zan yi rayuwata,ina nan zaune aka kira isha'i na tashi ita ma na sauketa bisanin na fita tsakar gida.
Abincin mu ka ci,Inna sai labarin ƙawayena uwanda suka yi aure bayan tafiyata.
Washegari
Tun safe na yi wanka na shirya,don sam ban yi wani baccin kirki ba.Sallama na yi masu kafin na je tasha na hau mota,tun a hanya na sanar da Hajiya .
Cikin ikon Allah mu ka sauka lafiya,ina ƙoƙarin kiranta na ji muryarta “ga ni nan”
Na washe baki tare da isa wurinta na gaisheta,ta amsa tare da buɗe bayan wata farar mota ta ce “shiga” na kuwa shige sannan ita ma ta shiga.
“Ya hanya?”ta tambaye ni.
“Lafiya lau alhamdullah ! Ashe har kin zo ki na jirana ” na faɗa ina ɗan dubanta.
Ta murmusa ta ce “eh saboda ina son mu wuce kanti ki yi sayayya”
Na ɗan sunne kai ina godiya yayin da ita kuma ta na min wani kallo da na rasa na mene ne don har sai da na ɗan tsargu.
Ina cikin saƙar zuci har mu ka isa mall ɗin,mu biyu kawai mu ka shiga yayin da direba ya tsaya cikin mota.
Tamkar wacce yau ne ta fara shiga birni haka na yi ta ƙauyanci,tun ina mamakin yadda Hajiya ke zaɓa min kaya har na bari na bar wa kaina kan cewa saboda ita ɗin mai taimakon jama'a ce kuma mai kuɗi.
Tun daga kayan sawa,takalmi,hijabai da kuma turare babu abin da ba ta saya min ba.Har mota aka kawo mana kayan kafin mu wuce gidanta,nan na tarar da ƴan matan da ta yi min hirarsu a jiya.
Cikin sakin fuska duk suka tarbe ni,bisanin Hajiya ta ce “ga ƴar uwar nan na samo maku abokiyar aiki,ku taimaka mata ta tsefe kitsonta sai ku kaita salon”
Ƴan mata biyu ne suka miƙe su na cewa “to Momah yanzu nan kuwa”
A kunyace na zauna aka tsefe min kitso,ɗaya daga ciki kuma ta haɗa wasu abubuwa ta shafe min jiki da shi an ɗauki minti talatin sannan na shiga na yi wanka da ruwan ɗumi nan fa na ga fatata ta yi wani uban kyau.
Cikin kayan da Hajiya Momah ta saya min na zaɓi ɗaya na saka.
Su biyun nan dai suka min rakiya zuwa salon,yau ne karon farko da aka sa min apple hakan ya sa na yi ta ƙauyancin yadda gashina yayi taushi da tsayi.
Musamman da aka fito da ni daga madafar gashin sai ya ƙara yin tsayi aka shafa min mayuka da kuma saka min ribob.
Gida mu ka dawo,Hajiya Momah da ta ga yadda na sauya ta ce “an gaishe da Munayya da Rumy ”
“Da girman kujerar ki Hajiya Momah” suka furta su na murmushi.
Abinci mai rai da lafiya aka zuba mu ka ci,har sauri nake domin na gama na koma can Takalmawa na nunawa Raheela yadda na koma sai na ji Momah na cewa “in kun gama cin abinci ku kaita ɗakin hutu ta kwanta,na san duk ta gaji irin wannan zirganiya”
Ban ce komai ba duk da ina son komawa gidan,amma haka na bi bayansu na kwanta ba kuwa jima ba bacci ya ɗauke ni.
Ina farkawa da Hajiya Momah na fara cin karo hannunta riƙe da wani ɗan ƙaramin kasko sai hayaƙi ke tashi sama yayin da ƙamshi haɗi da wani ƙauri suka garwaye ɗakin.
“Meelat kin tashi? Ki na jin yunwa ko?” ta tambaye ni.
Jin ta canza min suna ya saka na ɗan murmusa don na fahimci Hajiya ta na son bariki sannan kuma wayayyar mace ce.
Ta ci gaba da cewa “Munayya kawo mata madararta ta sha sai ta je ta yi wanka”
Munayya wacce ke gefena ta na game ta miƙe ta buɗe frigine ta ɗauko wata tasa,miƙo min ta yi na karɓa.Madara ce mai sanyi sai ƙamshi ke tashi,abun ka da baƙauya haka na kafa kai na shanyeta tasss.
Momah sai wani murmushi take ,ni kuwa toilet na shiga na fara wanka.
Tamkar wacce ake yi wa sauyin massarafar gangar jiki haka na soma jin duk wata gaɓa ta jikina na saki,yayin da kuma nake jin wani yanayi da ban taɓa tsintar kaina a ciki ba.
Ban shirya ba na ɗauki towel na ɗaura,idona har wani lumshewa suke ina ganin dishi-dishi.
Turus na yi ganin Hajiya da Munayya duk ba sa nan sai mutumen da na ɗauka matsayin Uba na biyu wato Alhaji Nera.Da wani mugun sauri na yi baya na jingina da ƙofa,a ɗan sauran ganin da ya rage min nake hango Alhaji Nera na tafowa gare ni.......
[31/08 à 15:22] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️
MRS SADAUKI 💫✍️
FCWA ☀️
Special gift fo my VIA FANS 🪷
❌Duk wacce ta san ba ta karantawa kar ta shigar min groupe
#Mafarin ƙaddarata
Page 4
Lokacin da Alhaji Nera ya iso gare ni bai yi wani ƙasa da gwiwa ba wurin jawo ni jikinsa. Ba bacci nake ba amma madubin idona ya dishashe ta yadda ban gani tarau.
“Jameela dama na san ke zazzafa ce! Yadda kike da shaf mai kyau ya tabbatar min cikin mata ke ajin farko ce ,dubi yadda fatarki ke sheƙi” ya na yin furicinsa ne haɗi da ƙoƙarin raba jikina da farin towel ɗin da ke ɗaure a ƙuguna.
Jikina babu wata attakar da zan hana shi,hakan ya sa ya ci nasarar zare masurturcin jikina haɗi da ɗaukata kamar ƴar tsanar roba ya ajiye kan latifa.
Gangar jikina yake sarrafawa wacce ban san dalilin da yasa nake jin saƙonsa na shigata ba,sai dai ba zan iya mayar masa da martani ba saboda jikina duk a mace yake.
Lokacin da Alhaji Nera ya ci nasarar raba ni da abu mafi daraja a wurin ko wace mace,sai na ji wasu hawaye masu gumi su na zubo min.Duk uwar azabar da nake ji bai sa na iya yin wani kataɓus ba,don kuka ma iya hawaye ne kawai suke iya fita.
Na ɗan ware idona kaɗan da har yanzu ba su ida dawo normal ba.Alhaji Nera ke tsaye ya na mayar da kayan jikinsa,a gaban idona ya fice sai kuma Hajiya Momah ta shigo.Wannan karon ita da Rumy ne fuskarsu ɗauke da murmushi sai kace abun arziki ne aka aikata gare ni.
Momah ta zauna ta na mai ɗago kaina yayin da ita kuma Rumy ta buɗe min baki ta fara zuba min wani shayi mai ɗan ɗumi,ɗanɗanason sam babu daɗi amma haka nake sha kamar wacce aka yi wa dole har na shanye.
Na lumshe ido,sannu a hankali gangar jikina ta fara dawowa normal.Sai a lokacin na fashe da matsanancin kuka,Momah ta shafa kaina ta na cewa “yi shiru mana,ai komai ya wuce yanzu burin ki zai cika za ki hau mota ,kayan jiki kuwa sai dai ki baiwa wasu”
Jin ta ambaci mota ya saka na ji nauyin zuciyata ya ɗan ragu,dakyar na yunƙura na tashi zaune ina mai kiciniyar suturta jikina da dara.
“Momah ki taimaka ki gasa mata jikinta mana,don wannan ban ce za ta yarda da na yi mata wankan ba” cewar Rumy ta na wani kwaɓe baki.
Dakyar na iya taka ƙafata zuwa toilet,sosai Momah ta min gashi mai kyau wanda ya sha magunguna.Sai kuma ta bar ni cikin wasu ruwan ɗumin,ina nan zaune na fara tunanin abin da ya faru da ni da tsakar rana.
‘Alhaji Nera !’ shi ne sunan da na aiyyana a rai,ina tunanin ranar farko da na sauka gidansa irin kallon da yake min kamar na son tantance wani abu.
Na lumshe ido can ƙasan zuciya na furta ‘mugu! Wato tuggu ya shirya min ya kawo ni tashar mota ya haɗa ni da muguwar can?’
Ɗaya ɓangaren zuciyata ne ya ban amsa da ‘to ai sau ɗaya ne tak! Kuma muradin zuciyarki ya cika yanzu za ki hau mota!’
Ban san lokacin da murmushi ya suɓuce min ba,ina hango yadda zan dinga parker motata a cikin jami'a ina kuma saka tsadadun kaya tare da shiga wurin manyan mutane.
“Wai har yanzu ba ki gama wankan ba? Likita na waje ya na jiran ki zai duba ki” Rumy ce ta turo ƙofa ta na kallona.
Da sauri na jawo towel sannan na miƙe,babu laifi yanzu ina ɗan takawa da ƙarfi.
Ina fitowa dadaɗan ƙamshin turare ya bugi hancina,yayin da kuma tuni an canza darar da ke shimfiɗe wacce da idona na ga duk ta ɓace.
Momah ta ce “kwanta likita ya duba ki kar aje kin ƙaru ”
Mutumen da ke sanye da wata farar riga irin ta likitoci na duba,fari ne sol mai farin saje shekarunsa za su kai arba'in da biyar.
Kamar zan yi kuka na kalli Momah na ce “hajiya namiji zai duba ni ? Da dai a bari gaski....” kallon ta jefo min ya saka ni haɗiye sauran maganar.
Kan katifar na kwanta ya duba ni,wanda da ace na san abin da zai faru da tabbas zan koma a toilet na rufe kaina.
Momah ta fice ta rufe ƙofa daga can baya yayin da shi kuma likitan na ga ya na ƙoƙarin cire kayan jikinsa.
Zuciyata ta buga da bala'in ƙarfi,ina mai tashi zaune na ce “mene ? Me za ka yi min?”
Wata dariyar shaƙiyanci yayi bisanin ya ce “mi kika gama yi yanzu kafin na zo na duba ki?”
Ban basa amsa ba sai wasu yawu da na haɗiye muƙut na tsoro,ina ji ina gani likita ya far mini.Wannan karon kuwa kuka har da kururuwa haka na yi shi amma kusan a banza.
Bayan ya gama cutar da ni ya yi min allura,“Allah ya isa!” na furta ina hararensa da idona da suka kumbura suka yi ja tsabar wuya.
Uffan bai ce min ya fice,kamar abun arziki sai ga Momah ta na cewa “Meelat a haka za ki cim ma nasararki ki na zagin costomer?”
“Costomer dai?” na furta a fili ina jin zuciyata na min ɗaci.
“Eh ! Ko har yanzu ba ki fahimci hanyar kasuwancin naki ba?”
Rararas ! Zuciyata ta tsinke.
“Karuwanci?” na jefo mata tambayar ba tare da na shirya ba.
“Madallah! Kwanyar ki na kawo wuta.Ga kuɗin ki na wurin likita,shi kuma ɗayan ya ce gidanku ɗaya za ku gyara kan ku” ta yi furicin ta na mai aje min kuɗi kusan kaina ta yi tafiyarta.
Na jawo pilow na rungume gam tare da fashewa da matsanancin kuka.Sai da na yi mai isata bisanin na je na yi wanka,na gasa jikina da ke min mugun ciwo.
Ledar kayana na jawo na zaɓi wata doguwar rigar abaya baƙa na saka.Na zauna tare da jawo kuɗin ,dubu ɗari ne cicif.
Aka turo ƙofa,mai aikin gidan ce wannan karon hannunta riƙe da abinci ta ajiye a gabana ta fice.
Yunwa nake ji hakan ya sa na fara cin shinkar wacce aka ɗora ƙatuwar kaza daga sama.Sai da na ci na ƙoshi sannan na je na ɗauko ruwa masu sanyi na sha,tunanin makomata na fara don ko giyar wake na sha ban turki zuwa Takalmawa ba dole Inna za ta fahimci abin da ya faru da ni.
Ina nan cikin halin ƙaƙanikayi,wayata da tuni na mance ina da ita ta fara tsuwa.Sabuwar lamba ce,na ɗaga ina mai kaiwa kunnena ba tare da na ce komai ba.
“Baby gani a ƙofar gida na zo ɗaukar ki,yanzu mu ka gama waya da Abban ki” shi ne abin da ya ce.Sarai na gane muryar,Alhaji Nera ne.Ban ce komai ba na kashe kiran,rigar ɗazu wacce na cire na ɗauki abata na saka a leda haka ma kuɗin bisanin na fito.
Har ƙofar gida Momah ta yi min rakiya sai daɗin baki take min da ƙara hura wutar muradina,ta yi min alƙawarin samo min costomer a duk lokacin da na buƙaci haka.
A gaba na zauna don shi ne ya buɗe min ƙofa,sai da ya hau titi da kyau sannan ya jawo hannuna ya ce “ya jikin naki?”
Cike da shaƙiyancin da ban san yaushe na koye shi ba na ce “wane jiki? Ce maka aka yi banda lafiya?”
Dariya yayi irin tasu ta ƴan duniya ya ce “baby duk fushin ne? To ki yi haƙuri da sannu zan cika miki muraden ki” ya jawo aljihun mota ya ciro min waya ƙirar Samsung ya ci