Showing 9001 words to 12000 words out of 21708 words
Chapter 4 - CELEBRITY FARASHIN TASIRI Book Complete by Mrs Sadauki .txt
kika rasa?”
“Yanzu dai sai an jima zan wuce gida” na faɗa tare da tashi tsaye.
“Ko kayan ba za a nuna min ba?”
“Mene ne na sauri kai da za ka gansu sanye a jikina?” na faɗa cike da kissa.
“Eh kuma haka ne fa,ni ɗin ne na cika sauri kamar sabon ango” ya faɗa ya na yaƙe haƙora.
Ɓangaren Hajiya su na shiga ta dubi Na'ilah ta ce “ban son sakarci mi zan yi da dubu biyu? Sanin zai baki kuɗi da yawa ya saka na haɗa ki da shi amma shi Alhaji Nera ya fi son sabuwa dal a leda tausayin ki yasa na rakuɓa ki wurinsa”
Na'ilah ta ce “duka fa 10k ne ya ban”
“Wlh ƙarya kike! Alhaji Nera ƙaramin biyansa talatin ne abin da ya haura sama,sannan kayan matan da na ɗirka miki fa kin zata kyauta ne?”
“Hajiya ɗan tsumin ma sai na biya?”
Hajiya ta kece da dariya ta ce “tun da nake da ke na taɓa baki maganin mata? Ina ce dai ke kike saya da kuɗin ki, wannan ma da na baki cikin na Meelat ne jiya Alhaji ya bada kuɗi na gangamo mata su ”
“Ai kam su na da kyau sosai ni kaina abun ya min daɗi ba kamar kullum ba”
“Hhh! Kayan Sokoto kenan,ita kanta Meelat ɗin ba ta fara aiki da su ba yau na aiki direba ya ɗauko min su tashar mota”
Na'ilah ta ce “don Allah Hajiya ki ɗan ƙulla min a leda yau ma ina son fita,ga 5k ki haɗa da 2k ɗin farko”
Hajiya Momah ta karɓe kuɗin ta ce “sai dai na baki lambar Hajiya Fatimah mai gyaran aure can ki saya,kayanta ba su da tsada ga kuma biyan buƙata(duk mai son ingantattun kayan mata masu kyau irin ƴan Sokoto sai ya tuntuɓe ta ga lambar nan +234 816 788 8934)”
Na'ilah ta yi godiya suka rakayo falo.
“Meelat ina kuma za ki je ?”
Har na kai bakin ƙofa na ji muryar Hajiya Momah ,na bata amsa da “gida zan je mana”
“Hajiya ita ce Meelat ɗin?” budurwar nan na ji ta tambaya.
“Eh ita ce! Meelat ga Na'ilah nan ko za ku yi ƙawance ne?” Hajiya ta faɗa ta na wata ƴar dariya wacce ta saka na yi zargin ko gulmata suka yi.
“Bani lambar wayar ki” cewar Na'ilah.
“Banda da ita” na bata amsa don ban ga dalilin da zai sa na ƙula ƙawance da ita ba.
Fita ta yi yayin da Hajiya kuma ta ɗauko min wasu garin magani kala biyu ta bani wai na rinƙa sha in ina gida.Duk da ban fahimceta ba haka na karɓe na saka a jaka,kafin na fice na bar Alhaji Nera nan.
Ina isa gida Hajiya Turai ta tarbe ni da fara'a,ledar kayan na zube ta shiga dubawa sai ta ce “uwannan ai sai dai na aje miki su har auren ki ya tashi” ta kwashe kayan baccin ta bar min pant da bra da turare” mi zan ce baya ga dariyar yaƙe,ina ji ina gani Hajiya ta kwashe kayan ta kai su can ɗakinta.
Nawa ɗakin na wuce,na haye katifa tare da kunna data.Hotunan Sadiq na fara cin karo da su,babu laifi duk sun yi kyau.Na yaba bisanin ni ma na tura masa nawa,aka yi katari shi ma ya na online .
“Jamee wai don Allah ina son na tambaye ki ina kika samu Android ?”
“Saya na yi” na basa amsa .
“Ina kika samu kuɗin? Ko kin sayar da Akuyar taki?” ya tambaya cikin zolaya don na taɓa faɗa masa ina kiyon Akuya.
Na yi ƴar dariya ina mai ce masa “ka ji ka da wani zance,babbar waya ce fa ta kai 80k” ya wani waro ido ya ce “sabuwa ce ma kenan?”
Kwalin wayar na ɗauka hoto na tura masa,maimakon ya yaba sai ma kirana yayi.
Na ɗaga sai dai yadda ya jero min tambayoyi ya saka na yi zuciya na kashe kiran,ya na ta maido wani amma na ƙi ɗaga wa sai kuma ya koma turo min saƙo.
Da na ga zai dame ni sai ma na fice zuwa falo na shiga kallo nan na ɓata lokacina,sallah ma a nan nake yi har aka kira magrib.
Ɗaki na koma na yi wanka sannan na yi sallah,ina nan kan sallaya na ji muryar Alhaji Nera.Ban san mi yasa ba haka kawai na ji ina ra'ayin yin kwalliya sai dai banda kayan.Wayata na ɗauka na yi masa text na sannu da dawowa,an ɗauki lokaci kafin ya maido min da yawwa my Baby.
Sai da aka yi isha'i sannan na fita falo,kamar kullum a zaune na tarar da su suna cin abinci a plate guda.
Hajiya ta ce “ga abincin ki can a kan table”
A ladabce na amsa bisanin na je na zauna,ina cin abinci sai ga saƙon Raheela ya shigo min ta WhatsApp.
Labarin da ta bani ya saka abincin fice min a rai,ita kuwa cike da murna take ta aiko min ɗan ƙaramin akwatin da aka kawo wai na baikon ta da Hafiz .
Ko ganin ban ce komai ba ne ya saka ta kira ni oho! Ɗaga dai kiran na yi.
“Jameela wlh kamar da wasa iyayen Hafiz sun zo an kawo kuɗin tambayar aure,nan da wata uku za a kawo lefe”
“Raheela wai ki na nufin aure za ki yi ki bar ni ? To karatun fa?” na tambayeta muryata na ɗan rawa.
“Zan ida can gidansa,ashe iyayen Hafiz kuɗi ne da su kin ga motar da suka zo da ita? Hafiz ɗin ma ya min da zarar an koma makaranta da ita zai dinga zuwa sannan zai koya min”
“Ni ma zan koyi motar in sha Allah ” na faɗa cike da jin haushi.
Ta yi dariya ta ce “ba dai da motarmu ba”
“Au! Har ta zama taku? To yayi masu mota” na faɗa ina mai yanke kiran kai kace ni na kirata.
Cike da baƙin ciki na koma ɗaki,ina nan kwance har dare yayi sosai.Kiran Alhaji Nera ya shigo,shaf na manta ban kashe data ba.Video call ne ya turo,dakyar na ɗaga ina ɗan ware idona da nake jin su na yi min ƙaiƙayi.
“Baby ya haka har yanzu ba ki shirya cikin kayan baccin ba?” Alhaji ya faɗa .
“Su na wurin Hajiya ta karɓe,wai za ta aje min sai na yi aure” na basa amsa.Cikin masifa ya ce “iskancin banza! Uban waye ya ce mata ki na buƙatar ta ajiye miki?” sai kuma ya kashe kiran.
Hotunan Sadiq na shiga duba wa,ina ayyana wa a raina ina ma ace shi ne ke da kuɗin Alhaji Nera? Da na ji daɗi.Ina cikin wannan zullumin bacci ya ɗauke ni.
Alhaji Nera kuwa sosai ya ji takaicin abin da Hajiya Turai ta yi masa.Hakan ya saka ya fita zuwa ɗakinta,a kwance ya tarar da ita kan bed ta na latsa waya.
Kayan baccin da ta saka ya bi da kallo sosai suka karɓeta ,amma kasancewar ba ta da lafiya bai kai tunaninsa ba nesa.
“Alhajina!” ta furta ta na mai tashi zaune.
“Hajiyata mai abun ikon Allah!” ya faɗa ya na mai ɗan sakin murmushi.
“Ah Alhaji ya haka kuma kake abu kamar wani yaro?” ta faɗa ta na janye hannunsa da ya ɗora a ƙirjinta.
“Kusan shekara uku kenan ba mu haɗa shimfiɗa ba,kin ce min ba ki lafiya amma har yanzu ban taɓa gani kin nemi magani ba” Alhajin ya faɗa ya na mata kallon ƙasa-ƙasa.
‘Ina zan yarda da kai ,garin neman matanka ka kwaso cuta ka ƙaƙaba min’ Hajiya ta faɗa a zuci,a zahiri kuma cewa ta yi “wlh Alhaji ko ruwan zan kama ba na iya saka hannu na wanke wurin saboda yadda ƙuraje suka addabe ni,har sabulun infection fa na saye ka ga shi can a ajiye”
“To Allah kyau! Ni bari na koma daga ciki,ina son yin kallo” ya faɗa ya na baza ido nan kuwa yayi arba da ledar kayan Meelat.
“Ki zo ki rufe ƙofa” da “to” ta amsa masa shi kuma ya fice.
Ɗakin Meelat ya wuce kai tsaye,dama ba wani key take sawa ƙofar ba.Ya tura ya shigo,can ya hangeta ta na bacci.Sai da ya ƙare mata kallo da kyau sannan ya ƙarasa ya zare wayar da ke hannunta.
Firgigit na tashi jin ana taɓa ni,ina buɗe ido na yi tozali da Alhaji Nera.
“Lafiya mi kuma ka zo yi ɗakina?” na tambaye shi ina mai jingina ga bango.
“Baby ina buƙatar ki ne,a nan za mu yi ko mu je ɗakina ?”
Na waro ido na ce “alhaji cikin gidan ka fa mu ke! Gaskiya ba zan iya ba ”
“Za ki iya kuwa! Gobe fa nake son kai ki wurin koyon mota shi ne ba za ki faranta min rai ba?” Alhaji Nera ya faɗa ya na shafar kumatuna.
Na washe baki na ce “da gaske Alhaji? Kar fa ace wasa kake min”
Bai bani amsa ba sai romance ɗina da ya fara,bisanin ya zarce zuwa mai kankat.
Ya na gamawa ya ficewar shi,ni kuma na shiga toilet na tsarkake jikina.
Washegari kuwa Alhaji Nera ya biya min kuɗin koyon mota,ƙaryar zan je karatu can makarantarmu na yi wa Hajiya .A haka har na ida kwanaki takwas ɗin da muke hutu a koyon mota,babu laifi na ɗan iya amma ba sosai ba.
Yau ta kama Monday,ranar da za mu koma makaranta.Cikin abaya blue na shirya tsaf na maida gashin kaina a tsakiya na ɗaure sannan na jawo wani a gefen goshina.
Ƙarfe shidda cicif na fito,motar nan wacce aka biyan 100 ta ƴan makaranta na je na yi tsaye ina jira har ta zo na shiga.
Ina zuwa makaranta direct aji na nufa,saɓanin da can baya da nake zuwa wurin Raheela.Tun ranar da ta sanar da ni zancen aurenta ba mu yi wata hirar da ita ba.
Ina nan zaune sai ga ta kuwa ta shigo,yadda ta yi wani turus shaye da mamakin ganin canjin da na samu ya sa sakar mata murmushi nace “amarsu ta ango!”
“Wai ke ce? Kin ga yadda kika yi kyau?”
Shigowar Hafiz da Sadiq yasa hirarmu ta gimtse.Su ma da ɗan mamaki suke kallona kamar sauran ƴan ajin,Hafiz ne ya gayyace mu zuwa waje inda ya parker mota.....
Only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,DM +22795045822
[02/09 à 09:34] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️
MRS SADAUKI 💫✍️
FCWA ☀️
Special gift fo my VIA FANS 🪷
My book is only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822. Ko kuma katin MTN,ƴan Nijar kuma carte airtel ta 300f
Page 7
Ni da Raheela mu ka zauna a baya,yayin da Hafiz ke tuƙi Sadiq na gefensa.
A ranar na ga ikon Allah yadda Raheela ke nuna min ƙiri-ƙiri motar saurayinta ce,sai wani shagwaɓe masa take ta na ƙirƙiro wasu sabbin abubuwa da ban santa da su ba.Amma na ajiye wannan a ma'adanar sirrina akan ƙila don an yi masu baiko ne.
Sadiq kuwa sai satar kallona yake ta madubi,ni kuma na share na yi kamar ban ganinsa.
Wayata na ciro na fara dube-dube ,ni ce WhatsApp ni ce cikin Gallerie.Raheela ta ce “wayar na da kyau sosai nawa kika saye ta?”
“Saya min aka yi fa” na bata amsa.
“Wa fa?”
“Alhajinmu” da yake haka nake kiran Alhaji Nera tun can asali.
“Ko son ki yake? Amma ai na ga bai haihuwa”
“Haihuwa ai ta Allah ce!” na faɗa ina mai ɗagowa na maido hankalina gare ta.
“Haka ne kam! Amma ke ki na son shi?” Raheela ta sake jefo min tambayar.
“Ina dai son kuɗin shi amma mi zan yi da tsoho?”
Daidai nan Hafiz yayi parking a Bouzou City ,duk mu ka fito.
Ciki mu ka shiga Hafiz ya saya wa kowa biscuits da cake duka kuɗin dai ba za su wuce 10k ba amma Raheela sai wani ɗagawa take.Na ji haushi sosai wannan ya saka na ƙudirci aniyar sai na shayar da ita mamaki tun yau ba sai gobe ba.
Mu na tsaka da tafiya na cewa Hafiz “don Allah ka biya da ni wurin Madugu mai Kaji yunwa nake ji zan karɓa ”
Da farko shiru yayi bai ce komai ba sai kuma ya juyo ya na kallona,idonsa ya sauka kan jakar kuɗina da zuge shagu ƴaƴan banki jere ras.
Dama ba wani nisa ke da kwai ba,haka Hafiz ya canza akalar mota ya na mai cewa “Jameela hutun nan da aka je ya mayar da ke ƴar gayu sosai,bayan canjin launin fata da kika samu wato har sabuwa bariki kika tsiro ta cin Kaji?” cikin raha yayi maganar hakan yasa ban jin zafi ba.
“A'a gyara sunan Meelat! Yaushe rabon wata Jameela! Wlh kuwa ka san an ce dare ɗaya Allah ya kan yi Bature ! Ni da kaza wani irin ƙawance mu ka ƙulla” na yi maganar ina dariya tare da satar kallon Raheela ta gefen ido .Yanayin fuskarta duk ya canza ,baƙin ciki ya hana ta cewa komai har mu ka isa.
“In babu damuwa za mu iya fita mu ci abincin sai mu dawo,na ɗauki nauyi” na faɗa,a cikinsu Sadiq ne kawai bai ga kuɗin Meelat ba lokacin da ta ce ta na son kaza sai da ya ji kamar zuciyarsa ta kama da wuta don takaici.Tun da dai ya san shi bai da ko ƙwandala ta saya mata ,dole dai Hafiz zai biya.
Yanzu kuma da ya ji banzar furincinta ya saka shi saurin juyowa.
Ido huɗu mu ka yi da Sadiq da yake min wani kallo da ban fahimci mi yake nufi ba,fita na yi daga motar don tuni Raheela ta fita ita da Hafiz .
Sadiq shi ma ya fito,mu na shiga ciki masu kula da wurin suka fara gaishe ni saboda a yawon da nake na koyon mota mu na haɗewa da Alhaji Nera a nan.
“Babyn Alhaji ina kwana! Mi za a kawo maku?”
Cike da kuri da yanga na faɗa masa ya haɗa mana couscous da kaza plate huɗu da kuma ruwa masu sanyi na cikin bidon.
Wuri mu ka samu mu ka zauna,ko wanensu yayi shiru kamar ruwa sun ci shi har abincinmu ya iso.
Ni da Hafiz kawai ke cin abincin nan cikin jin daɗi da walwala,saɓanin Raheela da Sadiq da ko wane nake zargin abin da ya hana shi sakin jiki.Ita dai baƙin ciki ne da kuma ba ta yi zaton haka ba,shi kuwa Sadiq ina tunanin kishi ne da kuma tambayar ina na samu kuɗi.
Bayan mun gama na zaro kuɗi na biya kusan 30k don ƙarfin hali da za a ban canjin da yayi saura ce masa na yi ya riƙe.
Hankali kwance na shiga mota na zauna sai ma lumshe ido da nake zuciyata fari tasss.Wannan karon babu mai magana a motar har mu ka isa makaranta.
Ina shirin shiga aji Sadiq ya fizgo ni na yo baya,kamar wata ɗiyarsa haka ya ja hannuna zuwa gefe.“Jameela mene ne haka? Irin wannan uban kuɗin da kika kashe ai sai ki sa a fara zargin ki. Ina kika same su? Ko aiken ki aka yi ?”
Na fizge hannuna na ce “mene haka Sadiq ? ”
“Yi haƙuri raina ne a ɓace ban yi hakan da niyyar kaina ba”
“Daga yau kar ka sake riƙe min hannu,dubi yadda ake kallonmu” na faɗa ina mai barinsa nan a tsaye na shige aji.
Kusa da Raheela na zauna wacce ta game ban da can.Ni ma na shareta ina mai duba saƙon Alhaji da ya shigo min,na saki murmushi tare da kiransa.Buga guda ya ɗaga, “da gaske Alhaji har ka buɗe min account?” na tambaye shi saboda tun jiya na yi masa ƙorafin riƙe kuɗi a hannuna Hajiya za ta iya shiga ɗakina ta yi bincike.
“Eh tun tuni,yanzu haka na saka miki kuɗi ma a ciki”
“Ok to babu damuwa yau in na fita koyon mota sai na biya Bank na ajiye na ga hannuna”
“Ok babu damuwa amma kafin nan ina son mu je hotel mu ɗan huta”
“Ok babu damuwa,yanzu dai ina cikin aji na ga ɗalibai sun fara shigowa ƙila malamin da zai mana darasi ya tawo” na faɗa tare da yi masa sallama farin ciki fal raina.
Ina ajiye waya kuwa malam ya shigo,darasinsa ya fara kamar kullum yau ma ina ta bada amsoshin tambayoyi.Canjin da na samu hatta malumaina sun fahimci haka don wasu su na nuna mamaki a fuska wasunsu kuma har tambayata suke.
Bayan mun gama ko wane darasi na fito ina daddana waya,muryar Raheela na ji a bayana “yanzu sai gida?” na juyo na dubeta,sarai na san abin da take son sani saboda lokacin da na ajiye waya malam ya shigo babu damar ta tambaye ni shine yanzu ta biyo ni.
Na ɗan rausayar da kai cikin kurin magana da salon da Hajiya Momah ke koyar da ni nace “zan je restaurant na ci abinci sai na wuce inda ake koya min mota”
“Allah taimaka” ta faɗa tare da yin gaba.Sosai na ci dariya yadda Raheela ta nuna min ta ji haushi babu ko ɓoye wa.
SADIQ
Sam ruhinsa ya ƙi samun salama,hankalinsa duk ya tashi.Ya na son Jameela sosai ta yadda ya kasa ɓoyewa mahaifiyarsa ita.Su na tafe cikin motar Hafiz amma sai jan tsuki yake shi ɗaya.
“Abokina haƙuri za ka yi tun da dai ba ka kai kuɗin aurenta ba,sannan yadda ta waye ɗin nan Allah sai ta ƙara kyau ai farin ciki ya kamata ka yi” Hafiz ya faɗa ya na riƙe da sitiyarin mota.
“Murna? Ni wlh na fi son ta yi zamanta a ƴar ƙauye zai fin min nutsuwa.Ka na dai ganin uban kuɗin da ta kashe mana ko a kwalar rigarta,kuma inda ka ga wayar hannunta Galaxy ce ”
“Hhh! Kishi dai kake! Amma fa alamu sun nuna kamar soyayya take da wani Alhaji ,tun da na ji ma'aikacin gidan abincin nan ya na kiranta da Babyn Alhaji”
“Hafiz kar ka sa zuciyata ta buga don Allah,ya isa haka ta je ta yi ta soyayya da shi ɗin.In ya na da kuɗi ni kuma ina da Allah zan ta kai kukana wurinsa har ya bani ita”
“Wai har haka kake son Meelat?”
“Fiye da yadda kake tunani,wlh yanzu haka ji nake kamar zan kama da wuta”
“Ka zage dantse wurin ganin ka samu soyayyarta fiye da shi wancan ɗin” Hafiz ya faɗa daidai nan ya kawo ƙofar gidansu Sadiq da yake nan unguwar Maraɗawa.
“Na gode abokina sai an jima” Sadiq ya faɗa tare da fita.
Ya na shiga cikin gida ko sallama babu ya shige cikin ɗakinsa.
Da sauri Mama ta biyo bayansa ta na tambayarsa lafiya amma ya ƙi faɗa sai ce mata yayi “ba komai Mama ”
“Ƙarya kake yanayin ka ya canza! Ba haka