Showing 12001 words to 15000 words out of 21708 words
Chapter 5 - CELEBRITY FARASHIN TASIRI Book Complete by Mrs Sadauki .txt
ka saba shigowa gida ba.Dole da wani abu,ka faɗa min ka ji”
Duk yadda ya so ya ɓoye wa Mama kasawa yayi saboda a soyayyar Jameela shi ɗin mai rauni ne kawai sai ya fashe da kuka ya ce “Mama Jamee ce...” sai kuma ya kasa ida maganar.
“Cewa ta yi ba ta son ka ko? Irin wannan nacin da kake yi mata ai dole ta faɗa.Yo ayi mutum babu jan aji kullum cikin amayar da abin da ke cikinka kake”
“Mama ba fa haka ba ne,soyayya take da wani”
Mama ta shiga taɓa hannuwa ta ce “shine kuma kake kuka maimakon ka yi tunanin hanyar da za ka raba ta da shi? To Allah kyauta!” ta na gama faɗa ta fice.
Sadiq yayi zaune kan yamutsatsar katifar shi ya rabka uban tagumi ya na tunanin mafita.
MEELAT
Taxi na ɗauka na tafi can auto-école,cike da girmamawa aka tarbe ni bisanin mu shiga motar da ake koya min da ita.Sai da mu ka hau titi sannan ya bani,ban sani ba ko don ina son mota ne sosai ya saka na yi saurin iyawa oho.
“Masha Allah ki na kula da komai yadda ya kamata, Allah dai ya nuna mana ranar da za a baki lasisin ki” cewar wanda yake koyar da ni.
“Amen na gode sosai”
Sai da mu ka yi yawo sosai sannan na wuce hotel ɗin da Alhaji Nera ke zaman jirana.
Tuni an tanadar min abinci,ya na ƙoƙarin taɓa ni na dakatar da shi saboda ina buƙatar yin wanka.
“Ki fara da abincin Baby sai ki yi wankan” cewar Alhaji Nera.
Na buɗe abincin,ƙamshi ya bugi hancina idona sun rufe da zalama sam ban lura da garin maganin da aka barbaɗe abincin ba.Ina gamawa na shiga na yi wanka,ko da na fito tuni Alhaji Nera ya shirya,ya na kwance kan bed babu kaya.
Na ɗan harare shi nace “wai don Allah wannan tumbin naka ba ka iya sha masa magani ya baje?”
“Don Allah Baby ki bar maganar tumbin nan,ki zo ki kula da ni” yayi maganar ya na jawo ni.
Bayan mun sheƙe ayarmu na kwanta luf ina lumshe ido,yau kwana goma sha ɗaya cicif da na shiga sabuwar rayuwar da nake jin daɗinta zuwa yanzu.
Na yi fari na yi kyau,shap ɗina ya ƙara buɗe wa ya fito da kyau.
Dogon hancina Alhaji Nera ya ja ya ce “my Meelat ƴar fullo”
Na yi murmushi kawai,“ya Sadiq ɗin ko shine ake tunani?”
Na ɗan yamutsa fuska nace “don Allah daga yau ban so ka na min zancen shi”
“Ok babu damuwa gimbiya,in kin tashi tafiya ga kayan baccinki nan na sayo”
Da ƴar murna ta na tashi ina cewa “Ah! Ah! Yau Allah yayi nufi kenan?”
Ya washe baki ya na miƙo min ledar na fara dubawa,“sun yi kyau amma dai wanda Hajiya Turai ta ɓoye sun fi kyau sosai”
“Zan bincikosu su ma,don Allah yau ki saka wannan ina son ki kwana a ƙirjina” ya faɗa ya na nuna min wasu farare.
“A'a in fa Hajiya ta shigo ɗakina ta gan ka? Na faɗa ma haka kawai cikin dare sai na ga ta faɗo min”
“A ɗakina za ki kwana,in za ki zo sai yi kuna pampon toilet ki yi wa ƙofar key kin ga ko ta shigo za ta yi zaton ki na ciki ne”
Na dube shi da kyau na ce “wai Alhaji ina kake samo irin wannan dabarun?”
Dariyarsu yayi irin tasu ƴan duniya ya ce “ke dai tashi ki yi wanka na kai ki gida”
Haka kuwa aka yi,bayan duk mun yi wanka mu ka kimtsa sannan mu ka fito Alhaji ya kai ni bank na ajiye kuɗina,sai kuma ya sauke ni a ƙofar gida.
Kiciɓis mu ka yi ni da ƙawar Hajiya Turai,ban kawo komai a rai ba na gaisheta kafin na wuce.
Mabaruka ta na fitowa ta ga Alhaji Nera a zaune,ga kuma Meelat ta shiga gida nan zargin kar dai ace tare suke ya sakata yi wa Hajiya Turai voice lokacin da ta isa gida.
Ina shiga na gaishe da Hajiya ta ce ga abincina nan nace mata a ƙoshe nake bisanin na shige ɗaki na yi ta baccin wahala.Wuraren sallar la'asar na farka,Hajiya Turai na gani ta na ta bincikar min akwatin kayana.
“Ina wuni Hajiya ?”
Da sauri ta juyo ba ta yi tsammanin zan tashi ba.“Jameela kin tashi? Nace halan a ƙafa kika dawo kike wannan mugun baccin?”
Zama da maɗaukin kanwa shi ke sa farin kai.Kasancewar ina tare da Hajiya Momah da kuma su Rumy tuni na halbo jirgin wato Hajiya zargina take.
Sai kuwa na ce mata “Wlh kuwa Hajiya ,halan Alhajinmu ya sanar da ke ya ɗauko ni, lokacin har na ma kusa kawowa gida.Yayi faɗa sosai ya ce miyasa ban tambaye ki kuɗin taxi ba ai ba za ki hana min ba,ni kuma wlh Hajiya kunya nake ji yadda kuke ta ɗawainiya ina laifin ciyar da ni da kuke hakan ma alkhairi ne.”
“Amma kuma shi alhajin bai ma shigo ba,to wai ina saurayin ki ba kin ce makarantar ku ɗaya ba?”
Na yi saurin dirowa daga kan katifa na ce “yawwa don Allah Hajiya ina neman alfarmar ki roƙa min Alhaji kan Sadiq ya dinga zuwa zance”
Hajiya ta washe baki ta ce “ke babu damuwa kawai kar ki damu” sai kuma ta fice,na bi bayanta da harara ,na ɗauki waya na shaidawa Alhaji komai kafin na shiga toilet.
HAJIYA TURAI
Ta na fita daga ɗakin Meelat ta kira ƙawarta Mabaruka,“ina ga babu komai a tsakanin su kawai ya sauketa ne kawai yayi”
“Ki dai ci gaba da kulawa kamar yadda kika ce ɗin,amma yadda baƙauyar yarinyar nan ta yi mugun canzawa da wuya in ba ta san maza ba”
“Zan kula,kin ga sai an jima bari na kira alhajin na ji shi mi zai ce” ta na gama faɗar haka ta kashe ta kira Alhaji .
Kamar yadda Meelat ta shaida mata shi ma haka ya ce a ƙarshe kuma ya fake da yi mata faɗan mi yasa take barin Meelat babu kuɗi ko ta manta ita ɗin amanarsu ce.
Hankalin Hajiya Turai sai ya ɗan kwanta ta basar.
Sai da na gama sallah sannan na fito falo riƙe da takardun karatu ina dubawa yayin da kuma Hajiya ta wuce kitchen.
Ina cin abinci na miƙe na cewa Hajiya sai da safe gobe zan zana jarabawa ina son yin karatu sosai.
Babu laifi sai wuraren sha ɗaya na tsaya da karatun da nake don wayata ma kasheta na yi.Wanka na shiga bayan na fito na shafe jikina da mai,sannan garin da Hajiya Momah ta ban na ɗauko shi na zuba madara na sha .Ina kunna waya Alhaji Nera ya kira ni,hira sosai mu ka yi ta tayar da hankali don har video call ya min ya na nuna min kansa.
Kayan baccin na saka farare sannan ɗora dogon hijabi a sama,na kunna pampo na ƙage ƙofar kafin na fita zuwa ɗakin Alhaji .
Hajiya Turai kuwa sam ta kasa bacci,tunaninta na kan Meelat hakan ya sa ta fito .Jin tsit babu muryar Meelat wacce ta yi ta ɗaga wa ɗazu ta na karatu ya saka ta saurin isa ɗakin. Wayam babu kowa kan katifa sai tarin takardu da kuma ƴar ƙaramar waya,Hajiya ta ƙara sa ta ɗauki wayar ta na mai kallon toilet da take jin motsin ruwa.Fitowa ta yi har za ta shiga ɗakinta sai kuma tace bari ta dubo Alhaji Nera.......
Mu haɗe💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
My book is only 300 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822
[03/09 à 08:33] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️
MRS SADAUKI 💫✍️
FCWA ☀️
Special gift fo my VIA FANS 🪷
My book is only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822. Ko kuma katin MTN,ƴan Nijar kuma carte airtel ta 300f
*Last Free page 8*
“Tok! Tok! Tok”
Na yi saurin tashi daga kan ƙirjin Alhaji Nera ina mai duba ƙofar wacce zuwa yanzu an dakata.
“Ka ga abin da nake guje wa ko? Hajiya ce fa ke buga ƙofa ” na faɗa ina mai jawo kayan baccina zan maida Alhaji yayi saurin riƙe ni ya na mai cewa “ƙofar a rufe take ba za ta shigo ba,kuma ma fa ke ce ke damun kan ki Hajiya ba ta da matsala ta sani sarai ina harakar mata”
Idonsa na kalla ko kunya ba ya ji,shi fasiƙancin ma ado yake da shi.
Jawo ni yayi ya ci gaba da cewa “kin ga har ta yi tafiyarta ko? Zo Baby ki saki jikin ki”
Ba wai tsoron Hajiya nake ba,a'a kawai ban so ace ta tarar da ni da mijinta cikin wannan halin shi yasa na ƙara zillewa.
Nan na ga fushin Alhaji Nera ƙarara ya na cewa “wlh in ki na tsiyar zan iya buɗe ƙofar nan ta gan ki kin ga shikenan sai mu bar ɓoyon nan”
Fahimtar ƙaramin aikinsa ne ya saka na yarda mu ka ci gaba da masha'a.
Bayan komai ya kwana na mayar da kayana,a gabana Alhaji ya jawo system ya na duba Camera da ya saita a falo,sai kuma ya shiga ta ɓangaren Hajiya Turai ta na kwance kan bed ta na sharara bacci.
Na dube shi da mamaki,shi kuma ya ɗagan gira ya na cewa “kin zata haka nan kawai na ce ki fito ɗazu? Sai da na tabbatar ba ta falo ”
“Ka ce kuma ba ka tsoronta” na faɗa ina hararensa don wlh zuwa yanzu na yi mugun raina Alhaji .
Ya ɗan bugu kumatuna da yatsunsa biyu ya ce “ita ɗin matata ce,rigar mutumcina .Ta dalilinta ake min kallon mutumen kirki,nan da ace ban ajiyeta ba to ina mai tabbatar miki da tuni sunana ya ɓace a gari”
“Shi yasa kake zuwa hotel kenan? Can sunan naka ba zai ɓace ba kenan?” na tambaye shi ina mai tsure shi da ido.
“Yanzu dai wuce ki koma ɗakin ki,zan kira ki”
“Kiran mi za ka min kuma? ” bai ban amsa ba ya je ya buɗe min ƙofa na fice.
Ina komawa ɗaki na ɗaga katifa na ɗauko key na buɗe toilet.Tsarkake jikina na yi sannan na fito na kwanta,kamar yadda na yi tsammani Hajiya ta ɗauki wayata wacce babu ko layi a ciki,kwanciyata na yi ban ɗau lokaci ba kuwa bacci ya ɗauke ni.
Hajiya Turai
Dama kusan jefi-jefi ta na duba Alhaji don kar ya fahimci zaman kuɗi take ba wai don ta na son shi ba.Wayar Meelat ta bincike sai dai babu komai a ciki wannan ya saka ta yi kwancinta.Sai tsakar dare wuraren asubahi ta farka,wayar Meelat ta je ta mayar inda ta ɗauke ta.
Washegari
Kamar kullum tun safe na shirya tsaf cikin shiga mai kyau.Ƙaramar wayata na gani na ɗauka ina murmushi,zuwa yanzu na fahimci duk wacce ta ɗauki harakar duniyanci to ta na buƙatar abubuwa na dabaru.
Takardu na ɗauka tsaf na fito,kamar yadda na yi tsammani ta na kitchen.Na leƙa na gaisheta,ta miƙo min abinci cikin kwano mai kyau ta na mai cewa “ga shi ki tafi da shi tun da ba ki iya jira”
Na sunne kai na ce “eh saboda kar mota ta bar ni ne”
“Oh! Na manta bari na ɗauko miki ko da 1k ne” cewar Hajiya kafin ta fice daga kitchen ɗin.
Hajiya na shiga ɗaki ta ɗauki kuɗi bisanin ta fito.
“Jameela ga wannan ki hau mota sauran ki ci abinci” na karɓa tare da yin godiya na fita.
Maimakon na tsaya jira Bus kamar kullum kawai sai na samu kaina da tafiyar ƙasa,ina tafe ina tunani a bayana na ji Horne.
Na tsaya tare da ɗan juyowa,a hankali aka sauke glass ɗin idona yayi tozali da wani matashi a ƙalla zai haura shekara arba'in a duniya.
“Hajiya an tashi lafiya?” ya furta cikin muryasa mai shegen daɗi.
“Alhamdullah” na amsa ina wasa da ido.
“Sai ina?” ya tambaya ya na kallon takardun hannuna,na masa wani kallo kafin na ce “suyar awara”
Ban sani ba ko ya fahimci baƙar magana ce ba,sai ya ƙyalƙyace da dariya ya ce “ai kuwa fatar jikinki ba ta yi kama da mai raɓar wuta ba ,ta fi dacewa da masu zama ƙasan ac.Am...in ba damuwa ki shigo na ajiye ki mana”
Sai da na ɗan yi jim bisanin na je na shiga,“sunana Bashir Sudan,Kano-kano nake zuwa ina da mata ɗaya da yara biyu fatan ban miki tsufa ba?”
“Daga rage min hanya sai nace ka yi min tsufa?” na faɗa tare da basarwa na yi kamar ban fahimce shi ba.
“Mi sunan ki?”
“Meelat!”
“Wato Meelat tuntuɓe na yi da sonki ƙaunarki kuma ta min dabaibaye tun a kallon farko”
“Allah sarki” na faɗa ina ƙare masa kallo,fari ne tass ya na da ƴar ƙiba ga saje da jan leɓo sai na ji ina sha'awar sumbatar su.
“Don Allah ki taimaka ki amince min”
Na saki makirin murmushina wanda na koya gun Momah tare da ƙanƙance ido ina tara wasu ƙwalla na ɗauke hankali,na karyar da wuya na ce “Allah shige mana gaba”
Cikin jin daɗi Bashir ya karɓi lambar wayata,sai a lokacin na sanar da shi kuma University zan je.
Daidai ƙofar makarantar ya ajiye ni tare da fiddo dumbujen kuɗi ya zaro min 20k ras,ko irin ɗan jan ajin nan ban yi ba na karɓe shegu.Ina ƙoƙarin fita ya ce “mi zan sayo miki matsayin tsaraba,sannan please ina son zuwa gidan ku tun yau”
Kalmar zai zo gidanmu ya saka ni jin wani mugun daɗi,nan na yi masa kwatance cewa Zariya ta uku nake.
“Abin da zan sayo miki fa?”
“Duk abin da ka sayo Meelat na son shi” na faɗa ina murmushi.
“Don Allah turo min hoton ki kafin ki tafi”
“Bari na tura ma ta WhatsApp kawai tun da ka ban lambar ka” na faɗa tare da kunna data,ban tafi ba sai da na tura masa hotuna.
Ina shiga ciki na zame ɗakin Raheela inda take kwana.A kwance na tarar da ita ta yi wanka ta shirya ta na duba takardu .
“Jameela babu ko sallama?” ta faɗa tare da tashi zaune,cike da murna na zauna kusa da ita ina cewa “Heelat na yi babban kamu yanzun nan bisa hanyata ta zuwa makaranta na haɗu da wani kyakkyawan saurayi fari mai saje”
“Shine sai ki shigo babu sallama?”
Na tamke fuska na ce “ke fa matsalata da ke kenan! To maganar sallama ba ta wuce ba,in ba ki ji daɗin ganina ne ba sai na fita na bar miki ɗakin ki” na faɗa cikin fushi.
“Allah baki haƙuri ina son dai sanar da ke ne muhimmancin sallama” Raheela ta sake faɗa.
“To sai ki yi ai !” na faɗa tare da fara danna waya sai na ga Bashir shi ma ya turo min hotunan shi.
“Masha Allah! Kyakkyawa kuwa da shi amma Jameela wannan kamar ya na da mata” Raheela ta faɗa.
“Ina ruwana da matar shi tun da ba auren shi ba zan yi! ”
“Jameela...” na yi saurin katse “Meelat za ki ce ban son sunan Jameelar nan”
Sai da Raheela ta yi dariya sannan ta ce “sunan kuwa na ƴan gayu! Amma don Allah da gaske ba auren shi za ki yi ba?”
“Kuɗinsa kawai zan ci.Heelat dubi laɓansa uwannan sai sun yi daɗin sumbata” na faɗa ina cije leɓena na ƙasa.
“Kin ce ba auren shi ba za ki kuma ki na zancen sumbata”
“Au! Aure kawai yake sa a sumbaci mutum Heelat?”
“Wai ni ce Heelat ɗin?”
“Eh ko bai yi daɗi ba?”
“Yayi sosai ma.Mu tashi mu tafi ko ƙarfe bakwai har da minti ashirin ” ta faɗa ta na kallon agogon wayarta.
“Ina wacce kuke kwana ɗaki guda?” na tambaya.
“Ta fita tun ɗazu wai motsa jiki”
Na miƙe ina cewa “ba ta son ta yi ƙiba ne halan?”
Ba ta ban amsa ba har mu ka fito ta rufe ɗakin,mu ka nufi ɓangaren da ake karatu.
Duk ko wane ɗalibi sai duba takardu ake,mu kam zama mu ka yi ina ta baiwa Raheela labarin Alhaji Nera yadda yake kashe min kuɗi amma ban sanar da ita ya na nemana ba.Mu na nan zaune sai ga Sadiq da Hafiz ,ko wane facing budurwar shi ya zauna kafin mu fara taɓa hirar da su.
Shigowar malamarmu ya sa kowa ya nutsu,kamar yadda mu ka yi tsammani ita ma jarabawa ta rubuta mana ta na mai cewa “Ya kamata ku dage sosai ku ƙara hazaƙa don kun kusa tafiya stage za a kai ku asibitoci ku ga yadda aikin likita ke gudana”
Cike da murna na cewa Heelat “na matsu na saka farar rigar nan”
“Za ta yi miki kyau sosai,amma ai ba sai mun sa ba”
Malama ta ci gaba da cewa “ku yi shiru ku ci gaba da aikin gaban ku,in an tashi kowa sai ya nemi farar rigar likitocin ” sai kuma ta fara zagayen ajin.
Duk tambayoyin na san su hakan ya saka na riga kowa idawa na baiwa Madam na fice.
Alhaji Nera na yi text na shaida masa ina jin yunwa,ya kuwa ce na jira zai kawo min.An ɗauki kamar minti ashirin sannan ya zo,har cikin makaranta ya shigo na je na karɓo sannan na zauna kan dakalin nan mai kamar kujera da ake yi cikin makaranta.
Ina tsaka da cin frite da dunƙulalar kaza, Heelat ta fito.Zama ta yi mu ka ci gaba da ci,dai hirar jarabawar mu ke.
Bayan mun gama mu ka hauda da exotic,sai a lokacin na sanar da Heelat cewa Alhaji Nera ya kawo min.
“Ƙawata Alhajin nan na ji da ke gaskiya,to amma ya za ki yi da Bashir?”
“Kowa da matsayinsa” na bata amsa.
“To wa kika fi so?” dariya kawai na yi na ce “so? Tabbb ! Ba ki taɓa bani labarin soyayyar ki da Hafiz ba”
“To ai a gaban ki ake komai” cewar Heelat ta na mai fara duba wayarta sai kuma ta ci gaba da cewa “jarabawar ta yi wa Habibyna wuya bawan Allah ”
Ci kan ki ban ce mata ba na yi kamar ban ji ba,don na ga alamu irin rawar kan amare ce take son nuna min .
Bayan kowa ya fito sai kuma mu ka ci gaba da yin cours har lokacin tashi yayi .Yau ban je koyon mota ba direct gida na wuce,a falo na tarar da Hajiya ta na cin dambu,“Jameela har an sauko? Ina kwanon da na zuba miki abinci?”
Gabana ya faɗi don kuwa na manta shi a motar Bashir,ban sani ba yawan shirun da na yi ne ya saka ta ce “kar ki min ƙarya”
Hakan yasa kuwa na faɗa mata gaskiyar inda na manta shi sai na ƙara da cewa “ya ce zai zo yau ,in sha Allah zan ce ya biyo