Showing 6001 words to 9000 words out of 21708 words

Chapter 3 - CELEBRITY FARASHIN TASIRI Book Complete by Mrs Sadauki .txt

10 Jan 2025

2190

gaba da cewa “ki saka layin ki a nan na saya miki Moov ya na ciki har ma na buɗe miki WhatsApp ”
Ganin waya na sheƙi ya sa na yi saurin karɓa sai dai ban san yadda ake amfani da ita ba .
Sai da ya samu wuri yayi parking sannan ya saka min ɗayan layin nawa tare da nuna min yadda ake amfani da wayar .
A nan mu ka shiririce waje har aka yi sallar isha'i,a mota sosai Alhaji Nera ya yi bidirinsa da jikina.






Mu na zuwa gidansa Hajiya ta tarbe ni da murna,bisanin kuma ta ɗan ɓata rai ganin irin canjin da na yi wanda sam bai ɓoyiwa.


Alhaji Nera ya ce “ke fa kika ce na je na dawo miki da ita ko ba ki yi murna ba”
“Na yi mana Alhaji ,na gode” ta furta , Alhaji kuwa yi yayi tamkar a gasken ƙauye ya je ya ɗauko ni.




Ɗakina na shiga na tsarkake jikina na zo na yi sallah,bisanin na fara taƙilar wayata.Kira ne ya shigo da wata baƙuwar lamba,ina ɗaga wa Raheela ta ce “Ke wace jaraba wa ce aka yi yau? Na je gidan ku aka ce ba ki nan kin koma Maraɗi?”
“Wa ya baki lambata?” ita ce tambayar farko da na yi mata.


“Hafiz,yau da mu ka yi waya yake shaida min wai kin yi wayar hannu shine nace ya cewa Sadiq ya turo masa lambar ki shine shi kuma ya ban”


“Hum! To me yasa ba ki tambayi Hafiz ɗin ba ya faɗa miki jarabawar da aka yi ɗin?”


“Hum! Jameela na san babu wata jarabawa akwai dai abin da ya maida ki ”


Shiru na yi ina ɗan tunani can ƙyarƙyaro ƙaryar “wlh ban iya zama ne babu fanka shi yasa na gudo ”
Dariya Raheela ta yi sosai ta na mai cewa “shi fa ɗan ƙauye bai iya waye wa ba”
Ni ma dariyar na yi ina mai ce mata “sai ma in kin ga yadda na yi kyau,sosai Hajiya Turai ta ji daɗin dawowata yanzu haka tuni ta fara yi min sayayya ta kai ni salon an wanke min gashi in kin ganni sai kin yi santi ”


“Wai gaske ko wasa?”
A yanayin yadda na ji ta yi magana tuni na fahimci tata cutar ta motsa,wato hassada.
Cikin tabbatarwa na ce “da ace babbar waya ce gare ki kamar ni da na turo miki hotunana kin gani”
“Ok yayi sai an jima” shi ne abin da ta faɗa ta na mai kashe kiran.




“Shegiya munafuka ! Sunan Malama ce amma hassada na ciciyar ruhinta mtsw! In ma mutuwa za ki yi sai dai ki mutu don nan kusa kaɗan zan zama babbar yarinya” na furta a fili ina juyi kan katifata.




Da dare misalin sha biyun dare text ɗin Alhaji Nera ya shigo wayata don sam na kasa bacci sai faman yin hotuna nake.
“Ki kunna data” shi ne abin da ya ce min.
Na yamutsa fuska don sam ban jin daɗin WhatsApp ɗin ba iya lambarsa ce sai ta Hajiya Momah kawai ke kan wayata,Sadiq kuma ƙaramar waya ce da shi balle mu yi hira.
Ina kunna data kiransa ya shigo,sanye yake cikin kayan bacci na maza duk muninsa ya ida fitowa.
Halshe ya fiddo cike da shaƙiyanci bisanin ya tambaye ni “ba ki yi shirin bacci ba?”
“Shi bacci har shiri ake yi masa?” na tambaye shi .
Kai ya jinjina ya na mai cewa “eh mana da wannan rigar za ki kwanta?”
“Eh ai ban daɗe da saka ta ba”
Wata dariya tuntsire da ita bisanin ya kashe kiran ya fara turo min hotunan ƴan mata cikin kayan bacci.
“Su kuma uwannan su waye?”na tambaye shi .
“Ƴan Matana ne!” ya ban amsa.
“Duk kai ɗaya sama da mace biyar?”
“Akwai ma uwanda ban turo miki ba,ki na son irin kayan jikinsu?”
“Eh ina so” na basa amsa .
“Ok gobe sai ki shirya mu je ki zaɓo ”
“A'a ni ba za ni ba sai dai ka kawo min,Hajiya zan yi wa wankin kaya”
“Ok ba matsala,amma don Allah cire rigar ki zauna haka nan yanzu zan kira ki ina son ganin ki”
Wani haushi ne ya kama ni,wato in na fahimta Alhaji so yake ya mayar da ni karuwarsa......
[01/09 à 07:59] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️


MRS SADAUKI 💫✍️


FCWA ☀️


Special gift fo my VIA FANS 🪷


My book is only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822. Ko kuma katin MTN,ƴan Nijar kuma carte airtel ta 300f




Page 5




Ina ƙoƙarin kashe data hotunansa suka shigo wayata,duk na tsaraicinsa ne.Ban san mi yasa ba ,kawai sai na shiga buɗe su abun takaici har da videos.Da dai na fahimci Alhaji Nera na son dole ya mayar da ni cikakkiyar ƴar iska sai na kashe data tare da saka wayar caji.Ina ƙoƙarin kwanta wa na ji text ya shigo,na duba.Sadiq ne ya turo min good nigth my dear,na ɗan murmusa bisanin na mayar masa da thanks kawai na kashe wayar.




Washegari


Kiran sallar asubah farin na yi wanka na yi sallah sannan na fito na fara wankin kayan Hajiya wanda tun jiya ta fitar da su.
Ina wanki ina tunanin sabuwar rayuwata har na gama.Hajiya Turai sai washe baki ake an samu banza,abincin breakfast ta kawo min har ɗakina.Na zauna na ci na ƙoshi sannan na zauna na kunna wayata,text ɗin Alhaji Nera ne birjit kai kace ya ban ajiya.Nan na shiririce wurin karanta saƙonninsa masu nuni da yadda yayi kewata,yadda na fita daban cikin ƴan matan da duk yake tarayya da su.Haka kawai na ji wani kishi kamar mijina,bisanin na koma duba text ɗin Sadiq .Yadda ya tsara min kalaman soyayya ya saka ni saurin kiransa ban shirya ba,ya ɗauka muryarsa a dishashe alamun daga bacci ya farka.
“Manya masu gari har yanzu ba a tashi ba?” na tambayesa.
“Wlh na gaji ne sosai ,jiya wuni na yi ina aiki shi yasa ma kika ga ban kira ki ba”
“Aikin me?” na tambaye shi ,ya ɗan yi shiru bisanin ya ce “Kadiro na je na yi dako,wlh so nake kafin ace mun je hutun ƙarshen shekara na tura magabata na ko baiko ne a yi ma mu kafin na haɗa na lefen”


Gabana ya faɗi,sai na ji kuma ban son maganar auren.To in ma an yi mi zan kai masa? Sauran mazan? Sai na ce “Sadiq don Allah ka mayar da hankalin ka kan karatu,duka fa yanzu ne mu ke shekarar farko cikin shekaru huɗu da za mu yi muna karatu”
Ya ja wata doguwar ajiyar zuciya ya ce “Ke ma haka za ki ce? Hum! Mama ma da na yi mata maganar ki ta ce na fara gama wa da karatu tukunna.Jamee wlh ina tsoron abin da zai raba ni da ke,ina tsoron kafin nan da shekara huɗun nan ki waye sosai ta yadda za ki fin ƙarfina”


Na yi ƴar dariya na ce “mace har ƙarfin namiji take?”
“Sosai kuwa! Jamee don ba ki san irin baiwar da ke tattare da ke ba ne shi yasa kike ɗaukar kan ki ƙaramar yarinya,amma ke ɗin ta daban ce”
“Kai ma ai haka kake ”
“Hum! Ba dai kamar ke ba,ina son ki don Allah ba don kyawun ki ba.Amma na san nan gaba duk wanda zai so ki to tabbas kyawun ki ne zai jan shi”


“Yanzu dai sai an jima,ka ci gaba da yin baccin ka” na furta tare da yanke kiran na lumshe ido bisanin kuma na miƙe kamar wacce aka tsikara na fita zuwa ɗakin Hajiya Turai.
Ba ta nan ciki,ƙarar ruwan da na ji a toilet na fahimci wanka ne take.Gaban dressing mirror na tsaya ina ƙare wa kaina kallo.Doguwa ce ni amma ba sosai ba,haka ba za a kira ni da siririya ba saboda shaf ɗina da ya fita kamar coca cola.Manyan idona masu dogayen gashi na ƙyafta haɗi da yin wani fari da su ina ɗan murmusa,dimple ɗina ya lotsa.


Tun ina yarinya babu abin da ke burge ni sama da rawa, wannan ya saka na ɗan fara girgiza irin yadda indiyawa kan yi rawa.
Hango Alhaji Nera na yi a tsaye bakin ƙofa ya harɗe hannuwa ya na kallona, “ci gaba!” ya furta min.
Zan yi magana Hajiya Turai ta fito daga toilet ɗaure da zane.
“Ke mi kike yi ɗakina? Alhaji mene ne za a ci gaba?” ta tambaya sai dai tun kafin na kai ga cewa wani abu Alhaji Nera ya ce “yanzu na shigo waya ce nake,lafiya ina za ki je na ga kin yi wanka”
“Ke kuma mi kika tsaya ki na yi?” Hajiya ta faɗa ta na kallona,na ɗan sosai kai nace “dama madubi nake so don Allah ki ban ko da guntu ne”


“Iyeee! Abu ga Fulani ! Bari na duba miki” ta faɗa tare da jawo tiroirs ta ban wani ɗan madaidaicin madubi da murna na karɓa na fice.


Ɗakina na koma ina ta kallon fuskata wacce ko maƙiyina yayi kaɗan ya ce banda kyau.
Wayata ta ɗau ringing na ɗaga,“don Allah ki fito na yi miki ganin ƙarshe ina son fita,sannan ki faɗan lambar bra da pant ɗin ki sai na sayo miki” Alhaji ya faɗa ina jin ƙarar mota.
“A'a na gode zan saya da kaina,don Allah Alhaji ka yi haƙuri ni ban son abin da kake yi min”
“Au! Kin fasa cika muradun naki na hawa motar kan ki da kuma rayuwa mai kyau?”
Shiru na yi ,sai kuma nace “amma hakan ka na ganin ....” sai na yi shiru saboda yadda Hajiya Turai ta shigo ɗakin ,ta kuma wani kafe ni da ido kamar mai zargin wani abu.




“Meelat ki mori ƙurciyar ki daga Kano sai Abuja ,don Allah kar ki bani kunya ko fito ina jiran ki” Alhaji Nera ya sake faɗa.
Murya na ɗan rawa na ce “Sadiq don Allah ka fahimce ni,karatu ne a gabana yanzu ba aure ba ka ga ma Hajiya nan tsaye ta rutsa ni ina waya” fuskar Hajiya ta ɗan sauya ta style ta na mai ci gaba da kallona.
Alhaji Nera gogagen ɗan duniya ne,ya tuntsire da dariya don ya fahimci abin da na son sanar shi ya ce “ok babu damuwa zan sayo miki kayan baccin” sai ya kashe.


Na ja tsuki ina mai mayar da hankalina ga Hajiya Turai na ce “hajiya ko da wani aiki da zan yi?”
“A'a babu,wane ne Sadiq?”
“Wani ɗan makarantar mu ne da yake sona,wai har ya far maganar aure sai kace wasar yara”
Hajiya ta washe baki ta ce “to in ba abun ki ba Jameela nan za ki zauna babu aure? Kawai ki amince masa ya fara zuwa zance!”
Cike da ladabi na amsa da “to Hajiya ” bisanin ta fice,na bi bayanta da harara.




HAJIA TURAI


Sanin halin Alhaji Nera na akuyanci ya saka kullum take kakau da Jameela,ko ba komai yarda ce ta saka mahaifinta kawota gidan karatu ba tare da ya san Alhaji Nera akuya ce da fatar kura.
Ba ta taɓa damuwa da ƴan matan Alhaji ba saboda ta san bai haihuwa balle ace ya yi wa wata ciki ta ji kunya,sannan ta na zaune da shi ne saboda kuɗinsa mutuwarsa kawai take jira ta ci gado.
Ɗaki ta koma ta ƙara kashe ɗaurin kallabinta na less ,sosai ta yi kyau . Kitchen ta shiga ta ɗora girkin rana.




Ɓangaren Alhaji kuwa sosai ya so Meelat ta fito su yi ban kwana,wani irin mugun sonta yake ji a ransa.So ne na sha'awa ba wai aure ba,hakan ya sa bai wani ji zafi don ta ambaci sunan Sadiq .






Sadiq
Ko da Meelat ta kashe waya tashi yayi ya je yayi wanka ya shirya tsaf ya tafi gidansu Hafiz.Cikin ƴar rumfar shaƙatawar da ke tsakar gida suka zauna.
Hafiz ya ce “ya na gan ka cikin damuwa?” Hafiz ya tambaya.
“Ba dole ba! Son Jameela yayi min kamun sandar makauniya.Wlh abokina mugun sonta nake,amma talauci ya min iyaka da cikar burina”
“To ai da zarar ka gama karatu aiki za ka nema,ka ga da ka samu shikenan”
“Amma kai auren ka da Raheela zuwa yaushe ne?” Sadiq ya tambaye shi.
Hafiz ya ce “jiya mun yi magana da Daddy,ka san tun can dama ya ce zai buɗa min kanti amma na ƙi to shine yanzu na amince.In ya so zuwa ƙarshen shekarar nan sai a yi auren ”




“Masha Allah! Nan da wata shidda kenan? Amma kun yi magana da ita Raheelar?”
“Eh! Ɗazu ma har Mamarta ta ban mu ka gaisa ”


Su na nan zaune su na ta hirar rayuwa motar Daddyn Hafiz ta shigo.Da sauri suka je suka gaishe shi,ya amsa ya na tambayar Sadiq Mamar shi ya amsa da ta na lafiya bisanin su koma su zauna.
“Abokina ya kake ganin in na fara zuwa da motar can ta Daddy makaranta?”
Cike da murna Sadiq ya ce “wlh za mu ji daɗi,ka ga sai na ajiye babur ɗina dama wani sa'in na mai na yi min wahala”


“Da mun sha yawo kuwa,jiya Raheela ta kira ni akan na saya mata babbar waya don Allah mu je ka yi min rakiya ”
“Ok to babu matsala”


Nan suka tashi suka je Tof Galaxy gidan sayar da waya.Tecno Pop2 Hafiz ya saya kala biyu iri ɗaya sannan suka fito,tun a hanya ya cire layinsa ya baiwa Sadiq tsohuwar tashi ya ce “ga wannan ka sa naka layin tunda na yi sabuwa ni da masoyiyya ” tsabar murna ya saka Sadiq idonsa cika da hawaye ya na ta godiya.






MEELAT




Tun fitar Hajiya Turai na zauna ina latse-latsen waya.Kiran Hajiya Momah ya shigo kamar ba zan ɗauka ba sai kuma na ɗaga.Gaisheta na yi ,ta ce “Su Meelat fushi ake da Momah ? Ko ɗan text ɗin nan na Barka da safiya?”
“Hum!” na ja ƙyaci.Ta ci gaba da cewa “to tuba nake ,dama kayan bacci ne Alhaji Nera ya ban kuɗi ya ce mu je sai na saya miki,yaushe kike da lokaci sai mu je?”


Cikin zumuɗi na son abu mai kyau na ce “jira gani nan zuwa” ta yi ƴar dariyarta da ta saba,sannan ta kashe wayar.
Sai da na sake yin wanka na shirya tsaf na fito.A kitchen na samu Hajiya Turai,“hajiya zan fita sai na dawo”
Ta juyo ta dube ni ta ce “Ah! Ah! Irin wannan uwar kwalliya ko dai wurin Sadiq ɗin za a je?”
Na ɗan sunne kai na ce “eh wai za mu je gun wata ƙanwar babarsa ne”
“Ok to ki kula da kan ki banda shashanci a hanya” cewar Hajiya .




Ina fitowa na tsayar da mai taxi ,dama ina da kuɗi ADS nace ya kai ni can unguwar su Hajiya Momah .Ya na sauke ni na shiga gidan kai tsaye,yau falon tsit ba kowa sai Hajiya da wata sabuwar fuska.
Na gaisheta kafin na samu wuri na zauna,gasashen kifi ta sa aka kawo min da kuma jus.


Na kuwa ci don akwai ni da son daɗi.Bayan na gama ne sai Hajiya ta dube ni ta na cewa “ jira ya na hanya”
Na dube ta da ɗan mamaki amma ban ce komai ba.Ko minti biyar ba ayi ba sai ga Alhaji Nera,sai wani rarraba ido yake ya dube ni ya dubi kuma baƙuwar fuskar da na tarar zaune wacce take wata zankaɗeɗiyar budurwa.


Kuɗi ya miƙa wa Hajiya ya na cewa “ga shi sai ku zaɓo masu kyau, Allah sa kafin ku dawo lokacin na gama”
Hajiya ta karɓa tare da miƙewa wannan ya saka ni ma na miƙe ina duban Alhaji Nera da bai da niyyar tafiya,don har mun fito daga falon.
“Hajiya shi kuma Alhaji fa? Mene ne yake maganar zai gama?” na tambayeta lokacin har mun shiga mota.




Ta yi ƴar dariya ta ce “matsalata da ke kenan Meelat ba ki iya cin ƙwan makauniya ba,sai kace ba ƴar hannu ba to mi zai yi bayan ya kwashi Gara.Ki gode wa Allah duk cikin ladies kin fita daban ke ce ƴar gaban goshi ”
Ban sake cewa komai ba har mu ka isa mall ɗin.Kayan bacci,pant,bra,kadar mata da kuma turare mu ka sayo bisanin mu jiyo .




Lokacin da mu ka isa gidan Hajiya Momah ,ko zama ba mu yi ba Alhaji Nera ya fito daga ɗakin nan na jiya ya na gyaran azargagin wandonsa.....






Just 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,MD +22795045822
[01/09 à 13:56] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️


MRS SADAUKI 💫✍️


FCWA ☀️


Special gift fo my VIA FANS 🪷


My book is only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822. Ko kuma katin MTN,ƴan Nijar kuma carte airtel ta 300f




Page 6




Kallon sheƙeƙe na yi wa Alhaji Nera ,ina ƙoƙarin kawar da kaina ita ma budurwar sai gata ta fito. Kallo guda za ka yi mata ka san ta gurzu ba laifi don yanayinta ya canza sosai,jan bakin duk babu, kwalliyar fuskarta kuwa duk ta dame.


“Har kin fito? Ina cewa na haɗa miki ruwan wanka” Hajiya ta faɗa.
Ta ɗan yi dariyar yaƙe ta na mai zuge zip ɗin jakarta ta ɗauko 2k ta baiwa Hajiya Momah .
Wani mugun kallo hajiyar ta yi mata ta ce “kar ki ɗauke ni ƴar iska mana! Mu je ciki” ta ja hannunta ƙiiii suka koma ɗakin.




Alhaji Nera ya yi dariya ya na mai cewa “hajiya Momah manya” bisanin ya zauna kusa da ni ya ce “Baby ya na ga sai cin magani kike? Ko wani ya ɓata miki rai ne uhum?”
Zan buɗe baki na yi magana wayata ta ɗau ringing,sunan Sadiq ne ɓaro-ɓaro ke yawo a kan screen ɗin.
Ban damu da Alhaji Nera da ke kusa na ba na ɗaga,cike da murna Sadiq ke shaida min yayi babbar waya har ma ya turo min hotunan shi ta WhatsApp na hau online na gani.


Na ɗan saki murmushi na ce “yaushe? Ah ! Kace ka faso gari ?”
“Ni ma fa Hafiz ne ya ban wayar,yau ya sayi sabuwa shi da Raheela ”
Tuni na fahimci Raheela ta yi masa ƙorafin Android shi yasa ya saya mata.
“Ok zan duba ,yanzu ina wani aiki ne ” na faɗa tare da kashe kiran.
“Wai don Allah waye Sadiq ɗin nan? Na ji ɗazu sunansa kika ambata don lurar da ni Hajiya ta shigo ɗakin ki”
Labarin Sadiq na basa da yadda yake mugun sona har yayi min alƙawarin aure .
Ga mamakina sai na ga fuskar Alhaji Nera ta canza,“ke da ke karatu ya zai yi miki maganar aure yanzu? Kuma ma mi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login