Showing 15001 words to 18000 words out of 21708 words

Chapter 6 - CELEBRITY FARASHIN TASIRI Book Complete by Mrs Sadauki .txt

10 Jan 2025

2193

min da shi”
“Ya na da kuɗi sosai kenan?” Hajiya ta faɗa ta na washe baki,ganin haka ya sa na zauna ina ta bata labari har da kuɗin da ya ban.




“Ah to yanzu na ji zance! Shi wancan faƙirin yaron ki fita harakar shi,yo yaushe ya gama karatun har ya nemi aiki har ku yi auren” cewar Hajiya ta na mai ƙara ƙawata min auren mai kuɗi.
Da na gaji dai na je na yi wanka sannan na zo na ci abinci.










Da dare misalin ƙarfe tara Bashir ya zo.Ya samu kyakkyawar tarba gun Hajiya don har ciki ya shigo ya gaisheta bisanin mu koma can waje cikin motar shi.
“Ɗazu sai kika bar wa mijin ki abincin breakfast” ya faɗa ya na murmushi.
Na ce “Eh wlh manta wa na yi sai da na dawo gida sannan Hajiya ta tuna min”
“Abincin yayi daɗi ga kwanon nan na gode”


Nan mu ka fara yin hira sama-sama har motar Alhaji Nera ta zo ita ma.Duk da ya na dare akwai hasken ƙwan fitila,yadda yayi tsaye ya na kallonmu ya saka Bashir cewa “bari na fita na gaishe shi” bai jira cewa ta ba ya je ya gaishe da Alhaji ,shi ya shiga gida yayin da Bashir ya dawo.
“Gida zan shiga na ga dare ma ya soma yi” na faɗa zuciyata na ɗan dokawa.




“Daddyn ki na da tsanani halan? Allah sa dai kar ya min iyaka da ke” cewar Bashir kamar zai yi kuka.
“Kar ka damu” na faɗa tare da ɗaukar kwanon na buɗe mota.Bashir ya miƙo min wata leda na karɓa na shige gida.






“Sarai kin san yarinyar nan amana ce aka kawo mana shine za ki barinta fita zance to daga yau sai yau kar na sake ganin wani ɗan iska ya zo min gida” shine abin da kunnuwana suka jiye min tun kafin na shiga cikin ɗakin.
A falo na tsaya na sunne kai ina sauraren masifar da Alhaji ke yi wa Hajiya kafin ya dawo kaina,da ya gaji kuma ya shiga cikin ɗakinsa.
Hajiya Turai ta ce “kar ki wani damu! Yo jiƙa ki za mu yi mu sha! Kawo mu gani mene ne ya kawo miki ”
Ledar na miƙa mata ta buɗe,ɗinkuna ne na atamfa guda uku sai gizner wacce ba a ɗinka ba da kuma less.
“Masha Allah! Ki na ji yanzu in kin shiga ɗaki ki kira shi ki ce saura kuɗin ɗinki in ya bada sai na kai miki gun tela a yi miki ɗinkin ƴan gayu ”


Sosai na ji daɗin yadda Hajiya ta ɗaure min gindi,ina shiga ɗaki na gwada kayan duk sun yi min cicif sannan na ɗauki waya na ce masa saura kuɗin ɗinki ko? Kawai ya kira ni.
“Su sauran ba su yi miki ba ne?” ita ce tambayar da ya fara yi min.
“Sun yi mana sosai ma”
“Shine ba za ki iya yi min godiya ba? ”
Ji na yi kamar ya watsa min petur,cikin masifa na ce “ka zo ka karɓi kayan ka in ka bani ne don na dinga ƙasƙantar da kaina wurin ka....” sosai na yi ta masifa.
Bashir ya ce “Meelat? Meeeela!” sai kuma na yi tsit,yadda ya kira ni cikin salo na fizgar rai sai na ji wani abu ya caki ruhina.


Da kuma na tuna da huɗubar Hajiya Momah kawai sai na fashe da kuka ina jan majina.Ina jin yadda Bashir ke sauke ajiyar zuciya.
“Yi shiru mana my Meelat! Ban son kukan ki! Amma don Allah ina miki kyauta ki dinga cewa kin gode”
A shagwaɓe nace “na ƙi ɗin! Kuma wlh sai na cije ka tun da ka bari na yi kuka”
Ya saki murmushi mai sauti ya ce “oh! My shagwaɓaɓiya irin wannan ai sai ki sa na zauce na dawo gidan ban shirya ba”
Cak na tsaya da kukan sangartar na ce “wai gaske ka na sona sosai?”
“Fiye da tunani! Yanzu dai sai da safe zan shiga gida ki kula da kan ki”
Haka kawai na ji haushi,amma na danne na ce “kai za ka kai ni makaranta gobe”
“Ok babu damuwa,zan fito zuwa shidda da rabi hakan yayi”
“Eh sai da safe” ƙittt na kashe kiran.
Text ɗin Alhaji Nera ne ke ta shigowa,ni dariya ma ya ban yadda yake nuna kishinsa a kaina ƙarara.
Ciki da izgilanci na tura masa “Ni ka yi wa faɗa ko? To yau babu inda zan je sai dai ka rungume pilow”
Ina gama tura masa saƙon ko minti ɗaya ba ayi ba ya kira ni,na ɗaga.
“Wallahi! Wallahi in ba ki zo ba in na fasa fita yanzu na je na shaida wa Hajiya Turai ke karuwata ce Shege Kuluwa ta haife ni.Wato Meelat ba ki son zaman lafiya! Duk gama ni da Sadiq bai ishe ki ba sai kin rakito min wani farin buzu wanda ka na ganinsa ka ga jarababe ”
Na tuntsire da dariya na ce “au! Buzaye jarababu ne kenan? Hum! Alhaji ni ka kira da karuwa? ”
“Ki dai fara shirya wa yau tun ƙarfe goma nake son ganin ki a ɗakina ”
“Ba zan zo ba”
“Sai kin zo!”
“To sai na gani in dole za ka yi min”
Ina gama tura saƙon na kashe wayata na je na yi wanka,cikin kayan bacci na shirya tsaf na kwanta tare da rungume pilow na fara tunanin Bashir .
Na lumshe ido ina ayyana cewa shi ne na rungume,tarau na buɗe ido tuna ya na tare can da matar shi na ja tsuki a fili na ce “wlh ba zan so ka ba!” sai kuma na turo baki gaba ina jin haushi.
Cikin wannan tunanin bacci ɓarawo ya ɗauke ni,jin ana hura min iska a fuska ya sa na fara buɗe idona a hankali da Alhaji Nera na ci karo durƙushe a gabana,ina shirin tambayarsa lafiya kawai ya sukuce ni yayi waje da ni.


Ina kiciniyar direwa mu ka yi kiciɓis da Hajiya Turai wacce ta fito daga kitchen,ruwan da ke hannunta ta saki yayin da shi kuma Alhaji Nera ke gyara min zama a ƙirjinsa.
“Alhaji mi nake shirin gani?”
“Abin da idon ki ya gane miki ai ba baƙon ki ba ne” ya gama faɗa ya nufi ɗakinsa da ni,kunyar duniya ta ishe ni tuni na fara hawaye. A ranar na tabbatar idon Alhaji Nera a ƙyanƙyashe suke,na yi tunanin Hajiya Turai za ta tayar da hankali ta zo ta yi ta kishin ƙofa sai kuma na ji tsit.A ranar ɗakin Alhaji Nera na kwana,mun kashe arna fiye da tunani inda a ƙarshe yayi min alƙawarin zai canza min gida na koma can da zama .


Washegari
Bayan na yi wanka a ɗakin Alhaji na saka doguwar rigarsa na fito,ɗakina na shiga na shirya tsaf tare da haɗa duk wasu kayan jikina da takarduna kamar yadda Alhaji ya faɗa.
Bayan na gama komai na fice zuciyata duk babu daɗi,duk da Alhajin ya tabbatar min ita Hajiya ko a kwalar rigarta zaman ta ci mai kyau ta sha mai kyau ne take da shi ta kuma rufa wa kanta asiri .


Sai na zo bakin titi sannan na kunna wayata ,nan kiran Bashir ya shigo ya tabbatar min ya na hanya .Ko da ya zo na shiga motar,ban cikin yanayi mai daɗi Bashir kuma ya fahimci haka don ya na ta tambayata amma ban basa amsa ba kawai sai ya wuce da mu filin ƙwallo na Maraɗi yayi parking mota ya ce na fito.
“Mene ne wai? Kin shigo mota kamar kurma,ina tambayar ki kuma kin yi shiru!” ya faɗa ya mai jingina da mota.
Ido na zuba masa nan na ƙara yarda da mai kyau ne na ƙarshen lamba,an ce so ya na shiga a kallo ɗaya kamar shigar sarɗe to ni ma hakan ce ta faru da ni.Ban san ya zan yi ba kawai na faɗa jikin Bashir ina mai fashewa da matsanancin kuka......






#Mafarin ƙaddara Meelat da Bashir




Nan zan tsaya da page na kyauta wato free page,duk mai so za ta biya kuɗin karatu only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822 ko kuma katin MTN,ƴan Nijar carte airtel ta 300f.


❌Kawai ki yi transfer don Allah ko kuma ki turo da kati👏🏻


NB: da zarar na kammala book 500 ne
[04/09 à 16:07] MRS SADAUKI 💫: 🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*FARASHIN TASIRI*🪺
```celebrity```🌬️
🪽🪽🪽🪽🪽🪽🪽
*Gajeren labari*🕊️


MRS SADAUKI 💫✍️


FCWA ☀️


Special gift fo my VIA FANS 🪷


My book is only 300 via 3184721842
Bala Maryam Mikailu first bank,sai ki turo da shaidar biya ta WhatsApp +22795045822. Ko kuma katin MTN,ƴan Nijar kuma carte airtel ta 300f


*Zuwa goma zan tsaya duk mai so ya biya kuɗinsa*🌚




Page 9




Duk yadda Bashir ke ƙoƙarin cire ni a jikinsa amma abu ya cuttura, saboda ba ƙaramin ƙanƙamesa na yi ba.
Wani abu nake ji wanda ban taɓa ji a ko wane namiji ba,a can ƙauyenmu na yi samari nan ma birni amma karon farko da na taɓa jin wannan lamari wai shi ƙwayar so.


A hankali na sassauta riƙon da na yi masa na ɗago jajayen idona da suke ta shatatar da hawaye.Gashin idona ya jiƙe sosai,shi yasa nake ganin fuskar Bashir dishi-dishi.Da mugun sauri na lumshe su jin ya na hura min iskar bakinsa bisanin ya sa tattausan hannunsa ya fara goge min ƙwallar.


Na ja da baya kaɗan amma za mu iya jin hucin juna.“Dubi yadda kika ɓata kwalliyar ki? Faɗa min mene ne ke damun ki?”
“Alhaji ne! ” sai kuma na yi shiru tuna Bashir kallon mahaifina yake yi wa Alhaji Nera.
“Wane Alhaji?” ya tambaye ni ya kamo hannuna.
“Daddy mana! Bai son na fara zancen soyayya ya fi son sai na gama karatu! Amma don Allah kar ka rabu da ni ina son...son ..kaaa !” Na yi ƴar gargada a kalmar ƙarshe saboda yau ne karon farko da na furta wa wani ita .




Daɗi sosai ya bayyana a fuskar Bashir ,a ɗan ruɗe ya fara tambayata “Meelat da gaske ki na sona? Za ki aure ni ? Wayyo Allahna! ”


Kai na jinjina masa ina murmushi sai kuma ya buɗe min mota na shiga,shi ma ya hau mazaunin direba.
Mu na tafe mu na tsara yadda rayuwarmu za ta kasance tare da yin soyayya a ɓoye ba tare da Alhaji ya sani ba har mu ka iso makaranta.Da zan sauka ya ban 2k don na ci abinci,yau ɗin ma ban yi masa godiya ba sai ce masa da na yi “sai an jima ka kula da kan ka!”
Ya saki murmushi mai sauti ya na cewa “na gode my Meelat ke ma ki kula min da kan ki banda kula samari”
Na yi ƴar dariya kafin na wuce ɗakun Raheela.




A tsakiyar ɗaki na tarar da ita ta baza kaya,“lafiya sai kace an fasa dilar Makka ?” shi ne abin da na faɗa daga shiga ta.
Yau ba ta yi ƙorafin sallama ba ta ce “yawwa don Allah Meelat zo ki taya ni zaɓar kayan da zan saka,kin san yau zan je gaida mahaifiyar Hafiz”


Na ɗan taɓe baki bisanin na taya ta duba kayan,don zuwa yanzu ita ma babu laifi Hafiz duk kusan ya canza mata sutura.Wata atamfa ƴar côte d'ivoire na zaɓa mata,da murna ta shiga shirya wa.
Na dubeta na ce “Yanzu za ki tafi gaishe ta ɗin?”
“Eh mana ko ba ki son yau babu makaranta ba?”
“Don me?”
“Oh! Na manta ban sanar da ke ba,jiya kin yi saurin tafiya ne SG ya sanar ba a makaranta ko zaɓen mi za su yi”


Jin haka yasa na yi kwanciyata ina cewa “madallah dama a gajiye nake”
Heelat ta dube ni ta ce “aikin mi kika yi?”
Sai na ƙyalƙyace da dariya ina tuna moments ɗin mu na jiya ni da Alhaji ,sai na ce mata “babu komai! Hafiz ɗin shi zai zo ya ɗauke ki ko yaya?”
“Eh haka ya ce,ya na ma gidan su Sadiq ,na manta ma ban tambaye ki ba ya jikin nasa?”
“Jikin wa?”
“Sadiq mana! Ba dai ba ki san bai da lafiya ba?” Heelat ta tambaye ni.
“Bai faɗa min ba” na bata amsa.
“Kuma fa ke ce sila! Duk a son ki ne,Sadiq na bala'in kishin ki.”
Na taɓe baki na ce “mene ne amfanin soyayyar tunda ko sisi bai da ballantana a yi zancen aure”


Heelat ta ce “ko Hafiz fa Daddynsa ne ya biya komai amma ai shi ma bai da ko sisin ”
“To shi nasa mahaifin ya mutu,bai bar masa komai ba sai wani guntun gidan laka ” na faɗa ina mai fara daddana wayata.


Dariya Heelat ta yi sosai bisanin ta ce “wlh Meelat ba ki da mutumci,shi gida har da guntu ke da kwai? ”
“I ba ki da labari?”
“Ko ma dai mene ai guntun gatarinka ya fi sari ka bani”


“Kar ki ɗora min ciwon please,bari na hau facebook na ga wace wainar ake toyawa a can” na faɗa tare da shiga yanar gizozo,yayin da kuma Heelat ke ta ƙoƙarin ganin ta yi kyau sosai.




Uwanda suka turo min saƙon ƙawance na fara mayar wa sama da mutum ashirin kuma duk maza ne.Kamar jira suke mu ka fara masayar kalma,a ƙarshe kuma wasu cikinsu suka tambaye ni lambar da nake WhatsApp na kuwa basu.
Sosai na shagala cikin wannan duniya,sai na ji muryar Heelat na cewa “zan tafi sai na dawo”
Na juyo ina watsa mata mugun kallo na ce “wa za ki bari yayi miki tsaron ɗaki? To tare za mu je Malama duk tsiyar ki yau sai na ci abincin gidansu Hafiz ”


Kai ta girgiza ta ce “mai hali dai bai fasa halinsa! Tun farko na so na tambaye ki ko za ki yi min rakiya,to sanin halin ki ya saka ban furta ba”
Na yi ƴar dariya ina mai maida wayata a jaka na ce “to mu tafi”
Mu ka fito ta rufe ɗaki kafin mu fita,gidan baya na zauna ita kuma ta shiga gaba.


Har mu ka kai gidan Hafiz hirar Sadiq ce yake min,akan na tausaya wa abokinsa na so shi kamar yadda shi ma yake sona kar na ci amanar ƙauna.Heelat ma ta daddage ta na kama masa sai goyon bayan Sadiq suke,tun ban jin haushi har ya kai na yi banza da su ina mai duba sabon group ɗin da aka saka ni à WhatsApp wanda iya sunansa kawai za ka fahimci babu abin arziki a ciki.






Ina shiga kuwa na ga sai abubuwa maras kyawu ake turowa,na fito ina dariya a zuci na ce ‘ana hau duniya!’
Gidansu Hafiz mai kyau ne,tun daga waje har cikin gida.Shi yayi mana iso har ciki,mahaifiyarsa da ƙanensa su na zaune.Mu ka gaishe su sannan mu ka samu wuri mu ka zauna, Heelat sai wani sunne kai take.


Mahaifiyarsa babu ruwanta don irin ƴan bokon nan ne,haka ta yi ta jan mu da hira bisanin ƙanwarsa ɗaya ta kawo mana ruwa da jus da kuma yankarkar ayaba,da gwada.
Ɗayar kuma abinci ta kawo cikin kwononin madubi don ka na iya hango lakaɗeɗen kifin da ke bacci a gashe abinsa.


Tashi suka yi suka bamu wuri,hatta Hafiz ɗin wanda kafin ya tafi ya ce “ku ci ku ƙoshi nan fa gidan ku ne”
A zuci na ce ‘kar ma ka yi ɓarnar bakinka don ko ba ka ce ba sai na yi narrr ’


“Wlh ni kunya nake ji,don Allah Meelat kar mu nuna ƙauyanci mu ci kaɗan ” Heelat ta faɗa ta na ɗaukar ayaba.
Na jefe ta da mugun kallo na ce “dalla can malam! Ga abincin sai na zauna da yunwa eh lalle!” ai kuwa na buɗe kifin da tun da aka aje shi yawuna suka tsinke plate na ɗauka na zuba acake da sauran kayan haɗin.




Kamar ƙaton da ya dawo daga gona haka na zuba na ci na ƙoshi, Heelat kuwa sai tsakura take ita ala dole ta zo ta zo gidan surukai.
Na dube ta da kyau na ce “kin ga Malama ki saki jiki ki ci abincin ki don dai in sun fito ba za su gane kaɗan kika ci ba”
“Na fa ma ƙoshi” ta faɗa ta na cire hannunta ta saka sabulu ta wanke hannunta a ruwan da aka kawo cikin wani kwano.




Don wulaƙanci sai ta koma gefe ta na danna waya,ni kuwa ban damu ba bayan na gama ci na fara shan kayan marmarin na ɗora da ruwa.
Sai a lokacin ƴar aikinsu ta zo ta kwashe kayan,Hafiz ya dawo ya mai cewa “ku taso ku duba kayan” ba tare da sanin kayan mi ba mu ka bi bayansa.
Wani ɗaki mu ka shiga mai shegen kyau sai ƙamshi ke tashi,tozali na yi da akwatinan aure kusan shidda ko wace a buɗe take da kuma kaya a ciki .




Ba ƙaramin ƙoƙari na yi ba wurin haɗiye abin da na ji ya zo min a maƙogoro .‘Wato dai Heelat aure za ta yi ta bar ni alhalin ko can a ƙauye ita ke kore min samari ta na aibatasu don duk kar ni na yi na bar ta,shi ne yanzu za ta ci amanata?’ na yi zancen zucin.


Dakyar na cira ƙafata na matsa na fara duba akwatinan,less,atamfa da duk wasu abubuwan da ake sawa cikin lefe hatta kayan bacci da bra da pant duk an saka.Turare da man shafawa trollynsu daban ta musamman.
Sarƙa da ɗan kunnai kuwa ba a magana sai ƙyalli suke.
Hafiz sai faɗa yake ya na ƙarawa “in da akwai abin da babu ku faɗa,don ina ga yau za a kai kayan ”


“Meelat komai yayi ko?” Heelat ta tambaye ni ta na min wani murmushi mai cike da ma'anoni,a cikin kallonta zan iya hango irin na yi miki zarra na wuce ajin ki.
“Duk sun yi Allah sa alkhairi ” na faɗa ina murmushin yaƙe.
“Amen! Shi yasa nake son yanzu na kai ku can Takalmawa tun da gobe ma babu makaranta sai ku yi shagalin taya murna ku da sauran ƙawayen ku”




“Tunanina da na ka sun zo ɗaya Habibi , Meelat ai za ki tafi ko?” ta dube ni ta na tambayata.
Na ce “a'a zan yi Bashir magana sai mu tafi tare”
“Wane Bashir kuma?” Hafiz ya tambaya ya na turniƙe fuska.
Na yi ƴar dariya ina mai danna wayata na shiga yi wa Bashir ɗin text babu jimawa ya kira,na yi saurin fitowa don sosai nake jin zuciyata na zafi in ina ganin trollyn nan.




Bayani na yi masa a ɗan takaice,ya shaida min ga shi nan zuwa.Tsabar takaici a waje na fita ina jiransa tun da an yi katari ya na kusan unguwar.Ina nan tsaye na tsinkayi motar shi daga nesa,idona har rufewa suke na soma tafiya direction

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login