Showing 30001 words to 33000 words out of 36805 words
Chapter 11 - Rainon Soja Book 3 Complete Hausa Novel By Maman Teddy .txt
lumshe ido tare da Sauke Irin numfashi.....Ashhh! Ohh!! Ma'eesha please please Ma'eesha ki buɗe mun na shiga Ashhhh!!! Ohhhh yana maganan Muryar sa na rawa haka jikin sa . Goga Shakiran sa yake yi yana ɗan jijjigata tare da dannata ciki .....Wani irin zafi ne yake ziyartan ta , amma duk raki irin nata sai ta dake , don tayi Alƙawarin ko da Uncle kashe ta zaiyi ba zata taɓa bujire masa akan abin da yake so ba a yanzu har zuwa ƙarshen Rayuwar ta.
[1/31, 5:12 AM] Real~Mamanteddy: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
80-81
*Littafin na kuɗi ne please don Allah kar ki karanta indai baki biya ba . Regular payment₦500 Vip payment₦1000 SPC payment₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 idan Vtu transfer ne sai ki tura ta wannan number 09061466409....✍🏻🤍#Mamanteddy#mrsusm.*
Book 3
Duk da Raɗaɗin na shigar ta sosai , amma sai saka hannu tayi tana ƙanƙane filon da take ƙwance a kai , tana rufe idanun ta dake tsiyayar da Hawayen azaba . Sambatun sa take ji da ihun sa yana Wasu irin zantuka wanda bata fahimta . Wani irin buɗata yake yi , tana jin yanda yake Yi kaman yana yagayaga da ita. A halin yanzu ko da ma tace zata yi kukan da ƙarfi don ta dakatar dashi bata da wannan ƙarfin iyawar . A hankali take kiran sunan sa “ Uncle... Uncle zafi zan mutu Uncle Zafi.... Mami ki taimake Ni Uncle ka cece Ni Ka bar Ni na huta...... Ɗaukewa maganan nata yayi sakamakon wani wuri da taji ya shigar da buran sa yana yi kamar balloon luɓuss kawai dai ita duhu duhu take gani ....tun daga nan bata sake sanin inda kan ta yake ba .
**
Hajiya Falmata kece yau da kan ki ? A'a lallai yau aiki kamin ki koma an yi shi kamar yankar wuƙa an wuce wurin .....Bokan Hajiya Falmata ya furta yana Wani karkacewa . Wani irin dariya Hajiya Falmata ta fashe dashi tana Girgiza kai tare da cewa “ Shiyasa bana jin haufi ko nawa ne a aikin ka , Saboda abin ka faɗa ne da cikawa. Ƙwarai kuwa ya furta yana wani zare idanun sa da suka sha Tazali har kusan hanci ga wani ɗige ɗige mai ban tsoro . Idanun sa jajaye ga su a warwaje yana ƙara fiddo su . Yanzu me ke tafe dake ? . Gyara zama Hajiya Falmata tayi kana tace “ So nake kowa ya rasa! Wato a yau A kashe Alhaji Adamu, wannan doguwar sumar da yayi kar ya farfaɗo a duniya sai dai A lahira. Hehehehehe!!!🤣 . Bokan ya saki Wani irin dariya mai amo da rikita hazo . Faɗa da cikawa . Ya furta yana miƙa mata Wani Abu a ƙoƙo kana yace kiyi maza ki riƙe shi da kulawa don wannan rayuwar Adamu ne . Kar ki bari ya buɗe a lokacin da kike zaune ko ƙwance, saboda idan ya zube kece taki ran zaiyi halin sa . Idan kin koma a tsaye zaki zubar dashi , to tabbas shi da miƙewa sai kuma a ƙiyama ”.
Jiki na Rawa Hajiya Falmata ta amsa tana saurin miƙa tsaye tare da cewa “ Godiya nake boka , sai na dawo akan suma lamarin sauran kishiyoyina ”. Tana maganan tana tura masa rafa rafa biyu na kudin da ta kawo masa kamin tayi saurin nufar moton ta tana shigewa cikin wani irin mahaukacin gudu. Gaba ɗaya ta ƙosa taje ta aiwatar da abin da Boka ya faɗa........A dai dai Wani round about ne tazo zagaye kiffffff😲 Ƙoƙon ya kife. Innalillahi wa'inna ilaihir......kamin ta ƙare tuni sitiyarin ya ƙwace mata moton na wani irin majajjawa da ita..... ji kake ƙuuuuuuiiii kawai sai ya daki wannan round about ɗin yana karuwa da Wata babban moto da ta kunno kai .
Kun san me ake ce ma rugu rugu nuƙurƙusu shi moton Hajiya Falmata yayi wanda kowa da gani sai dai ace Allah ya jiƙan Musulmi .
**
A hankali yake sauke numfashi don yafi mintuna Goma yana sauke nishi kana ya miƙe yana Rungumo ta jikin sa , bin kyaƙyƙyawar fuskar ta yake yi da kallo inda idanun ta suke a rufe , alamun suma tayi kuma Bata farfaɗo ba . Ƙurrrr yayi mata yana tuno da Wasu abubuwa na cikin rayuwar su . Fuskar ta ya tuno a lokacin da bata fi shekara ɗaya ba kwance kamar haka a saman cinyarsa . Wasu irin Ƙwallah ne yaji suna zubo masa Wanda ya bai san dalilin zuwan su ba . Kawai abin da zai iya cewa shine ya mutu a kan ta💔 . Ruwan Hawayennsa dake ɗiga bisa kuncinta ne yayi nasarar fara saukewar Numfashin ta , a hankali take ware idanun ta , shi bai lura ba ma , don gaba ɗaya ya rasa mene zai yi mata . Ba abun da yake tunawa da ya wuce lokacin baya , yanda yake saɓata a wuya , wurin exercise training....Da lokacin da idan ana mata karatu a aji zai saka duka ɗalibai suyi barci yana dakatar da Malama daga karatun da take yi wai sai Ma'eesha tayi barci ya gama kuma kowa yayi shiru kar a dame ta . Yau gashi yasa Ma'eesha ta suma😯ko yaya kenan?🤣 . Kafesa tayi da ido tana ganin yanda yake zubda ƙwallah abun da bata taɓa gani ba . Zafi take ji amma sai ta daure tana motsa bakin ta cikin wani irin Sanyayyar Muryar ta ta kira sunan sa “ Uncle! . Saurin kallon ta Haidar yayi kana ya fara kame kame ya rasa me zai ce mata , haƙurin ma bai san wani iri zai bata ba . Wani irin Murmushin ƙarfin hali tayi tana cigaba da cewa “ A tunanin ka na mutu ne kake kuka? , Lumshe idanun sa yayi yana bin ta da wani irin kallo mai ɗauke da narkakkiyar so mara iyaka . Ƙara sakin masa murmushi tayi kana tace “ A'a Uncle zamu rayu tare ,babu inda zan tafi na Barka , kuma sannan ma Ai ba Zafi banji ba sam”. Hannun sa Aliyu yasa yana Saurin Rungumo ta tare da mannata da ƙirjinsa , Wasu irin jaruman Ƙwallah ke zuba masa Cikin Muryar sa wanda a yanzu tayi rauni yake furta “ Ina sonki Ma'eesha, Ina sonki matata! Kiyi Haƙuri n.......Rufe masa baki tayi da hannun tana komawa lamo tare da ƙwanciya ”. Kusan mintuna uku kamin ya ɗauketa yana nufar Toilet da ita .....!
**
Kallon General Saleh Mom Hajara tayi kana tace Wai Ni meke faruwa ne ? Kawai ka ɗauko mu ka kawo mu Asibiti ka faɗa mana Menene ya faru don Allah Janar, kar sai munje hankalin mu kuma ya tashi. Buɗe ƙofan da Alhaji Adamu yake ciki soja daya yayi , yayin da Mami Jidddr Khalil da Mom Hajara suka shiga zuwa Ɗakin . Zaune suka ga Hajiya kaka tana riƙe da cazbihan ta , kallo ɗaya zaka yi mata ka fahimci tana cikin jimami .
Ba tare da Mom Hajara ta lura da Alhaji Adamu ba , Ita dai ganin Hajjiya yasa ta saurin nufar ta tana furta “ Hajiya lafiya? Me ya kawo ki nan? Wani.......A'a Lafiya na qlau , mijinki yasa na zo nan! Mijina? Mom Hajara ta furta tana saurin juyawa tare da kallon mutanen wurin , idanun ta ne suka sauka akan gadon Alhaji Adamu inda ta tsaya suuiiiii tana sakin jakarta da Wayoyin ta anan ....A hankali kan ta ke juya mata , Tana bin sa da Kallo tare da tunano Rabuwar su ta ƙarshe......Ƙaran hatsarin na dawo mata tare da ihun jama'ar cikin moton , Kukan yarinyar nata shine yake dawo mata , Wanda cikin sauri ganin tana baya Nurses da Mami suka taro ta. Cikin wani irin Muryar tashin hankali take kiran sunan ɗiyar nata “ ZAHRA! Ina Zahra ta take? Zahraaaaaa!!!! Luuuuuuu tayi tana zubewa babu alamar rai bare.......!
[1/31, 5:39 AM] Real~Mamanteddy: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
82-83
*Littafin na kuɗi ne please don Allah kar ki karanta indai baki biya ba . Regular payment₦500 Vip payment₦1000 SPC payment₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 idan Vtu transfer ne sai ki tura ta wannan number 09061466409....✍🏻🤍#Mamanteddy#mrsusm.*
Book 3
Hankulan su ne duka ya tashi musamman Alhaji Adamu wanda shi ma a yanzu komai ya dawo masa Tamkar yanzu ya faru . Allahu Akbar! To wai shin Meye labarin Dake tsakanin Hajiya Hajara da Alhaji Adamu ?. Muje zuwa 💃🏻 Saurin Nufa da Mom Hajara ɗakin taimakon gaggawa aka yi , inda Kamin wani lokaci tuni dangin Alhaji Adamu na ƙauyen Fallanki sun fara isowa , Abun ka ga Ƴan ƙauye suna samun labarin Bayyanar sa , A ranar suka yo ɗauko hanya . Ganin yanda ya zama Alhaji Abin yafi basu tsoro . Musamman a da baya da suka san shi a almajiri , Almajiranci ya kawo sa birni .....Tuna baya!
(A salin Alhaji Adamu)
Alhaji Adamu Sunan sa Wanda aka yanka masa Salihu ne , Ɗan wani ƙaramar ƙauye da ake kiran ta Fallanki , Ƙauyen karama ce sannann ba mutane da yawa , Asali ma duka dangi ne yan uwa . Almajiranci ne ya kawo Alhaji Adamu Birni inda ya wahala sosai , Daga baya Allah ya taimake shi ya fara Aiki a cikin gidan Hajiya kaka , Wato Gidansu mami da Mom Hajara . Shine mai yanke fulawowi da Wankin takalmar su . Wannan shine aikin sa tsawon lokaci a cikin gidan . Hajara macace ita tun tana yarinya masifaffiya ƴar tijara ce bata da kirki , idan kaji an yi sallama a cikin gidan to itace ta Kori mutum . Kowa tsoron ta yake ji ƙwarai , don ko zuwan Alhaji Adamu Bai san ta ba , don bata ƙasar tana ƙasar Spain don kammaluwar karatun ta .
Dawowan ta ya wahala ta tattaka shi babu iyaka, tsanar duniya tayi masa , ga Wahala , amma a haka Adamu yake haƙuri tsawon lokaci , don ko a lokacin Mami da Auren ta da General Saleh . Kasantuwar itama mami ba mazauniya bane saboda yanayin Aikin ta na police yasa ko ƴaƴan ta Hajara ba sani tayi ba , haka suma sai dai suji sunan ta . Rabon ta da Mami tun haihuwar Haidar a wannan lokacin kuwa da ta dawo da cikin Jidder. Taso ta koma Spain amma Hajiya tace A'a , sai mami ta haihu daga baya sai ta koma .
A haka Rayuwa ya cigaba kowa yasan Yanda Hajara ta tsani mai aikin nata , Haka Mami ta haihu Hajara wulaƙanci ko ganin jariri ba taje bare suna . Kai daga karshe Daddy ne ya dauki Khalil ya kawo mata , a lokacin Ali baya jin dadi wannan yasa shi bai samu ganin Mom Hajara ba sai dai a hoto . Da kuma yanda ya santa tun yana ƙarami sosai .
Abun da ya faru wanda ya jijjiga a halin shine a dare daya lokaci guda Hajara ta nuna ita tana ra'ayin Alhaji Adamu, don tun da take bata taɓa ganin mutum mai haƙurin sa ba. Tun tana musguna masa ɗan ƙauye Almajiri jahili kawai daga haka sai kuma tausayin shi ya fara shigar Zuciyar ta . Tun tana daurewa ta gaji ta bayyana ma iyayen nata. Inda anan kowa ya daka ƙafan da cewa “ Ai Asiri Alhaji Adamu yayi mata ”. Horo azaba babu wanda bai gani ba , amma nan tafa ce ita shi take ra'ayi, ai ita zata zauna dashi ba wani ba.
Bala'i da yayi Bala'i , a wani dare ta tarkata ta je inda aka rufe shi ta gudu da ita dashi , suka nufi ƙauyen su na Fallanki , a takaice acen aka daura masu Aure , har suka Haifi Yarinyar su Zahra , idan kaga Mom Hajara a wannan rayuwar ƙauyen sai kayi mata hawaye ,amma a haka ta share ta manta da komai , don a lokacin cewa tayi kowa ma da yake son ta ,saboda iyayen ta ne , a i yanzu babu mai yin son tsakani da Allah . Ta sha wuya gaba ɗaya ta sauya har kamannin ta . idan mun tuna a shafin Farko , sun shirya ne don zuwa dangin Hajara , Don Alhaji Adamu ya bada haƙuri sai kuma Allah yayi ikon sa , ashe haɗuwar da Sauran lokaci sai a yanzu ”.
**
Murmushi yake yi mata tare da cewa“ Buɗe bakin , a hankali Ma'eesha ta buɗe bakin ta yana bata fruit ɗin , Yana murmushi . Ƙwanciya tayi a jikin sa tana lumshe idanun ta dai dai Ƙofar su na ƙara alamar Door bell . Saurin juyawa Ma'eesha tayi , inda cikin sauri ta miƙe daga jikin sa tana bin mai shigowar da kallo . Nurse Narret ta furta cikin wani irin murya ”. Kallon Ma'eesha Aliyu yayi kana ya kalli inda Narret ke shigowa da Akwati a hannu tana jaaaaaaa😯!
*Mmnteddy 08081202932.*
[1/31, 6:15 AM] Real~Mamanteddy: *🕊️RAINON SOJA🕊️*
*Through the gate of love a valiant fearless heroical and Sympathetic Story.*
84-85
*Littafin na kuɗi ne please don Allah kar ki karanta indai baki biya ba . Regular payment₦500 Vip payment₦1000 SPC payment₦1500 via 6037312299 mohammed Aisha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932 idan Vtu transfer ne sai ki tura ta wannan number 09061466409....✍🏻🤍#Mamanteddy#mrsusm.*
Book 3
Haɗe giran nan nasa yayi yana murtiƙe fuska tamkar wanda bai taɓa dariya ba . Don tuni yasan labarin Narret duka kallon ta yake yi , don ƙawarta ta sanar dashi komai har ta ƙaryar ciwon ma'eeshan . Miƙewa Aliyu yayi yana raba jikin sa da Ma'eesha kana ya kalli Narret dake bin su duka da Kallo na cikakkun yan duniya tana kallon Ma'eesha ƙasa ƙasa . Me ya kawo ki gidana? . Ya furta cikin dakakkiyar Muryar sa.
Murmushi Narret tayi kana tace “ Fatan kaga tayin soyayya ta ”.
Na gani sai aka yi yaya? Fice mun daga gida bana son sake ganin ki a rayuwata dana iyalina . Wani irin Abu Narret ta haɗiye kana ta Girgiza kai tana kallon Ma'eesha wacce itama ita take kallo jiki a sanyaye,don ta tuno da Alƙawarin da tayi ma Narret.
Murmushi Narret tayi tana ƙare mawa ma'eesha kallo kana cikin Wani irin murya ta fara magana da cewa “ Allah Sarki Yarinya! Gaki kyaƙyƙyawa tabbas ke matace ta nuna ma Sa'a . Amma ki sani ba zai yiwu Miki ki zauna ki sance tasa har abada ba. Saboda masu so da yawa dole ki dan matsa wasu su shigo! Takawa tayi tana juyi a tsakiyar falon kana ta cigaba da cewa “ A wancen lokacin da kin fada mun duka a layi ɗaya muke ai da ban azabtar da Zuciyar ki wurin faɗa mata irin Soyayyar da nake mawa abun da kuke so da hari ba ...amma ko a yanzu ba abun damuwa bane , a namiji mijin mace huɗu ne ....yanzu nazo ne a bani ɗaki, kamin na shigo a na biyu ko uku ko huɗu ....ke idan ma babu Wuri to zai sake ki ya Aure Ni......Kamin ta rufe baki Ita dai taji saukar marine mai tartsatsin wutaaaa “...tasssss”.
Wani irin tsorata Ma'eesha tayi ganin lokaci guda ya koma mata Aliyun da baya . Narret kuwa dauke gani tayi na sakanni kana ta furta “ Mari na kayi ?”. Yessss! Na mareki komai ma zan iya Miki Indai bakin ki ya cigaba da furta kalmar cewa “ na rabu da Ma'eesha, daga yau kar Na sake ganin fuskar ki idan ba haka ba Wallahi sai na karairaya Miki ƙafa🫨 ”. Juyawa Ma'eesha tayi da sauri tana ƙoƙarin Guduwa jikin ta na rawa , carafff taji ya riƙota yana Haɗata da jikin sa tare da Rungume ta yana shafa bayan ta a gaban narret wacce ta kusa haɗiye ranta don baƙin ciki . Ita Rayuwata ce! Fice ki bani wuri. Ya furta yana haɗe giran sama da ƙasa. Fuskar sa na huci . Ganin a tsume yake ya saka Narret saurin juyawa tana furta “ Wallahi ba zan bar ku ba da kai da ita duka zaku gani...”
Kallon Aliyu ma'eesha tayi hawaye na ciko ƙwarmin idanun ta. Uncle Zan koma gida ”.
Gida!
Ai ke kuma da su Mami sai dai ziyara, wani gidan bayan gaki a gidan mijinki . Ƙwanan nan zamu wuce Ƙasar Oustralia ina tunanin zan kwana biyu acan, amma anan zaki zauna ba zaki koma gidan Daddy ba . Ya furta yana kissing ɗin bayan ta. Shiru tayi tana kasa ce masa komai , don ita gani tayi al'amarin narret ko a jikin sa . Mtswww!!! Wai to Ni sai aka yi yaya? Ya furta yana ƙara wayar A kunnen sa tare da Sauraren Maganan da Khalil ke faɗa masa na Dawowan Mijin Mom Hajara .
Alhamdulillah ”. Ali ya furta kana ya datse kiran ya na kallon Ma'eesha tare da cewa “ Kinji an ga mijin Mom Hajara, alhmdlh kin ga yanzu inshallah zata sakar mana mara muyi fitsari, zata yi laushi ,don naji labarin yanda take mugun Masifar son mijin nan nata . Kallon shi Ma'eesha tayi kana tace “ Ɓata yayi ne dama ?. Gyaɗa mata kai Ali yayi kana yace mu zauna na baki labarin Wacece Mom Hajara da Auren ta da Mai Mata wankin takalmi da yankar fulawa. Ni fa soyayyar naga bugeni yayi ,wannan shine definition of true love 🥰 kaman dai soyayyar mu kennn! Aliyu ya furta yana murmushi Hushiryar sa na bayyana ”.
**
Shiru duka aka yi a falon Hajiya kaka , Dangin Alhaji Adamu, dangin Mom Hajara duka zaune ana kaji yawa. To Alhamdulillah Allah kenan mai yanda yaso , yau gashi Wai Hajara ce Da Adamu aka ƙara haɗuwa. Itama yarinyar Allah zai bayyana ta! Hajiya kaka ta