Showing 27001 words to 30000 words out of 48742 words
Chapter 10 - INA ZAN GANSHI Complete Book By Xahra Bukar.txt
motar wuta yayi gaba.
Yak'en da yafi kuka ciwo tayi hade da sa hannu tadau kudin da tuni ya fad'i k'asa, jinjina kai tayi, tana xancen zuci, ko mi yay mata bataga laifin sa ba ita ta jama kanta, asalima sonshi ba raguwa yayi a xuciyan taba idan ma ya dawo gareta hannu bibbiyu xata amshe sa, saidai ayadda taga fuskar sa she doesn't tink xai k'ara waiwayanta, kuka sosai take tana consoling kanta, tasan Mamuda nada kirki da kyakyawan zuciya baxai share taba, he will definitely come for her.
Hope sosai tayi ta bawa kanta, taxi ta samu ya dawo da ita gidan sanna ta biyasa da dari biyar din.
Marwa tagani tsaye gaban gidan, yana zuba yan tarkace a gidan baya, da azama ta shige gidan sanin cewan tarkacan Inna ne.
Tsaye taga Inna bakin kofa tana kokarin datsewa da k'wado, dan ihu mai tattare da tashin hankali tayi tana fadin
"Inna karki tafi ki barni"
Sai sannan Inna ta ankara da ita, sosai Batul ta bata tausayin sakamakon fita hayayyacinta da taga tayi.
"Batula kin dawo ashe" Inna ta fadi hade da zare mukillin k'wadon.
Karasawa gabanta Batul tayi ta tsugunna, cikin kuka tace "inna dan Allah ki zauna dani, bansan ina xan nufa ba, Mamuda ya sakeni ko kuma ince RMd ya sakeni dan nasan kinsan komai"
Dagota Inna tayi tanai kallonta.
"Batula laifin kini ai, kwanaki ba yadda ban rokeki karki tafi ba kikayi kunnan uwar shegu kika kara gaba, inda ace kin tsaya da Rasheed bai sake kiba, aranar yaso bayyana maki kansan amma ke kika tafi nuna mai kanki"
Sosai take kukan tace, "nasan na tafka babban kuskure, amma Inna ai bai kamata ya sakeni ba kodan son dana kemai"
Goge mata hawayan Inna tayi.
"Kidaina kuka, Allah yasa sakin yafi alheri, yanxu
Ki dau kayanki ki koma gidan ku"
Kai ta girgiza, "Inna tsoro nakeji bazan iya komawa gida ba, ki temaka ki zauna dani kafin wasu kwanaki saina koma gida inyaso muje tare ki tayani bawa Baba da Hajjo hakuri"
Ajiyar zuciya Inna ta sauke tace "kinga ni baa garin nan nake ba, Jikana ne abokin rasheed shiya kawoni nazauna dake na dan wasu lokuta, yanxu kuwa gida xan koma Zaria na cigaba da sana'ata shiyasa kika ga na dawo daukan sauran tarkace na"
Kyankyame Inna tayi tana rokonta, "dan Allah kije dani Zaria, ko talla ce xan miki, Inna ki temaka.." Karashe maganar tayi cikin matsananci kuka.
Ba karamin tausayinta Inna taji ba, tace mata ta dauko kayanta su tafi, cikin rawar jiki Batul ta fada daki ta warb'o ghanar ta fito sukayi waje, Marwan suka shiga yajasu zuwa tashar kawo suka shiga motar Zaria.
*Kauyen Marke*
Jigawa state.
Zaune Hajjo take a tsakar gidan su mai zagaye da kara masu kauri, Rike take da rariya tana tankadar garin masara. Shigowa baba yayi yanai wa su Hassan nuni da inda zasu ajiye buhun albasar dake lafce bisa bayansu, ajiyewa sukai hade da sauke numfashi.
Zama Baba yayi bisa tabarma dake shimfud'e, Hajjo tamai sannu hade da mikewa bakin randa dibo mai ruwa.
"Noma akwai dadi, kaman karmu koma Kaduna" Hussaini ya fadi yana zama kan tabarmar.
Hassan dake tsaye yace "nikam na matsu mu koma naga Batula"
Guntun tsaki Hussaini yayi.
"Batula ta manta mu, tunda tayi aure bata kira kosau daya ba, gashi ita layinta baa samu, na tabbata arziki tayi ta yashe mu"
Kwafa baba yayi yace "banason gulma, ku tashi ku bani waje".
Tsum suka mike suka fice, takaici ne yakama Hussaini, ya dade da lura duk cikinsu Baba yafi son Batul, sau da dama tayi laifi baya hukuntata saiko Hajjo ta mata duka amma su abu kadan yahau masu fada, shiyasa sam Jinin su bai hadu da itaba dan kuwa bayason raini dukda ita din yayar shice.
Ruwan Hajjo ta mikamai ta zauna tanai kara mai sannu.
"Ka sanar da Mamuda batun fasa tafiyar ? Acewar Hajjo.
Wayar aljihunsa ya ciro yana fadin "zuwa gobe dai xan kirasa yanxu wayar ba caji".
Numfasawa Hajjo tayi tace, "na yaba da hankalin yaron sosai, saidai halin Batul nake tsoro, Allah yasa tana kyautatamai"
"Karki damu, Insha Allahu lafiya suke".
"Allah yasa" ta fadi,
Hira su cigaba dayi cikin kwanciyar hankali.
****
Kaduna.
Aiki sosai yayi a office, bayan yayi sallah isha ya nufi hanyar gida.
Cikin shirin atampa riga da skirt tayi, fitowa tayi daga dakinta da niyya sauka kasa taji tashin zuciya, da azama ta ruga toilet, wani mugun amai yaxo mata tahau kwararawa, dogon numfashi ta sauke bayan tagama ta wanke baki ta fito, bakin mirror ta nufa ta kara shafa powder sannan ta sauko kasa.
Mom ta iske zaune parlour tana shan fruit,
Kallon ta tayi sannan ta zauna tace
"Mom yaushe kika dawo " ta fadi in state of confusion tana kura mata idanu.
Guntun tsaki Mom taja bata tanka taba, zama Mardiyya tayi tana tunanin tambayar danai mata can kuma tace
"Mom har yanxu fa princess bata dawo ba
Takaici ne yakama ta, magana xatayi ya shigo palon hade da sallama, jacket suit dinsa rike a hannu.
Mardiyya ce ta amsa fuska dauke da fara'ara tanai mai sannu da zuwa, mikewa tayi zuwa kitchen dauko mai abun sha.
Zama yayi kan doguwar kujerar da mom ke zaune, gaidata ta yayi ta amsa ciki ciki.
"Ina fatan bakaje bibiyar matsiyaciyar yarinyan nan ba" ta fada tana kallonsa.
Amsar ruwan da mardiyya ta mike mai yayi ta koma ta zauna.
Kai ya girgiza yana kallon Mom yace "nasan bakya kaunar ta, pls Mom kibar kiranta da matsiyaciya, she was once your daughter inlaw but not any more"
Tashin hankali ne ya durar mata, cike da kidima tace "Bangane ba, inlaw as how.
Maida da dubansa yayi bisa Tv dake kunne yace "ex wife ditace"
Zabure wa Mom tay tsaye, cikin rawar jiki ta kwashe sa da gigitancen mari da saida Mardiyya ta kwalla ihu tsabar firgita.
"Abdulrasheed ni zaka rainawa hankali, da izimin ubanwa ka aureta.." Cikin huci mom tayi magana.
Ransa ya bacci matika, saidai bazai tsaya yi mata bayanin sanadin auran ba, dukda ba son Batul yake ba bazai fadi masu halinta da dalilin zuwanta gidan nan ba.
murya mai dauke da bacin rai yace "it doesnt matter tunda nariga na saketa" mikewa yayi yahaura sama ba tare daya tsaya jiran abunda zata ceba.
Rai bace Mom ta zauna tana huci, yaushen hakan ta faru bata da matsaniya, lailai kuwa Rasheed yayi betraying soyayyar da takemai, kallon Mardiyya tayi dako ajikinta saima remote dake hannuta tana canxa channel.
"Waike wace irin dabbace, kinaji ya maki kishiya bada saninki ba amma ko ajikin ki" Mom tafadi cikin tsananin baccin rai.
Ajiye remote din tayi ta dubeta sanan tace "Mom mi kikeso nayi, ihu da hauka dan kawai ya auri princess, d first time dana gansu tare nagane he truly loves her, shiyasa ban taba interfering da duk care da yake nuna mata ba"
Harara Mom takai mata tace "sai yau nagane bakya son d'ana kin aureshi ne dan kudin sa"
Murmushi Mardiyya tayi.
"Ko daya wlh, as far a good wife kuma maison mijinta dole nayi supporting abunda yakeso, koda ace zai dawo da princess i"ll support him.
Haushi da takaici ne suka cikata, miketa tayi hade da wurga mata pilo dake gurin tabar palon afusace.
Cikin rashin damuwa Mardiyya ta mike ta nufi kitchen, fridge ta bude ta dauko ice dake leda ta fito ta haura sama.
Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga, zaune yake kan gado kansa dafe bisa hannusa, zama tayi kusa garesa hade da janye hannusa, dagowa yayi duban ta da idanuwan sa da suka sauya launi.
"Sweetie kayi hakuri" ta fadi tanai dumama mai gurin marin da ice, shuru kadai yayi ya kwanto da kansa bisa kafadarta haunta daya na shafar mai baya.
***
Washe gari daya tashi hankalinsa gabadaya yayi gurin Batul, ko breakfast bai ba ya wuce gidan, wayam yagani bata gidan kuma babu jakar kayanta.
Hankali tashe ya fito yana tunanin ko su Baba sun iso ne ta koma can gidan da sassafe, da axama ya fada motan ya nufi gidan Baba nan ba basu dawo ba.
Wayarsa ya fiddo yayi dailing no din Baba, buga daya ya dauko.
Aladabce ya gaidasa.
Baba ya amsa da fara'a
Shuru yayi yama rasa mai xaice, katse shuru Baba yayi da cewa "Mamuda kaji mu shuru ko, dawowar bata yuyuba sai nan da sati uku saboda aikin noma daya rikeni"
"Allah ya kaimu Baba" ya fadi cikin kokarin boye damuwarsa.
"Ya matar taka ? Baba ya tambaya.
"Kalau take" ya amsa agajarce.
Sun jima suna waya da Baba daga bisani sukayi sallama.
Iya kidima Rasheed yakai, tsoransa daya kar ace ta gudu wani gidan, number Daddy malam yahau trying, kusan sau biyu bizy, ana ukun ne yadauka.
Rasheed yace "wai dawa kake wayane kusan rabin awa"
Dariya yayi yace "inna ce fah, kasan jiya ta koma Zaria"
Guntun tsaki yaja.
"Miyasa Inna ta koma da kanta, naso ace nina maida ta Zaria dakai na".
"Kunfi kusa, saika kirata kamata ya hanya"
"Tukun nadai, nazo gidan banga Batul ba
Dariya daddy malam yayi yace , "why do you care, ta tafi gidan su kenan".
Bata rai Rasheed yayi yace "bata gidansu, so nake ka bincika min unguwan masu kudi ko Allah zaisa aganta sannan har kad poly ka je ka bincika min"
Dariya sosai Dady yake babbakawa, "toh kadai yace mai"
Rasheed ya katse wayan, can gidan da take ya koma ya zauna na kusan awanni biyar babu alamun ta.
Bayan kwana Uku
*Zaria*
Abinci dake gabanta ta matsar gefe tana sharar kwalla, rashin nemanta ba karamin ci mata zuciya yake ba, all her tot xai dawo gareta, amma shuru ko inuwarsa bata gani ba, kuka sosai ta fashe dashi, rashin zuwan sa kadai ya nuna mata both Rmd da Mamudan basu da good heart kuma ba santa suke ba, itace kadai take wahalar da kanta, share kwalla tayi ta mike tana alwashin yakace sonshi aranta, tunda har baixo ba he is dead to her, gwara kawai ta cireshi aranta dan samun nutsuwa.
Dakin Inna ta shiga ta sanyo Hijan ta fito gaban gidan inda Inna ke tuyar wainar, ga mutane da dama zagaye da ita suna jiran abasu.
"Inna kawo" ta fadi tana amshen ludayin hannuta,
Murmushi Inna ta sakar mata ganin yadda tayi maganar ba tare da kuka ba, tunda suka iso zaria bata da aiki saina kuka, asalima yauce rana ta farko data fito temakawa Inna, sabanin da saidai ta zauna gidin pampo tana kuka.
Sakar mata Inna tayi ta mike zuwa cikin gidan dauko miyar wainar, zuciya daya Batula ta dage da juya waina a tanda, tuni masu miko kudi suka fara tana zuba masu, wani matashi ne ya karaso gurin yana fadin "jikar mai waina sako min na dari" ba masu ta amsa mai hade da zuba mai.
Murmushi Inna tayi, tana daga gefe tana zuba miyar, mamaki sosai tayi da Batula bataji haushin sunan da yaron ya kirata dashi ba, sabanin ada saidai ta bisa da ashariyar an zubar mata da aji.
Babu inda Rasheed da Daddy Malam basu nufa ba babu labarinta, sosai hankalinsa ya tashi, duk wayar da sukayi da Inna bata taba cemai Batul na tare da ita ba, shima bai mata xancen ba yasan ba yadda xaai Batul taje gidilanta.
Sosai ya wahala ya gangara komawa gida.
Handbag dinta dake ajiye kan gado Mardiyya ta dauka, sanye take cikin doguwar abaya ta yane kanta da babban mayafi, gurin takalma ta nufa da niyya sanya heel sai kuma ta fasa sakamakon dan kumbura da kafafunta sukayi, flat tadau tasa, ta sauko ahankali tayi waje gurin motarta, shiga tayi taja ta fice daga gidan, motar Abbanta taga yayo kwanar unguwar, mamaki sosai tayi saida bazata iya komawa gidan ba sakamakon appointment da take dashi da Doctor a asibiti.
Jiki ba lak'a motarsa ta danno cikin gidan, parking yayi ya fito ya iske Motar Abba parke daga gefe, baiyi mamaki ba atunaninsa Mardiyya yazo gani.
Cusa kai yayi cikin palon, harxai haura sama ya jiyo muryar Mom da Abban Mardiyya daga can Guess Parlour.
Kaman xai wuce ya fasa, mamaki ne yakamasa, yasan Hajiya safara da Mom basu rabuwa da kuskus, yau kuma miya kawo mijinta gidan, karasawa yayi bakin kofar ya tsaya sauraran su.
"Alhaji nasha gayama ka rabu dani danba auranka xanyi ba, yama zaai ace na aurin mijin aminiyata bazai yuyuba" acewar Mom.
Nisawa yayi yace " amintakar ku ba hujja bace, gidanta daban naki daban"
Murmushin dabai kai xuci ba ta saki, ta lura dai yana son ballo mata ruwa.
"Bafa xan aure kaba" tafadi.
Magiya da rokonta yahau yi, Mom kuwa ta k'ule dashi, dan kuwa bai kai matsayin da zata aure saba, tafi karfin sa.
"Kai Alhaji ka bar batun auran nan, akwai igiyoyin aure akaina, kasa kuma baa aure kan aure".
Kallon rashin fahimta yayi mata yace "kina da aurene, yaushe kika sake aure, bayan mutuwan Baba Rasheed" atare ya jero mata tambayan.
Guntun tsaki taja cikin kagara da batun sa tace, "akwai Auran Baban rasheed a akaina
Ware idanu yayi
"Bangane ba, a aljanna ko a duniya, nasan mamaci baya dawo wa"
Afusace Mom ta mike tsaye
"Waikai baka da fahimta ne, nace ma auran Babban rasheed na rataye wiyana kuma yana nan da ransa bai mutu ba" cikin karaji ta karashe maganar.
"What" Abban Mardiyya da Rasheed suka fadi atare cikin zare idanu.
Karasa shigowa parlour Rasheed yayi yana kallon Mom da tuni tasha jinin jikinta.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar
®NWA
xarahbukar.wordpress.com
*Special greetings to IZG* *fans, thanks much for the* *love & Support, ILYSM*❤
*TeamDiyyah*❤
71
Daskarewa Rasheed yayi, tashin hankali da firgici shimfid'e bisa fuskar sa.
Shi kansa Alhaji Bello ware idanu yayi yana sauraran karin bayani, kallan wulakanci tamai sannan tace
"Alhaji ka fita idanu na, kaga adalilin nacin ka na furta abunda ba hakan bane, tunda kaki ganewa gwada nama b'aro b'aro, bana sonka dan Allah ka shafamin lapia".
Hular kansa yahau gyarawa yana fadin "Allah ya baki hakuri, kinga tafiya ta" ficewa yayi daga palon batare daya jira cewarta ba.
Ajiyar zuciya ta sauke ta maida dubanta ga Rasheed da itama kallonta yake
"My boy dont mind my words, haushi yaban yasa na furta hakan, babu wani aure akaina"
Cikin rashin gamsuwa da maganar yace "kince my Dad is alive"
Kwantar da Murya tayi tace "bakaji nace kawai fada nayi ba, believe me your Dad is dead".
Baice uffan ba ya fice parlour ba tare daya gamsu da abunda tace ba. Tunda har ta furtan hakan akwai kamshin gaskia ciki, idan ma koran Abba mardiyya take sonyi ai akwai oda strategies da zatayi using ba wannan ba.
Main palon ya k'arasa ya zauna yana tunanin wazai tuntuba da batun yadda mutuwar Babansa ta kasance, kawu Habibu ne ya fadomai arai, tabbas shi d'aya zai iya fayyace mai ko Babansa nada rai koya mutu, duk azuci yake xancan, dafe kai yayi, gabadaya duniyar tamai zafi, bai gama nutsuwa da b'atan Batul ba ga wata gagaruma Mom ta janyo mai.
Mikewa yayi da zama ya haura sama zuwa dakinsa. Freshen up ya shiga toilet yayi ya fito, ya shirya cikin kananun kaya, ya sauko kasa ya fice haraban gidan, motarsa yafada yaja zuwa home of hospitality (katsina).
Cikin sa'a ya iske kawu habibu gida bai fita ba, gaisawa sosai sukayi daganan ya zayyano mai xancen dayaji Mom ta fada.
Jinjina kai kawu Habibu yayi yace.
"Tabbas abunda ta fadi ta fade sane kawai dan wata manufarta, amma kam Baban ka ya dade da rasuwa, tunshi kuma bata sake aure ba"
D'aurewa kan Rasheed yayi da kalaman kawu, yakasa aminta da abunda suke fadi, shidai yasan akwai wata boyayyen al"amari dan jikinsa na fadi mai babansa na raye tunda Mom ta furta.
Nisawa yayi yace "kawu miye sanadin mutuwar sa, kunyi mai jana'iza ?
Girgiza kai yayi, yace
"Bana nan sanda ya rasu, ina Ghana karatu lokacin, bayan na dawo Maman ka kece min ya jima da rasuwa, nayi kuka rashin sa ba kadan ba, tsohonka akwai halin kirki da daddako"
"Allah yaji kanshi" Rasheed ya fadi asanyaye, saidai ayyada ya lura da xancen Kawu bai da matsaniya akan mutuwar Baba, same story da Mom tabasa shine wanda yasani, ba yadda ya iya dole ya nunawa kawu ya yadda da xancensa dan bazai iya mai masu ba.
Sun dade suna hira daga bisani yamai sallama ya kamo hanyar dawo wa Kaduna.
*Zaria*
8.26pm
Iya karfinta ta sanya tana wanke shinkafa wainar gobe, daga can gefe Inna ke zaune tana yankar alaiyaho.
"Ilimi akwai dadi, Inna nima dai xan shiga islamiyyar daran nan" Batul ta fada tana sauraran karatu dalibai dake tashin daga can islamiyar dake gaba dasu.
Inna tace "Islamiyar akwai karantarwa, babu wasa sam, yaro kadai xan tura ya karbo maki form ki ciki gobe ki fara zuwa'
Cikin jin dadi tace "nagode sosai Inna".
Yaro ya shigo hade da sallama, amsawa sukayi yace "Nafi'u mai shayi ke sallama da jikar mai waina, yana waje"
"Kai yaro koma kace bata fitowa" Inna ta fadi tanai zarowa yaro ido, tasan xaa rina sunga yar kyakyawa zasu fara damunta da k'wado sallama.
Dakatar da Yaro Batul tayi tace "kace mai gani nan"
Toh" yaro ya amsa ya fice.
Kallon Inna tayi tashe, "inna kiyi hakuri naje, kinsan shi dan adam komin yadda yake ba abun wulakantawa bane, wannan abu ya faru akaina, banaso tarihi ya kuma maimaita kansa.
Dariya Inna tayi, tace "gaskia ne, kije amma karki dade".
Hijabin ta dake lankaye kan igiyar shanya tadau tasa ta fice wajan gidan.
Tsaye ta iske shi, hannusa rike da bakar leda, jkinsa sanye da kodaddiyar tshirt da wando daga ganin wankan kure adaka yayi.
"Ina