Showing 39001 words to 42000 words out of 48742 words
Chapter 14 - INA ZAN GANSHI Complete Book By Xahra Bukar.txt
karasawa yayi inda yaga kayan a ajiye, Murmushi yayi, aranshi yana jin dadin yadda tasan taste dinsa,
Duk akan Idon Mardiyya, tasan sarai ya dauka Batul ce ta fiddo mai kayan, batace komai ba, taci gaba da adjusting pilo acikin case dinsa.
Shiryawa yayi tsaf cikin kayan, fita Palo xaiyi Mardiyya tayi saurin bin bayasan tana fadin "Sweetie kayi kyau sosai"..
Murmushi yake cikin jin dadi yace "Thank dear"
Kallo daya tayi masu ta tashi tabar palo, ta fita gurin Motar ta tsaya, wani irin haushi take ji na ba gaira ba
dalili.
Har bakin Motar Mardiyya ta rakosa tanai masu Allah ya kiyaye hanya.
Yaken dole Batul tayi tace "Sister Mardy saimun dawo" hade da fadawa cikin motar.
Amsata Mardiyya tayi fuskarta dauke da Murmushi, saida taga sunja sannan ta koma cikin gidan.
Tuki yake cikin hankalta da kwarewa harya iso Zaria, babu mai magana da junansu, kallonta yayi yaga yadda ta daure fuska, kumatun duk sun kumburo, kiris ya rage ta fashe da kuka, Dariya sosai tabashi, dakewa yayi yace "Princess kinfi kyau when you smile"
Bata kallesa tace
"Babu ruwanka dani"
Dariyar daya kasa barin aransa yahau yi, yace "yayanki kike cewa babu ruwank dashi ?
Ya gama kuleta ba kadan ba, ita tana kokarin boye sonshi aranta, amma shi kallon kanwa ta jini yake mata, bata iya basa amsa ba tace "gidan inlaws dina zaka ajiye ni, daga kwanar gidan Inna sai tasu"
Daure fuska yayi
"Wato kinma san gidan har zuwa kike kenan ?
Kaman zatayi kuka ta dubesa tace "ban taba zuwa ba, Nafiu ya min kwatancen gidan"
Baice uffan ba har suka shigo layin, da hannu tamai nuni da gidan, parking yayi kafin ya karasa gurin, kallon gini yake wanda kiris ya rage ya rushe tsabar tsufan sa.
Maido da dubansa yayi gareta ganin bata da shirin sauka asalima k'asa idanuwanta ke kallo tana zubda hawaye.
"Miye kuma na kuka" ya fadi cikin rashin damuwa da yanayinta.
Kasa magana tayi banda kukan daya sarke ta, sosai takeyi harda shesheka, bai kuma cewa uffan ba banda kafeta da ido dayayi tanai kukan ta.
Dakatar da kukan tayi tahau kokarin bude motar zata fita taji ya riko hannuta, wani irin yanayin taji ta shiga marar mitsaltuwa, juyo da fuskanta tayi suna duban juna cike da so da kauna.
Handkerchief ya cusa mata a hannu yana fadin "ki sharar hawayanki, banaso inlaws dinki su ganki haka"
Janye hannuta tayi tace "thank you"
Yace "In 30 minute xan dawo daukar ki"
Bata iya basa amsa ba ta fice daga motan. Afusace yaja motar yabar gurin, bin kurar daya had"a tayi da kallo.
Bakin kofar gidan ta tsaya hade da sallama cikin sanyayyar Murya, daga ciki aka amsa hade da mata iso.
Wata dattijuwa tagani tsaye tana surfen gero a turmi, daga gefe kuma yar budurwa ke tankade da reraya.
Risinawa tayi tana fadin "Ina wunin ku"
Dattijuwa mai suna Goggo tace "lapia yammata, dadddawa da kuka zaki siya?.
Kafin tayi magana yarinya mai suna Naja'atu tamike tsaye tana fadin "Goggo bara na leka waje ko budurwar Ya Nafiu ta iso" da azama ta rugu waje.
Bata rai Goggo tayi ganin Batul bata da niyya magana, kuma da alamun yar masu kudi ce, ita kuma batason harka dasu dan bata daukan raini, balle ayadda suke marasa hannu da shuni.
"Lafiya kika tsayamin akan" Goggo ta fada cikin kakkausar murya.
Tuni Batul tasha jinin jikinta, tace "Fatima ce, Budurwar Nafiu"
Ware idanu Goggo tayi tana kallonta, fatima da take expecting iri iren suce ba wannan ba, Sallamar Nafiu ce ta katse mata hanzari.
Karasa shigowa yayi, fuskar sa dauke da fara'ar yana fadin "Fatima kin iso ashe, na fita siyo kankana ne"
Gaidasa tayi aladabce, tabarma yayi saurin shimfuda mata yace da ita ta zaune, zama tayi cikin dardar ganin har yanxu Goggo bata saki fuska ba, saima dauke kai da tayi tana cigaba da dakan ta.
"Goggo ga Fatima fah ?
"Naganta" ta fadi atakaice
Baiji dadi da yadda ta ansa ba, tanason fatima yanxu data ganta kuma ta sauya yanayi.
Hira yahau jan Batul dashi, amsa shi kawai take, jikinta asanyaye, tunanin yadda zatai aure agidan take ganin yadda Goggo ta daure mata fuska.
kankanar Naja'atu ta wanko ta dire wa Batul, godiya tayi sosai, Naja ta mike zuwa aikinta suka cigaba da hirar su.
Gidan Inna Rasheed ya nufa, sun jima suna hira daga bisani ta shiga daki ta fiddo wata takarda
Zama tayi tana fadin "tun ranar data bani takardar na karanta abunda ke cikinta ya sanyani matukar mamaki da abunda take fadimin"
Dariya Rasheed yayi yace "ranar bata cikin hayyacinta, kallo daya tama abunda ke rubuce ta dauke kai, banyi tsammanin ta karanta ba"
Warware takarda Inna tayi tana karanto abunda ke rubuce kamar haka "Ni Mamuda na bawa Matata wata d'aya ta koma gidan ta zauna har tayi hankali" dariya sosai Inna tayi tana karantawa, tace "tsabar kidima yasa wata dayan data gani yasa tayi tsammanin Saki daya kayi mata"
Yace "ban sake taba, saidai ayadda tayi tunanin na mata sakin naji dadin hakan, sosai hakan ya temakamin cikin plans dina"
Nisawa Inna tayi "yanxu ya zaka fadi mata akwai auranta akanka kuma kai ba yayanta bane"
Ajiyar zuciya ya sauke yace "datx d problem, bazata ji dadi ba idan tasan ba Baba ne mahaifinta ba, shiyasa nake lallaba ta as my sister har Baba ya dawo ya sanar da ita da bakinsa"
"Ka kawo shawara mai kyau, saidai Mamanka fa, anya zata barta kuwa, kasan dai idan akwai abunda ta tsana bai wuce babanka da zuri'a saba"
Nisawa yayi yace "ayanxu dai bata san cewa nasan komai ba, dole na bitta ayadda ta dauke ni, dadin abun am one step ahead of her".
Jinjina kai Inna tayi tace "Mamanka tayi nisa Allah ya shirye ta"
"Amin" yafadi, mikamai takardar Inna tayi ta nufi gindin murhu tana iza huta.
Murmushi Rasheed yayi hade da shingidewa kan tabarmar dayake zaune, jinjina kai yayi yana mamaki halin Mom dinsa dana Batul two different womem from different world amma halin su daya, at first strategy din Batul yayi using har ya gyara mata zama ta shiryu, ga Mom dinsa data zauna tana fadi mai karya da gaskia, very cunning, haka take shiyasa shima yayi using style dinta ba tare data sani ba, baya Manta ranar data dawo daga Abuja, da dare ya sauko palon kasa sha coffee, yaji maganganu na fitowa daga dakinta, adan tsoroce ya karasa bakin kofar dakin da kusan rabinta bude yake, lekawa yayi yaganta tanai kai komo adakin tanai surutai kaman tab'ab'iya, kasa kunne yayi saidai bai dago inda xancenta ya dosa ba, kalamai kalilan yaji tana fadin "dole yarinyar tabar gidan nan tun kafin My boy yagano cousin dinsa ce" karaf yaji ta rufo kofar dakin da karfin gaske, barin gurin yayi batare daya dago inda xancen ta ya daso ba, washegari dayaga she was desperate ta kori Batul agidan ya sashi sensing akwai wata boyayye, begama gagasta xancenta ba saida yaga ta k'ala mata sata duk dan tabar gidan, baiyi niyyan duka Batul ba amma saboda Mom kawai ya dageta sanna ya bata chance din barin gidan.
Ranar daya bata takardar nan duk part of his plan ne dan ta koma Gidan Inna da zama just to protect her from Mom, unfortunately she was confused tayi tunanin ko sakinta yayi.
He wasn't stupid dazai barta ta kwana awannan gidan datx y turo Inna kwasan wasu takarce yasan definitely bazata zauna ba bin Inna zatayi.
Bayan ya koma gida ya fadi ma Mom Batul matarsa ce, yadda tayi overreacting yasa shi zuwa gurin Abban Mardiyya hade da rokonsa ya auri Mom dinsa akan ta rasa mashishini, dakyar ya amince mai, ranar daya zo kuwa yaji abunda ya dade yana son sanin daga bakinta.
Saidai inda tace Batul kanwarsace ya gigita shi, bai zame ko ina ba sai gurin Baba Lamido dayake ganinsa tare da Baba, gurinsa yaji labarin Batul ba yar cikinsa bace.
Tun ranar daya fadi ma Mom princess is missing ya lura akwai motar dake binsa duk inda ya nufa, shiyasa ya tsiro da aikin nemanta akullum tamkar baisan inda take ba, abunda bai saniba shine yadda Mom tagano Batul na Zaria saidai baiyi mamaki ba yasan hali mom, idan tasawa abu ido sai taga bayansa.
Abincin da Inna ta ajiyemai agaban sa ne ya dawo dashi daga tunanin daya lula,
"Inna harkin gama kenan".
Dariya tayi tace kusan awa daya fa baka hayyacinka.
Ware ido yayi, yace "nabar matata damai shayin"
Dariya Inna tayi, yahau cin abincin, sharp sharp yagama yay mata sallama hade da barin gidan.
Wajen gidan Batul da Naf'iu suka fito jiran dawowar sa, hira suke Nafiu na bata hakurin yanayin Goggo, "akwai ta da wadatar zuci, shiyasa akullum bata tunani kai kanta inda Allah bai kaita ba, laifina take ganin akan ban samo daidai dani ba"
Kwantar da Murya Batul tayi tace "karka damu Nafiu, ka kwantarwa Goggo Hankali, nida kai duk daya muke, saidai wata alfarma nakeso kamin"
Kallon nutsuwa yabita dashi
Tace "Nafiu aure nakeso muyi nan da kwana hudu".
Gabansane yafadi, yasan dawuya Goggo da Baffan sa su yadda yayi aure in four dayx.
Tacigaba "Nafiu ka temakeni ka aureni, karka damu da shirin komai, adai dauran auran kawai"
Sosai yaji ba dadi, saidai bazai iya kin auranta ba dan yana sonta sosai, balle ga dama yasamu bazai so ta kufce mai ba.
Nisawa yayi "insha Allah Fatima karki damu, na amince xan aureki"
Dadi taji sosai aranta dukda wata gab'a a zuciyar ta nai mata radadi, "nagode sosai Nafiu, Goggo kuma nasan zata soni"
Farin ciki shima yake, hira kadan suka taba Rasheed ya iso daukan ta, ganin yadda take washewa Nafiu baki yasa shi daure fuska, gaidashi Nafiu yayi bai amsaba yaja motar afusace.
Murnan dayafi bakin ciki ciwo take a motar, dadin ta daya Mom bazata kashe mata iyayenta ba, kallon Rasheed tayi daya daure fuska.
"Yaya prince ka tayani murna, yau ina cikin farin cikin"
Bai tanka ba banda gudu dayake.
Cikin rashin damuwa da yanayun sa tace "nan da kwana Hudu zamuyi aure da Nafiu, kuma kaine zaka dauramin auran" .
Wani wawa burki yaja da saida kanta ya buge da glass din window.
Huci kadai yake batare daya kalle taba ya kuma tada motar.
Kallonsa tayi kaman zatayi kuka, ba lailai ne ya yadda ya daura mata aure ba, saidai bata da wani zabi daya wuce ta daure ta rokesa.
Shuru tayi bata kara magana ba har suka iso gida, fitowa yayi ba tare daya jirata ba, da sauri ta fito hade da riko hannusa, "plz yaya ka dauramin aure, nayi magana da Nafiu xai turo gobe ayi maganar"
Bai tanka taba har suka shigo palon tanai mai magiya.
Mikewa Mardiyya tayi daga kujerar da take zaune tanai masu sannu da zuwa, bai iya tankawa ba banda tsayawa dayayi tsakiyar palon cikin tsananin baccin rai.
Hannun Mardiyya Batul ta riko tana fadin "Sister inlaw plz ki tayani rokonsa ya amince ya dauramin aure in four dayx"
Ware ido Mardiyya tayi cike da mamaki, saidai zuciyanta na fadin ta rokesa koba laifi zata huta da yadda Batul ke mannewa mijinta.
Kallon Rasheed tayi tace
"Sweetie if dax her wish, y not kayi mata granting, tunda tace aure takeso it better ka aurar ta b4 its too late"
Yaken da yafi kuka ciwo yayi, kusan minti biyar yadauka yana nazari sannan ya dubi Batul yace "na amince".
Ihun murna sosai tayi ta fada jikinsa,
Ran Mardiyya ya sosu, sosai take jin kishin Batul aranta dukda ma kanwar sace, b'ata rai tayi zata wuce daki taji ya riko Hannuta
"Am so happy My prince" Batul ta fadi hade da janye jikinta, idanuwan tane suka sauka kan hannusa dake rike dana Mardiyya, sosai taji ba dadi saurin dauke fara'arta tayi hade da juyawa ta shige daki.
Kallon Mardiyya yayi yana murmushi, "bazaki kawo wa Sweetie ruwa yasha ba"
Saurin sakin fuskarta tayi, cox she cnt afford to lose murmushin dayake mata, "right away my sweetie" ta fadi hade da janye hannuta, kitchen ta nufa da azama yanai bi dakin da Batul ta shiga da kallo.
Am sorry Rasheed, this time around Mom is one step ahead of you.
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: 💖 *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar
®NWA
xarahbukar.wordpress.com
75
kufcewa da kuka Batul tayi had'e da fad'awa kan gado, tunani barkatai ke yawo a kwakwalwar kanta, so take ta fad'imai akwai aure tsakanin su amma bazata iya ba, dole tayi sacrificing love dinta for her parent safety...
Kusan mintinu talatin ta kwashe tana zubda hawaye, turo kofar dakin ne yasata azaman mikewa tsaye tamkar marar gaskia, hannuta takai bisa fuskarta tanai kokarin goge hawayan hade da kirkiro murmushin dole, karasa nufota yayi, fuskarsa dauke da fara'ar yace "Amarya da kanta take kuka"
Girgiza kai tayi tana ja da baya sakamakon matsowan dayayi daf da ita suna shakar numfashin juna.
Hannunsa yakai bisa hab'arta hade da tallafo fuskarta sunai duban juna.
"Miyasa kike son yin aure in four dayx"
Kawar dakai tayi tana fadin "ina son Nafiu, bazan iya rayuwa ba tare dashi.." Kasa karasa kalamanta tayi sakamako murde mata baki da yayi yana fadin
"Gayamin gaskia"
"Dagaske nake" ta fadi kaman zatayi kuka, hannu takai tana matsa bakinta daya murd'e.
Kallon idanuwanta yayi tuni ya gano ba hakan bane band tsoro da fargaba dake kwance jikinsu, karanceta yayi tsaf ya gano akwai abunda take boyewa mai. Baice mata uffan ba ya juyawa ya fice daga dakin
Dakinsa ya nufa yanai kai komo, azuci yake fadin it doesnt make sense tace tana son yin aure in just 4dayxx, tabbas akwai wata boyeyye akasa amma ya kasa figuring out, kodai Mom ke threatening dinta ? Sauri kawar da tambayan yayi, yana fadin it cnt be. Sosai kanshi yayi zafi dabarar kirar Nafiu yayi da tuni numbarsa na wayan, bugu daya Nafiu ya dauka, atunaninsa Batul ce yasashi washe baki, jin muryar yayanta yasa shi nutsuwa hade da saurara kalaman da yake fadi akan yayi hakuri ya rabu da Batul matar aurece ita kanta batasan dakwai aure kanta ba.
Jiki sanyaye Nafiu yahau basa hakuri akan bai taba sanin matan aure ceba kuma yayi akawarin bazai kara kiranta ba dan tuni Gogonsa ta taka mai birki tsakanin su.
Sosai RmD yaji dadi da fahimtar sa, katse wayan yayi hade da hamdala, saidai yasan Batul bazata fasa nemo wani ya aure taba ayyadda yaga she is desperate taga tayi aure cikin kwanaki hudu, kaman wasa ya gwada trying Numbar Baba, yaji tayi ringing, farin ciki marar mitsaltuwa ce ta mamaye mai zuciya, sau kusan hudu yana ruri baa dagawa, ana biyar ne Baba dake aikace aikace agona ya adaga hade da sallama.
Gaisuwa sosai sukayi, nan take cikin girmama Rasheed yahau mai bayanin abunda ke faruwa in Brief.
Cikin nuna rashin damuwa Baba yace karya damu gobe zaibar abunda yake su dawo kaduna, maganar tafi karfin waya, sun jima suna tattaunawa daga bisani sukayi sallama.
Ajiyar zuciya ya sauke cike da mamakin rashin damuwa da Baba yayi, atunaninsa xai nuna farin ciki bayyanar dansa sai yaga sabanin hakan tamkar dama yasan shi amatsayin dansa.
***
Zaune suke su ukun a parlour, kowa wanne su da abunda yake tsakawa aranshi ba tare da sunce uffan ga junan suba.
Mikewa Batul tayi daga ce nesa da take zaune dashi ta karaso inda yake hade da daukar wayarsa sa, baice da ita uffan ba ta koma mazauninta hade da dialing no din Nafiu, akashe ta jita kusan sai goma tana trying.
Guntun tsaki taja hade da dubansa da gabadaya hankalinsa na kan Tv.
"Yayana nambar Nafiu bata shiga, kuma munyi dashi zasu xo yau"
Bai kalleta ba yace "nasani ai, suna hanya"
Ware idanu tayi cike da murna tace "kunyi magana dashi ne"
Kallo daya yayi mata yadauke kai, aranshi yana fadin "she's really an actress".
Shurub da yayi bai tanka ba yasa ta tunanin ko dagaske suna hanya.
Murmushi Mardiyya tayi daga inda take zaune tana latsar wayarta, kallon Batul tayi tace "Sister inlaw yakamata muje shopping, afara shirye shiryen bukin".
Yatsine Fuska Batul tayi
"Sister Mardyy banason wani shiri, iya kaci ashafa fatiha ya mik'a ni, aurena na farko aka akamin balle kuma ma na biyu" karashe xancen tayi cikin zolaya.
Dariya ne yakusa kufce mai amma ya daje yace "Diyya ta kowa good idea, ki tashi sai kuje tare yin shopping din"
Fir Batul taki yadda, saida taga yayi mata jan ido sannan ta amince suka fita shopping din bayan ya baiwa Mardiyya credit card su siya abunda suke so, shopping din kayayyaki masu tsada sukayi da temakon Mardiyya, saidai ita ko zobe bata siyawa kanta ba haka suka dawo gida.
****
Matashin saurayi da Mom ta tura unguwar su Baba sa idon dawowar sune tsaye a farfajiyan gidanta yanai jiran fitowan, cikin takun isa ta nufosa, yan dubu dubu rike a hannuta.
Gaidata yayi bata amsa ba tace "ya ake ciki ?
"Sun iso jiya da daddare" ya fadi hade da risinawa.
"Ka tabbata".
Yace eh.
Kudin hannunta ta mike mai ya amsa hade da godiya, ya juya ya fishi.
Ciza labba tayi tanai neman mafita, batayi expecting dawowar suba tun kafin Batul tayi aure, kwafa tayi tana tunanin abunyi, dole nate gidan naci masu mutunci kafin My boy su rigata zuwa, muddin ya iske Baba akwai amatsala.
Kwalla Altine kira tayi hade da fadin ta dauko mata mayafi da mukullin motar ta. Da azama altine ta dauko ta fito ta bata, saurin fadawa