Showing 33001 words to 36000 words out of 48742 words

Chapter 12 - INA ZAN GANSHI Complete Book By Xahra Bukar.txt

14 Jan 2025

2383

karamin konamai zuciya yake ba, ita kadai yakeson gani koya ji sanyin a zuciyar sa, yasan itama bazata rasa sanin wani abu game da auran baba da Mom ba.
Haka dai suka karaso
maidaidecin gidansa mai dauke da daki biyu da palo, parking sukayi ya sauko cero masu kayansu, dakyar Mardiyya ta samu ta fito daga motar, taku daya biyu tayi, taji tana neman faduwa, sauri taro ta yayi dan kuwa kiris ya rage bata je kasa.
"Are u alright" ya fadin yanai kallonta, itama kallonsa take saida ta kasa furta koda kalma daya.
"Muje ciki" yace da ita, kasa takawa tayi yayi saurin cicibarta suka shiga ciki, dakin ya shiga ya direta kan gado yanai mata sannu.
"Diyyah kodai muje asibiti"
Kai ta girgiza kafin yayi wata maganar tuni ta rufe idanu, bacci yayi gaba da ita
Shafe gefen fuskarta yayi yana jiyo numfashin ta dake fita ahankali, cike da tausayinta ya janyo comforta dake gurin ya lullube ta, yasan kukan data yi yasa tazama exhausted.


Shuru dataji yasa Mom fitowa parlon, haurawa sama tayi ta leka Dakin Mardiyya, babu ita balle kayanta, murmushin jin dadi tayi ta karasa dakin Rasheed, wayam ta gani babu kayansa sai wata takarta data gani da rubutu, an ijeye kan gado.
Dauka tayi ta bude, tahau karanta abunda ke ciki.
"Am sorry Mom, banda zabi daya wuce nabi matata mubar miki gidanki, burina daya na nemo duk inda princess take although she is my sister i won't stop loving her, dukda da diyar kishiyar ki ce, i hope wataran zaki sanyawa zuciyar ki so da kaunar ta. Love you Mom"
Squeezing takardar tayi hade da wurgi dashi tana huci, wayarta dake hannuta ta duba hade da dialling wata number, bugu daya aka dauka
Tace "Roze kaga picture dana ma sending ?
Cikin muryarsa ta yan daba yace "Nagani, na miye ne ?
"Roze yarinyar nake so ku nemo ku kawo min ita dead or alive"
Dariya yayi yace "angama hajiya, yanxu xan tura yara parade duk inda take zasu ganta.
"Make sure duk wata kauye da birni na kaduna ku bincika, Yarona is desperately searching for her, make sure ku kawo min ita kafin ya ganta".
"Ba matsala Hajiya, muna da branch ko wana gari, duk inda take zamu ganta.
Katse wayan Mom tayi tana huci, afili tace "saura ke Safara, i have unfinished business dake" afusace tabar dakin.
Mayafi kadai da car key ta dauka ta fice waje, motarta ta shiga taja zuwa gidan Hajiya safara cikin fusata.
As usual, daga window Hajiya safara taga dirar motar Mom, fito tayi da azama zuwa farfajiyan gidan sukayi kicibis.
"Munafuka maciya amana, kwadayayya, duk hallacin danai miki haka zaki sakamin " mom ke fadi cikin daga murya.
Harara hajiya safara takai mata, tace "karuwan banza kin dauka bansan bibiyar mijina kike ba, idan ni mai kwadayi ce ke kuma karuwa ce"
Hannu Mom tasa ta wanke ta da mari,
"Kika mareni" Hajiya safara ta fadi kin shock.
Kokuwa ce ta barke tsakanin su, da gudu Biebee dee dake labe bakin kofa ta fito tanai rabasu, dakyar tasamu ta janye Hajiya safara da tuni tafara jigata.
Cikin huci mom tace "zaki ci ubanki, saina nuna miki ni ba tsarar ki bace" juyawa tayi ta koma motarta.


Zagi sosai Hajiya safara take lailayo mata, dakyar Biebee taja ta suka koma parlour cike da mamaki aminan juna yau sune da zage zage da bankadawa juna asiri, jinjina kai tayi, azuci tace "aminantaka akwai dadi, saidai duk yadda kake da mutum ba ko wana sirrin ka zaka fadi mai ba, koba jima koba dade akwai shaidan yana iya shiga tsakanin ku, daganan kuwa fallasan asirin ya biyo baya, love all but trust no one" (ni xarah nace maganarki dutse.)


Fitowa Mom tayi tare da parking gefen titi, tunanin kadai take yadda zata rama betrayal da aminiyarta tai mata, sai yanxu takejin haushi fadi mata komai nata alhalin ita bata taba gayamata komai game da ita ba, dogon tsaki taja tana karason tuno wani abu da zatai using against her, abu daya ta dade tana son sani game da Hajiya Safara shine "source of her income (asalin dukiyar ta)" asali Alhaji Bello talakane, Mardiyya nada shekaru biyar aduniya hajiya safara ta koma Ghana gaisuwar rasuwar Babanta, bayan wata shida ta dawo amatsyin mai kudi, abu daya tace masu wai gadon Ubanta ne, kadarorin daya bari ta siyar ta dawo Nigeria.
K'wafa Mom tayi tana kara fadin "babanki talakane, asalima talauci ya kawo ki nigeria har muka hadu a skull din da kika shigo amatsayin yan alfarma, i know you're hiding something, amma miye ne ?
Ajiyar zuciyar ta sauke ta kunna motar ta karasa gida.


****


Bayan kwana biu.


Rasheed da Daddy Malam basu bar neman Batul ba, sune har Abuja zuwa nemanta, aganinsu can garin Manya ne kila can ta nufa, ba hope haka suka dawo kaduna.
Ta bangaran Mutanan Mom su Roze suma basu fasa baza idanu ba, akullum saita ninka masu kudi da zata masu idan har suka gano ta, sosai suka fantama yin aikin su.




*Zaria*


Juya wainar take cikin hankali da kwarewa, masu siya sai siya suke, wani yaro ne ya miko kudi.
"Gashi inji Nafiu wai kisamai ta hamsin"
Toh" Batul ta fadi hade da amsan kudi tana murmushi.
"Shiga cikin gida ka dauko min kwano" tace da yaron.
Kwanon ya dauko ya bata, ta zubamai harda miya tare da karamai da nama.
"Gashi ka kai, kace ina gaida sai, karya manta da dare idan na dawo islamiyya zamu hadu" ta fadi tare da mikama yaron kwano, amsa yayi da toh sannan ya wuce.
"Mu kenan bazaa a samana a kwano ba sai leda" wata yarinya dage gurin ke magana.
Dariya kawai Batul tayi tasan zolayar ta take.


"Ke jikan mai waina sako min ta dari" wani matashi dan Tasha ke fadin haka cikin daga murya.
Daure fuska tayi, koda wasa taga iri irin su b'ata rai take, "kawo kudi" ta fadi.
Hannu yasa aljihu yana kokarin ciro kudin tare da kare mata kallo, fasa ciro kudin yayi, ya ciro wayarsa kirar Techno yana kallon hoton ta dage cikin wayar, kusan minti biyu yayi yana compare and contrast din fuskar ta dana hoton, babu tantama yagano ita dince, fasa siya yayi yabar gurin, lungun ya samu ya kira ogansu na gurin ya shaida mai yaganta, nan take suka ajiye plan din cafketa da dare.




Kaduna


Cikin sauri ya fito daga dakin, kitchen ya nufa inda yaji motsi Mardiyya.
"Diyyah na fita" yace da ita.
"Sweetie ina kuma, dazu kawai fa kadawo"
"Kin manta we are still searching for princess"
Kallon rashin fahimta tamai
"Wace princess?
Gira sa ya daga yanai kallonta, yace "Sister inlaw dinki"
Still bata gane ba, ganin zata b'ata mai lokaci yasa yabar gurin.
Dafe kai tayi tace "Allah ya bayyanaki Princess"
Rasheed dake labe bakin kofa yana jinta, recently haka take behaving so confused anjima kuma ta koma normal, bai kawo komai aransa ba ya fice ya shiga mota yabar gida.


Daddy malam ya kira awaya suka hadu a hanya ya daukesa suka bazama da shiga unguwanni neman ta, daddy malam kam ya fara gajiya da abu daya babu hope, shawarar zuwan gidan redio da talabijan y kawo, ba masu Rasheed ya yadda dan shima ya dade da tunanin haka.
Juya kan motar yayi zuwa hanyar da zata sadasu da gidan labarai.
Wayar Daddy ce tayi rurri, dubawa yayi yaga Inna, cike da fara'a ya dauka suka gaisa,
Tace "wato ka manta ni ko?
"Haba kakus zanxo kwanan nan, aiki ne yamin yawa" ya fadi.
"Wana aiki ni xaisa kaki xuwa" Inna ta fadi atakaice.
Yace "Batula ce ta b'ata, shine fa muke yawon nemanta haryau babu labarinta"
Salati Inna ta saki, tace "Batula ai muna tare, ta jima a Zaria"
Cike da mamaki yace "batula na gidan ki"
Wani mugun burki Rasheed yaja tamkar yaji maganar da suke, karbe wayar yayi yace "Inna gani nan zuwa" katsewa yayi hade da saurin yin reverse.
"Nidai sauki ne na koma gida, nabar Maman Aryan ita daya" Daddy malam ya fada yana dariya.
Tsayar da motan yayi ba tare daya kallesa ba.
Daddy yace "ka bari gobe sai muje, yanxu fa Magrib tayi"
Harara ya kai ma "kaidai sauka kawai".
Sauka yayi yana Dariya.
Rasheed yaja motar, massallacin hanya ya tsaya yayi Sallah sannan ya buga motar to zaria, cikin mintina ashirin da biyar har ya iso, a gurguce ya fito ya shiga gidan.
Inna na zaune tsakar gida tana jan jarbi ya shigo, zama yayi jiran ta sallame sannan ya gaida ta, cike da faraa ta amsa mai.
"Inna ina Batul take ?
Dariya tayi.
Daure fuska yayi atunaninsa wasa take mai
"Bata nan, taje islamiya, sai tara zasu tashi".
Ware idanu yayi, wai batula a islamiya, mikewa yayi yanai tambayarta ina islamiyar take, nan ta kwatantamai na bisa bakin titi.
Da azama ya fice, bakin gate din islamiyar ya tsaya cike da farin cikin xai ganta, agogon hannusa ya duba just 20 minti ya rage su tashi.


karamar kofa dake bayan Islamiyar suke tsaye daga can nesa.
"Ka tabbata tanan take biyowa idan suka tashi"
"Eh, ta nan ne, yafi kusa da gida da take azama"
Matsawa gefe su hudun sukayi jiran ta fito su chapke ta.

Cikin sa'a Batul ta fito daga karamar kofar, tafe take hankalin kwance tanai kara tilawar karatun da Malama Sophie ta koyar su, takun data ji abayanta yasata waiwayawa da sauri, wayam tagani babu kowa, gabanta ne yahau dukan uku uku, cikin sauri takara daga kafafunta tanai waiwayan bayan, kamar daga sama taga gardi biyu tsaye a gabanta, kafin ta juya tuni biyu su tsaya daga baya sun zagaye ta.




Murmushi Rasheed yake baki yaki rufuwa, yan mata da samari sai fitiwa suke daga gate din, ware ido kadai yake yana jiran fitowar little Sister dinshi.....
[10:01PM, 5/26/2017] Xarah Bukar: *INA ZAN GANSHI*💖
Rubutawa
Xarah Bukar


®NWA


xarahbukar.wordpress.com

73




Shuru babu alamunta, har dalibai suka k'arasa fitowa, Mai gadin gurin ne ya mike hade da kokarin kullo gate din.
Yace "dan dakata, karka kulle kanwata bata fito ba"
Karasa kulle gate din yayi hade da datseta ta k'wado, sannan ya kallesa yace.
"Lokacin rufewa yayi, saidai ka duba karamar kofar baya"
Nagode" yace da dashi yayi azaman zagawa baya.
Dalle mata idanu Roze yayi yana kallon fuskarta, kallon hoton wayarsa yayi yace da sauran ita dince, ku dauke ta kusa ta cikin mota.
Tsoro ne ya dabaibayeta, kallon su take bata gane ko wanne cikin su ba sakamakon mask dake sanye fuskar su, kuka ne ya kufce mata tahau rokonsu, ko sauraranta basu yi ba sukayo kanta, ihu ta kwalla, dabarar tsugunnawa tayi ta kwaso kasa ta watsa masu fuskar. A 360 ta arta aguje, cikin tsananin fusata suka bita da gudu suna goge idanuwa da shikadai ke bayyane cikin mask din.
Ihun ta daya karad'e dodon kunnansa yasanya shi saurin barin gurin da tuni ya iso yana jiran ganinta, cike da tashin hankali yahau zubawa hanyar ido, daga nesa ya gano katti na gudun famfalaki, motarsa ya fada da azama ya fuzgeta afusace.
Gudu sosai take. Tsabar kid'ima wuce layin gidan Inna tayi ta fada makarantar UBE dake fuskan tar ta, ajin farko ta fada ta karasa can karshe ta boye karkashin desk, dagowa tayi ahankali tana lek'e ta window, tsaye tagansu daka can nisa suna leka ajujuwan dake gefe, aji biyu kadai ke tsakani kafin su karaso inda take. Sosai hankalinta ya tashi tanai sharar kwalla, ziro kofofinta tayi ahankali ta window ta fito kasancewar babu glass, tuntube taci da dutsen dake gurin ta kwalla ihun daya janyo attention dinsu gurun, da axama suka fada ajin tare da baza idanuwa.
Cike da radadi da azaba ta falla da gudu, bata ankara ba taji hannu ya rikota, ihu xatayi yayi saurin sa hannu ya toshe mata baki, janta yayi suka lafe cikin bishiryar dake gurin, runtse idanu tayi tuni ta sadakar sun kamata, saidai kamshi prince dinta dake bugar mata hanci yasata faduwar gaba.
Hannu yakai bisa fuskar ta yanai share mata kwalla, cikin sanyin muryar sa ya kira sunanta da princess, kin bude danu tayi banda rawa da jikinta yake, atunanin ta bashi bane, zuciyar ta keson yaudarar ta.
"Princess baxaki bude ido ki kalli prince dinki ba"
Bude idon tayi ahankali ta daura sa bisa fuskarsa, kuka ta fashe dashi ta fada jikinsa tana fadin "i know you hate me but plz ka temakeni kar mutanan nan su kamani, plz save me" kuka sosai take tana maganar.
Baice komai ba, yasan inda xancen ta ya dosa, rikota yayi suka karasa motarsa yabude yasanya ta ciki sannan ya shiga yaja.
"Oh shit" Roze ya fadi adaidai lokacin da suka karaso yaja motar, kallan yaran yayi yace operation continues tomorrow, jiki sanyaye da haushi rashin kamata suka bar gurin.
Kuka kadai take a motar har suka karasa gidan Inna, kafin ya daidaita parking tuni ta sauko ta ruga cikin gidan, daki ta nufa hade da rufo dakin ta ciki.
Mikewa Inna tayi daga inda take zaune a tsakar gidan.
"batula lapia kuwa" Inna ta fadi cike da tashin hankali, ganin rasheed ya fado adan kidime yasa ta kallesa tanai tambayar sa make faruwa, bai iya amsa taba ya karasa bakin kofar yanai bugama Batul kofa hade magiyan ta bude. Banxa tayi dashi tanai cigaba da kukanta.
Yaro ne ya shigo yace Nafiu mai shayi na sallama da Batula, daga Shi har Inna kasa tanka yaron sukai, Batul dake jinsa ta bude kofar ta fito, bata ko kallesa ba ta raba gefensa tayi waje, Sauri binta yayi ya tsaya bakin kofar ganin ta tsaye gefe kusa da wani saurayi.
Gaidasa tayi cikin kokari boye yanayinta, cike da farin ciki ya amsa, yahau ta da hira da ba fahimta take ba, banda eh da a'a dakadai take cemai, gabadaya hankalinta baya tattare da ita
Yace "fatima yaushe zamu je ki gaisa da iyayena, na jima ina basu labarin ki"
Yaken daya fi kuka ciwo tayi tace "duk randa ka shirya sai muje"
Dariya yayi.
"Toh amarya yata, Allah ya kaimu, nizan wuce sai da safe.
"Haba dai, tun yanxu" ta fadi ita kanta ta kosa da hirar, saidai ganin Rasheed tsaye gurin yasa batason ya tafi.
Tsayar da Nafiu tayi na kusan awa daya sannan sukayi sallama ta shigo gida.
Riko ta yayi da sauri ta fuzge zata shige daki, Inna ta kira sunanta, dole ta tsaya bazata iya share taba.
"Zonan ki zauna" Inna ta fadi hade da mata nuni da tabarma, jiki sanyaye ta zauna kanta na kallon gefe daban.
Zama yayi kusa da ita, "plz princess ki saurareni.
Dogon tsaki taja tare da dubansa tace "kaga malam idan ma kazo ne kamaida ni gidan ka you're mistaken, cox bazan bika ba, i'd rather die akan na kasance dakai, saboda na tsanake"
Murmushi yayi da jin kalamanta, mikewa tayi afusce tana fadin "ga mahaukaciya na magana dole kayi dariya" rikota yayi yace dawo ki zauna.
Zama tayi tanai buga mai harara.
Yace "nazo ne amatsayin yayanki na jini ba mijin kiba, plz princess ki gayamin gaskia matan Baba nawa ?
Kallon rainin wayo tayi tace " Allah ya sauwake ka zama yayana, mugu kawai, kuma babu ruwanka dako matan Baba nawa"
"Dan Allah ki gayamin badan hali naba" ya fadi amairace.
Kallonsa tayi taga lailai ba wasa tattare dashi, saidai tambayar tai mata bambarakwai.
Tace "matan Baba daya, itace Maihaifiyata Hajjo"
Hannuta ya riko, kaman zaiyi kuka yace "princess ke kanwata ce ta jini, baban mu daya dake"
Kallon rashin fahimta tamai, gabadaya yasata duhu.
Yacigaba "apart from Hajjo wace mace ce kika sani arayuwar Baba ?
Shuru tayi tanai tunani tasan dai babu ko wace mace daga Hajjo sai ita, can dai ta tuna da wani abu tace "akwai mace daya mai sunana, saidai bansanta, Baban bai taba xancen taba, abakin Hajjo nima nasanta, idan nayi laifin takance halin ku daya da mai sunanki, wataran na tambayi Baba wace ce mai sunana, cewa kadai yayi baya fatan nasanta".
Kur yayi mata da ido, yace "Ci gaba"
"Shikenan abunda nasani"
"Plz princess try to remember wani abu
Bata rai tayi hade da dauke kai, tace "ni ba princess bace kadai na kirana da hakan".
Juyo da fuskar ta yayi yace "to mi you're a princess, sunan Momcy gareki kinsan bazan iya fadin sunan kiba".
Gabanta ne ya fadi adalilin kamshi gaskia data fara ganowa cikin xancen sa, sau da dama takan ga kamarsu da Baba saidai bata taba kawo komai aranta ba, kallon sa take tana son tuno wani abu, azubure ta mike tana fadin "OmG".
mikewa yayi hade da riko ta, tuni jikinta yahau rawa.
Cikin muryar kuka tace "you're right, kai yayana ne, what am not sure shine ba Mom ta haifeka ba, i tink Hajjo ta haifeka"
Sabon rudani ya shiga, yasan dai Mom ce uwarsa, yace "miyasa kika ce haka
"Hajjo once told me bani ce yarta ta fari ba, tacemin akwai yayana saidai ya b'ata baa gansa ba" ta fadi cikin kuka, rungumota yayi yanai lallashin ta, abunda dama yake son sanin wato su sibling ne, it doesnt matter ko wace ta haifesa, abu daya yasani shine Mom ce amatsayin mahaifiyar sa.
Kuka sosai take cike da tashin hankalin ya haramta gareta, sai yanxu tagane ashe tun asalin soyyayar jini ce ta hadasu take ta shirme da haukan son shi.
"Princess" taji tlya kira sunanta cikin wata kasalalliyar voice.
Kasa amsa mai tayi, tajanye jikinta gefe, kusa da Inna ta zauna hade da daura kai kan cinyarta tanai kara sautin kukan.
Tausayin su sosai Inna taji, ita kanta sharar kwalla take, matsowo yayi daf da ita yace "Baba suna kauye, gobe ki shirya sai muje can, ai kinsan garin ko ?
Girziza kai tayi alamun a'a bata san garin ba, asalima ma ko sunan kauyan bata sani ba, Jigawa state dai tasan kauyan yake, tun bayan da tana karama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login