Showing 51001 words to 54000 words out of 60557 words
Chapter 18 - ZABIN ABBANA Book Complet by Ummeey Muhammad Lawan .txt
ama bansamuba sakamokon daren da yayi
Haka naita bulayi a cikin anguwa ama bansamu Abu hawaba hankalina ya tashi sosai
Gida nakoma Dan naje Naga wane halin Ameenah keciki
Inazuwa nasameta a wahale Aysha nakanta Tana Mata sanu
Damisalin karfe 3 : 20 Ameenah tahaihu tahafin d'ata namiji ama kash!!!!!!!!!! Dan Bezo da Raiba
Ameenah tayi kuka Kamar Ranta zaifita nima kawai daurewa nakeyi Dan nikadai nasan irin radadin da nakeji a Raina Allah yasani muci buri a kan Wana cikin saide kana naka Allah nanashi saide Kuma na Allah shine dedeee
Muna cikin Wana yanayi itama Aysha nak'uda tataso Mata gadan gadan kafin nafita Nemo Naffe har tahaifi santaleliyar Yar,tah mace
Bayan tahaihune jini ya b'allee Mata a zahiri gaskiya hankalina bakaramin tashi yayiba
Nazo zanfita Dan Neman Mai Naffee saiji Muryarta nayi Tana fadin Mallam...tsayawa nayi cak jin muryarta kasa kasa Tana fadin Mallam ga Amanar yariyata nabar muku ita kuriketa Amanna
Wana jakar kudine a cikin da gwalagwalai namalaka makasu halak malak kakulamin da yariyata a cikin jakar akwai photo mahaifita a cikin Alahaji Sadiq sananene a cikin garin Bauchi a G.RA yake da Zama
Dan Allah Mallam Ina rokonka kada kasada Wana yariyar ga Mahaifinta danyin hakan tankar salwantar da rayuwata ne
Dan natabata idan Saratu tasan Ida Wana yariyar take bazata tab'a barita a rayeba
Dan Allah Mallam inason kazamewa Wana yariyar Uba a gareta kekuma Ameenah inason kizame Mata Uwa
Hawayene suka zubo daga idanun Ameenah cikin kuka tace kidena fadin haka insha Allah Zaki tashi zakiyi rayuwa tare da Yar,kin cikin Amince da kwanciyar hankali
Kallonta nayi cikin sanyi jiki nace da ita Nagode Aysha da Wana kyauta mafi girma da daraja da kikamin
Nakarbi Amanar da Kika bamu Zan rike Wana jariyar tankar Yar Dana haifa a cikina Zan nuna Mata duk wani gata da yadace Uba yabawa Yar,sa
Bazan karbi Wana dukiyarba da Kika malakamiba saide Zan dakawa yayana ya diga juyata har zuwa lokacin da Allah zai rayamin Wana jaririya Zan danka Mata kayanta mudin tamalakin hankalin kanta
Cikin zafin ciwo tace nagode Mallam Allah ya sakamaka da mafifincin alkairi
Sai mukaji tayi shuru jijigata Ameenah tafarayi Ashe Rai yayi halinsa haka naje nasanar da limamin unguwarmu a
cewa Allah ya karbi rayuwar Yar uwata
Aiyi Jana izzarta an kaita makwancita nakira yayana nashaida Masa komai
Shima yayana Abdallah yasanar da baba
Baba yakirani ya min nasiha akan narike Wana yariyar da Amana kada nakuskura nasanar da ita cewa bamu muka haifetaba saide idan lokacin da Zan Aura da ita nakan yazamo Dole
mijin da zai Aureta yasan gaskiya wana lamari
Murufe Wana Sirin muhudu muka sanar da Yan,uwa da saura dangi cewa Ameenah ce tahaihu
Dagina gaba daya suzo suna nasawa yariya suna Mahaifiyarmu Ummulkhari
Bayan suna natafi Gombe nasamu yayana Abdallah namika Masa Amanar dukiyar Ummeey da gwalagwalai ta akan ya sayar dasu ya diga juya kudin tuda shin ya kware a harkar kasuwanci
Dakar Yaya Abdallah ya karbi Wana dukiya sanan yasanar dasu Halima cewa tadalilina wani ya temakesa ya Raya Masa jarin
Allah ya Albarkaci kasuwanci Yaya Abdallah lokaci kalilan arzikin yayana ya habaka
Habiba nagani arzikin mijita ya habaka tasake daurawa kanta girman Kai gawani tsanar da takeyiwa Ummeey saboda taga yayana Yana daukar duk wani d'awainiyarta
Rayuwa taci gaba da tafiya Ummeey tagirma ta malakin hankalin kanta naci gaba da ajiyar photo Mahaifinta
Wasiyar da Baba ya barwa yayana Abdallah itace Muhada Ummeey Aure da Muhammad Dan gudun kada Wana sirin namu ya fita
Sanan ya zabin nadawo Gombe ne Dan nasanar dashi cewa Ummeey tasamu Mijin Aure a lokacin suna tare da Haydar
Babamu yakin Amincewa da wanan hadin tsakani Haydar da Ummeey duk Dan gudun kada wata Rana Ummeey tawulakanta a gusa
Shine baba yace mu dawo Gombe dazama to dalilin Dawowarmu Gombe kenan Wana itace wasiyar Mahaifimu
Muhada Ummeey da Muhammad Aurene saboda gudu tonuwar Wana Siri
To kuji takai tace tarihin Ummeey
Mamana dafatan kifahici koke wacece Kuma Ina rokonki kada matsayimu ya canja a guki har gobe mu iyayyenkine...._*ZAƁIN🤵🏻♂ABBANA👳🏼♂*_
_*NA*_
_*UMMEEY MUHAMMAD LAWAN*_
_*(UMMUH AFNAN)*_
_*"YAR AUTAR💃🏻DASHEN🌲 ALLAH*_
https://www.facebook.com/profile.php?id=100087451774783
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=2192729347574173/?ref=share
_*FACEBOOK LINK*_
https://www.facebook.com/groups/2192729347574173/?ref=share_group_link
_*WHATSAPP LINK*_
https://chat.whatsapp.com/CnAupcS3i8c4y3JHVuXYXA
_*DASHEN🌲 ALLAH*_
_*WRITER'S ASSOCIATION📚📚*_
_*ALLAH SHINE GATAN MU*_
_{ƙungiyar dashen allah ƙungiya ce ta jajurtattun marubuta kuma tsayayyu masu aiki da ilimi wajen rubutunsu dan ganin sun kawo muku labari wanda zai wa'azantar daku ilimantar daku, faɗakar daku.}_
*Alƙalami✍🏽 yafi takofi🗡️*
For more information
08140801885
Page 97 & 98
______________Dago Kai tayi tadaura daradaran idanuwata akan Abba wasu hawayene masu zafi suka zubo kan Fuskanta
Cikin wata iriyar murya tace Abba. Mama kalmar godiya tayi k'ank'anta a gareku saide nayi muku Adu'ah
Allah Ubangijin ya saka mukun da mafifincin alkairi Allah ya biyaku da gidan aljannah
Abba da Mama bani da wasu iyayyen a Wana duniyar saiku kune kuka raineni tun Ina tsuman Haihuwa harzuwa girmana kuka bani tarbiya Tagari kuka dau duk wata d'awainiyata bana manta irin wahalhalu da Abbana yasha akaina duk Dan ganin ya inganta Rayuwata bakutaba gajiyawa akan d'awainiyar da kuke daniba.
Wlh yau zuciyata cike take da farin ciki inajina tankar wace akayiwa bishara da Aljannah
Gani nake nafi kowa sa,a a cikin Wana duniyar Allah nagodema daka sanya rainona a hanusu Abba da Mama
Mutane masu karanci wad'ada suka fifita fari cikina akan nasu Basu da buri daya wuce suga sun ingata Rayuwata
Wlh iyayyena matsayiku bazai taba sanjawa daga gareniba saima darajarku da kimarku da suka dad'a nikuwa a zuciyata har Abada kune iyayyena wada nake Alfahari dasu
Cikin jin dadin kalaman da suke fitowa daga bakin yar'tasa yace Mamana tsakanimu dake Babu godiya duk abuda mukayi mikin mumikine saboda musauke nauyi dake kamu
Mahaifiyarki tamalaka manake halak malak tadanka Amanarki a hanumu
Mukarbi Wana Amanar muka yimata Alkawari zamu rikeki bisa Amanna har zuwa Ranar da Zamu Aura dake
Allah nagodema daka bani ikon cika Wana Alkawari da nadaukarwa Aysha Allah Kaine sheda akan iri rikon danayiwa Wana yariyar idan har akwai Ida nagaza Allah kayafemin
Ummeey zatayi magana Abba Muhammad ya dakatar da ita tare da fadin
Ummeey Abbaki ya sauke nauyi dake kansa sai Kuma niiiii
Nima a yau Zan sauke kayan daya dade yanamin nauyi a kaina a yau Zan danka mikin dukiyarki
da tayi kimani shekaru Ashirin a hanuna Ina juya mikinsu
Cikin ikon Allah Allah ya Albarkaci Wana dukiya tabukasa harta jawo an malakin manyan kadarori kamar su filaye da gidaje
Yazu Zan dankamiki dukiyarki Kamar yarda muka tsara nida Abbanki duk lokacin dakika malakin hankalin kanki zamu dank'a mikin dukiyarki a hanuki
Muso mudank'a mikin dukiyarki tun lokaci da muka hadaku Aura da Muhammad ama sai nayi wani tunani nace mubari zuwa nagaba tukunna muga irin rikon da Yaya naki zaimiki
Sai Kuma yayi mikin rikon irin na zalinci wlh nayi danasani hadaki Aure da yayanki. Muhad'aki Aure dawada Kwata Kwata Bai dace dakeba..
Mikewa Momy tayi tsaye cikin tashin hankalin tace wlh bazai inyuba Wana gaba daya shirine iri na Muhammadu wato Tana kabulo yazu Kuma Too wlh bazai iyuba bazan taba barika kayi nasara a kan Mijinaba
Alhaji ka dawo cikin hayacinka
Natabata Muhammadu wani Asiri yasake maka Dan ya rabaka da dukiyarka
Tooo wlh baka isa karaba mijina da dukiyarsaba
Tsawa Abba ya dakamata wada ya hadasa Mata tsorasa a Ranta
Cikin bacin Rai Abba yace kada nakarajin kice wani Abu Ana gurin ai dama Iri Wana Ranar nake guje muku dagake har d'anki Ranar da zakuyi nadaman da danasani akan Abubuwa da kuke aikatawa
Gaba dayaku kusan waneneni kafin shekaru Ashirin dasuka wuce
Bazansa kaina daga cikin Tallaka ba haka Kuma bazance nimai Arziki bane
Saide nasan Ina da narufin Asirin
A cikin lokaci kalilan kikaga canji a tatare Dani ama baki taba Tabayata ta dalilin Wana canjiba bare harkiyi tunani ta Ina nasamu Wana dukiyar
Haka mukaci gaba da rayuwa dake batare da kitaba min magana akan Arziki da kikaga nayi lokaci gudaba. Saima murna da farin ciki da kikeyi mijinki ya zamo Mai Arziki baki damu kisa dalilin samuwar saba
Yan,uwana su Halima da Asabe suzo susameni da maganar
Ama sai naboye musu gaskiya lamari nace musu Muhammadu ne yahadani da wani mutumin a can Kano ya bani jari sana suka samu nutsuwa a rannsu
Gaba daya dukiyar da kuke tikaho da ita too kalilance tawa a ciki saura dukiyar Ummeey ce
Hata gidan da Muhammad keciki shima natane
Dago Kai Muhammad yayi a razane yace Abba gidanta Kuma tayaya gidan daka malakamin zaizamo nata
Murmushi Abba yayi yace kwarai kuwa gidan Ummeey ne da dukiyarta aka gina Wana gida hasalima Mahaifita shine ya bukaci Dana danka Wana gidan a hanuka tuda Kaine zaka zamo mijinta
Too kaji dalilin baka Wana gidan danayi
Zufane ya ketowa Muhammad take nadama da danasani suka kamasa inama ace zai iya maida hanu Angogo baya daya mayar
Ya goge duk wani laifin daya aikata a gareta
Gwogwo Halima tace tooo suuu Habiba karyar Arziki yakare ko Ashema Arzikin dakike gadara dashi na Yar,mune
Mama ce tace Halima kibar Wana maganar ai komai yariga da yawuce kuskurene Ariga da anyishi saide muyi fatan Allah ya yafemana
Gaba dayasu suka Amasa da Ameeen Momy ko jitake Kamar tanitse kassa saboda kuyan Abuda ta aikata
sai yazu take danasani Abubuwa data aikatawa Ummeey Ashe yariyace Mai Arziki nadiga musguna Mata batare datasaniba wayooo Allah nacuci kaina nacuci d'ana yazu da a gidan d'ana take da gaba daya Wana Arzikin ya Zama nasa. a Ranta tace yazuma lokaci bai kureba zanyi duk yada zayi dangani tadawo gidan d'ana
Ummeey tace Abba bana bukatar komai daga gareku kugama min komai a rayuwata bazan tab'a biyaku iri d'awainiyar da kukayi daniba
Abba Wana dukiya takuce bazan karbi ko sisiba nabar muku bana bukata komai daga cikin
Abba Muhammad ne ya kaleta cikin mamaki yace kada kiyi haka Mamana bazamu dau ko kwadala daga cikin dukiyarkiba
A lokaci da Mahaifinki yake cikin halin matsi rayuwa bar karbi ko kwadalla daga cikin Wana dukiyarba bare yazu
Rokonsu Ummeey tadigayi akan surike Wana dukiya ama su Abba sukakin
Haydar ma rokonsu yake akan sukarba tuda ita tabar musu
Dakar Su Abba suka Amince nama Saida Ummeey taita kuka Tana rokonsu
Sunyarda zasu rike dukiyar ama bada gidaje da filaye Wanaka suce bazasu karbaba
Ummeey ta Amince da hakan ama badan Ranta yasoba Dan ita gani take Babu abuda zatayi dasu
Sanan tace Abba Dan Allah acikin gidaje inaso Abawa Gwogwo Halima da Gwogwo Asabe
Abba gidan da Yaya Muhammad keciki shima nabar masa
Dago Kai yayi cikin sauri ya sauke idanusa Akanta wani irin kallo yake Mata Mai cike da nadama yace Ummeey yazu duk irin abuda na aikata mikin har zakin iya min kyauta Mai girma irin Wana
Kallonsa tayi tare dafadin ya Muhammad kaifa d'an uwa nane Kuma yayana wlh kafin k'arfin komai a guna Zan iya malaka maka duk wani Abu dana malaka batare danaji d'ar a Rainaba
Tsura Mata idanu yayi Yana Mai jin haushin kasa tayaya akayi tunda baigane Ummeey itace mace data dace dashiba
Innallillahi wa,Inna ilaihir raji u nacuci kaina nasake reshe narike ganye narabu da yariya Mai tarbiya naje nadaukowa kaina masifa nabiyewa Son Zuciyata naki yarda da ZABIN da ABBANA yamin
Kallonta yake yanajin wani mahaukacin Sonta nashigarsa batare daya shiryaba a hankalin ya bude bakisa wada ya Masa nauyi yace nagode Ummeey hakika kincika Yar halak wace idan aka Mata Shari take sakawa da alkairi
Kiyafemin Ummeey hakika nacutar dake a zaman damukayi dake nak'utatawa Rayuwarki nazalinceki nazauna dake a gidana a matsayin Matata ama nakasa sauke nauyi da Allah ya dauramin
Nakasa kusatarki amatsayinki na Matata Ummeey idan har baki yafeminba basan Ida zansa kainaba hakinki bazai barniba a cikin Wana duniyar tudaga yazu hakiki ya fara bibiyata Dan Allah kiyafemin
Ummeey tace kadena rokona ya Muhammad nariga da nadad'e da yafema
bazan tab'a iya rikeka a Raina ba kakwantar da hankalinka komai yariga da ya wuce kaifa yayanane wada duk duniyarna bani da d'an uwa daya wuceka
Muhammad yace nagode Ummeey Ina mikin Adu,ar Zama lafiya a gidan Aurenki Allah yabaku zuri,a d'anyiba
kallon Haydar yayi Yana maijin radadin a ransa yace inatayaka murna Haydar kayi dace Mata Mai hakuri da tarbiya Dan Allah karikemin K'awata Amanna hawayene kekwokarin zubowa daga idanusa yayi sauri kau dakansa gefee
Murmushi Haydar yayi tare da fadin karka damu yayamu insha Allah Zan rikema kan'warka da Amanna
Gwogwo Asabe da Gwogwo Halima godiya suka rigayiwa Ummeey harda kuka farin cikin sana sukariga samata Albarka
Mama ne tace Ummeey kiyiwa Yaya Abdallah godiya da iri d'awainiyar dayayi dake tukina karama har zuwa girmaki hata kayan dakin shiyamiki da kudinsa
Ummeey tace tooo Mama kallon Abba Muhammad tayi tace Abba nagode da irin d'awainiyar dakayi Dani Allah ya biyaka da gidan aljannah
Murmushi Abba yayi tare da fadin Amiiiin Mamana karki damu ai nima mahaifinkine
Abba yace Mamana tashi kutafiko kada dare yayi muku a hanya
Narai narai tafarayi da idanu tace Dan Allah Abba kabari sai gobe inaso muyi bankwana da Mama
Abba yace wane irin bankwana zakuyi wada bakuyishi daba kee tashi kibi Mijinki
Matsawa tayi kusa da Mama tare da fadawa jikinta tasa kuka
Rarashita Mama tafarayi tare da Mata nasiha akan tabin mijinta ta zauna da Abokiyar zamanta tsakani da Allah
Sana shima Abba ya daura danashi itade Ummeey sai kuka takeyi a Ranta tanajin zafin rabuwar da zatayi da iyayyenata
Abba ya sanar da Haydar nada wata daya zasuzo Kano domin daukar Ummeey susadata da Mahaifinata
Haydar yace Allah ya kaimu lokaci kowa naguri yanayiwa Ummeey fatan Zama lafiya Mai daurewa a gidan Aure nata ama bada Momy da k'ya shi da hassada ya cika Mata zuciya
Suna shiri tafiya saiga Hauwa tashigo rugumeta Ummeey tayi tare da fara wani sabon kuka rabuwa da Aminiyartata
Dakar suka rabu kowanesu zuciyoyinsu cike da rad'adin rabuwa da junasu
Haydar ne ya bude Mata Motar tashiga shima shiga yayi ya tada motar zuciyarsa cike da farin ciki
Ummeey nagani sufara tafiya kuka tasa tanajin ciwo rabuwa da Iyayyenta
Jayota yayi jikinsa takwanta akan kafad'arsa a yacin gaba da tukin
Damisalin karfe 6 : 20
Suka inso cikin Kano Yana Isa gida Mai gadin ya wagale Masa gate
shiga ciki gidan
yayi parking fitowa yayi daga Motar zagayawa yayi