Showing 21001 words to 24000 words out of 37025 words
Chapter 8 - JININ ABBANA BOOK COMPLETE TXT By Zainab Habib Mom Islam.txt
yana cikin tunani ne ,yaji mutum ya fad'o cinyarsa , a zabure ya mik'e yana ihu , hankalin mutanen dake zazzaune ya dawo kansa , kowa sai kallonsu yakeyi , Beauty ce ta fito a zabgegiyar budurwa ,amma kamaninta basu 6ace ba , Bash besai ya zaiyi da rayuwarsa ba ,yasa hannu a ka kamar zaiyi kuka , beauty ko na cinyarsa gata k'atuwa ."
Cikin masifa ya yaye zanin daya luly6e zaninta , kofato ya hango wani ihun yakuma sawa yana cewa ku kuke ganinmu ba mu muke ganinku ba , kiyi hak'uri ni dama nasani ina tare da Aljana ne ,babu Wandaya kuma bi takansa shi kad'ai yake shirmensa , hawaye sha6e _ sha6e a idansa yaci kuka gashi koyaya idanshi yakai kan k'afar Beauty a tsorace yake , tunanin ya fara to tayaya ta shigo jirgi batare da tagama komai ba ......✍️.
Vote me on wattpad
Please share
♦️😭JININ ABBANA!!😭♦️♦️.
_Labari mai d'auke da tsan tsar zalunci cin amana dakuma nishad'i_
*Story and writing*
*By*
*ZAINAB HABIB*
_(Mom Islam)_
Zainabhabibu713 @gmail.com
Wattpad momislam2020
Whtsapp group. https://chat.whatsapp.com/CehHXDP6kjk9GTiqw3BVfk
Telegram
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w
_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
EPISODE 35 & 36
____ Da haka dai jirginsu ya sauka a Nigeria , driver ne yazo d'aukarsa , juyawa yayi yaga baiga Beauty ba , babu wani farinciki da zaiyi tunda yasan yana shiga motar zai ganta a ciki , driver ne ya d'auki jakar kayansa yasa a Booth , ya rufe , yana tada mota sukaji alamun kamar mutum ya fad'o Beauty ce keta dariya , Bash yarasa inda zeyi kawai yafara kuka , ga wani tsoro daya ziyarci zuciyarsa , driver ganin wanan yarinyar yasashi taka burki ya fice da gudu , Bash ne yace ”Idi kazo ka tuk'amu mu wuce ,ina Idi ya bazama ko tsayawa baiyi ba ."
Bash ne yaji mota na tafiya , zaro ido yayi yana salati , kafin ya tsalako , gurin zaman driver Beauty ta zauna ,tafara driving , Bash dai yariga ya suma babu nunfashi , driving takeyi tana dariya har ta iso gidansu Bash , tana horn taji shiru , ba'a bud'e get d'inba , sauka tayi tafara bubugawa kamar ba hanun mutum ba , kowa na cikin gidan ya tsorata , haka mai gadi ya fito ya bud'e get d'in , suna had'a ido da Beauty ta sakar masa murmishi , a zabure ya juya kansa dan , gani yakeyi idanunta suna yimasa kamar na mage , parking tayi a parking spice na gidan ta fito , gyara zaman d'an karamin hijab d'inta ta nufo cikin gidan."
Kowa sai kallonta yakeyi ita ko babu wanda ta kula ta shige parlorn momyn Bash , da ganinta momy tace ah y'ata barka , da fara'arta Beauty ta zauna momy ce takawo mana ruwa da lemu , abin mamaki babu abinda Beauty tasha , ta dubi momy dake kallonta tace ”Bash na cikin mota , daga haka Beauty ta 6ace , ihu momy tasa tana salati , wanan mutum ce kuwa ?" to in mutum ce ya za'ayi ta 6ace ?"babu mai bata amsa yasata fitowa waje cikin tsoro , bataga Beauty ba , haka taje ta bud'e k'ofar motar , ganin Bash a kujerar baya jiki a sandare yasata k'wala ihu , tana kuka , hankalin su dady ne yayo gurinta mutane suka taso kowa yazo ya lek'a cikin motar , dady ne yace ”shikuma mai yasameshi , momy takasa bada labarin wacce ta shigo mata hartace Bash na mota sai dai kuka kawai , dady ne yace ” wa momy ta Shiga motar su wuce hospital , a tsorace ta shige ko mayafi babu ,dady ya tuk'a motar , da isarsu aka wuce dashi d'akin gaggawa wato emergency , aka fara bashi temako , basu sha wiya ba gurin samun dai _ dai tuwar nunfashin sa."
Yau bikin Harun saura sati uku , shiri kam anayi ta 6angaren su , Basma sosai momy ta ke gyarata kasancewar taga angon nata tsaf tsaf , magugun guna na mata itatuwa ne su kankana apple ayaba da aya da dabino da sauransu momy na bawa Basma , musamman ma dataji za'a had'a Bash da wata bayan y'arta , Basma ta k'ara k'iba tayi kyau fuskarnan sai k'yali takeyi ga wani k'amshi da inka zauna kusa da ita kokuma ta zauna kusa da kai baza kaso tashinta ba ."
Asma'u kam ita ke gyaran jikinta da kanta bata jira Umma ta temaka mata ba , sai rawar kai , gashi bata ta6a ganin angon ba lol , ko number shi batadashi bare sanin ko inane gidan su , itadai tana gyara kanta ."
Mom ce ta dawo daga kasuwa , kaya masu gadi da drivers suke shigowa dashi , akwatuna ne set goma sha biyar , palorn Hajiya sukayi dashi , oyoyo Hajiya ke yiwa mom , cikin fara'a mom ta ce ”Hajiya na gaji wlh , kayan Hajiya tafara fitowa dasu masha Allah , gaskiya koni da nake rubuto muku duk abinda nagani ,hmm zan iya mancewa da wasu , akwatunan atamfofi daban akwatin gyaluluka daban haka ma na skirt shima daban na bra daban na ves daban na turaruka daban , kai barin barku haka ,dan kayanfa sunyi babu makusa , tundaga akwatinma zakasan kayan na manya ne."
Bayan 1 hour da zuwansu ,komai ya zama normal , aka sallamesu suka dawo gida ,Bash kam yariga ya tsorata , shi besan wanan wace masifa bace , tunda ya had'u da Beauty bashida zaman lafiya kodai dama tazo ganin bayansa ne ?"oho yadinga tunaninsa barkatai ."
*INDIA*🌹
Yau alk'awarin Emmanuel da dodo zai cika , gashi wanan ne na k'arshe ,yarasa jinin wa zai bada , gashi ya bada na mamanshi da na babanshi da jinin k'anwarsa dakuma na jaririn da mamansa ta haifa duk ya badasu , ga jaririnsa na gurin Bahija , yanzu kuma bashida wanda zai bada , misalin k'arfe 2 pm na dare kowa ya hallarci d'akin tsafi , shikam yazuba uban tagumi ta kansa dodo yafara , yau mukayi dakai zaka cika mana alk'awari , Emanuel ne yace ”nace muku Ku kasheni ko nace kusha nawa , cikin masifa yake maganar , tsawa aka daka masa ,shiru yayi yana maida nunfashi , dodo ne ya d'ago ,wani k'aton k'ok'on tsafi , fuskar Bahija ce ta baiyyana , daga inda mutanen suke zaune suna hango komai na cikin k'ok'on , cikin masifa Emanuel yace ”inko kukayimin haka bakuyimin adlci ba , zan fita a wanan k'ungiyar kuma koda yin hakan zai janyo mutuwata ."
Hango Bahija a cikin k'ok'on tsafi yayi ,tanata jujuya kanta tana cije baki , kuka Emmanuel yafara tare da cewa tur da wanan k'ungiya kuma sai kunyi nadamar yin hakan , babu wanda ya kulashi ,kuma duk maganarshi bazata sa su tsaida k'udirinsu ba , haka aka tashi taro ran Emmanuel babu dad'i komai ya birkice masa , direct offishin matakan tsaro ya nufa wato sojoji , yana kuka yana bada bayanin abinda ke faruwa , wani farin mutumi bature yace ”masa a inane zamu samesu , Emmanuel ne yayi musu kwatancen inda zasu had'u , sashi a motar sukayi suma suka shiga , abin mamaki da zuwansu sukaga gurin ya koma jeji."
Kallan kallo suka fara , sumadai sunsan akwai gidaje bila adadin a gurin amma gashi babu alamun anyi gini yanzu , Emmanuel ne tsoro ya kamashi yana tunanin hukuncin da zasu yanke masa."
Bikin Sumaiya da yaron k'anwar momyn ta ya matso ,yau saura kwana biyar , kyau kam amarya tasha dan kobatayi kwaliya ba tanayin kyau to inaga ranar bikin , yanzu kam ta hak'ura ta mik'awa Allah komai ta amshi za6in iyayenta , sosai suke zuba soyayya da saurayin nata mai suna Khalid , kamar masoyan da suka shekara."
Wani abin mamaki ashe beauty na d'akin Bash tana bacci tun lokacin da momy ta nemeta ta rasa , suna shirin shiga da Bash d'akinsa , suka hango Beauty na kwance tana bacci cikin nishad'i , tsabar tsoro momy sake Bash tayi a k'asa ta ruga da gudu tabarshi shi da dady , Bash ne yafara cewa "nidai nashiga uku bansan yazanyi ba ko wane lokaci aljanar nan na tare dani."
Ashe zancen zuci ya fito fili ,dady yaji duk abinda yace ”aljana ?"dady ya mai maita ,eh wlh dady , tsoro ne ya fara kama dady yace ”ai ance ljanu basuda k'afafuwa bud'e nata mugani , a tsorace Bash ya kalli dady dady ya kalli bash , dakewa Bash yayi yaje gurin bak'ar jallabiyar Beauty ya bud'e k'afarta , kofaton suka hango cikin tsoro dady zai zura da gudu k'ofa ta rufe , gashi ga Bash kuma ga Beauty aljana lol."
Bash ma neman gurin guduwa ya keyi amma babu hali k'ofa a kulle take , Beauty kuma na bacci , Bash yana tsoron yacewa "dadynsa wanan aikin ma Beauty ne ta farka tabashi horo , yaja bakinsa yayi shiru ...✍️.
Vote me on wattpad
♦️♦️😭JININ ABBANA!!😭♦️♦️.
_Labari mai d'auke da tsan tsar zalunci cin amana dakuma nishad'i_
*Story and writing*
*By*
*ZAINAB HABIB*
_(Mom Islam)_
Zainabhabibu713 @gmail.com
Wattpad momislam2020
Whtsapp group. https://chat.whatsapp.com/CehHXDP6kjk9GTiqw3BVfk
Telegram
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
*JININ ABBANA FANS GROUP*
*JININ ABBANA PANS (2)*
*WANAN PAGE 'DIN NAKUNE 🤙*
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w
_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
EPISODE 37 & 38
____ Mutane suka gani cike a d'akin , kuma duk sa'anin Beauty ne , da bak'ak'en kaya , tsalle suketa yi suna dariya , dady da tsoro ya gama kamashi ,ya ce ” kai Bash tashi waccan mai baccin , ido Bash ya zare yace ”dady wlh itace babbar su , dady na kallon Beauty ,yace ”ke tashi , beauty ce ta mik'e tana dariya , wanan dariya ba k'aramin firgita dady tayi ba , yaran da suka zagaye dady da Bash suka fara magana wata iri , suna cewa "baku kun iya mugunta ba ?daga kai harshi bakuda tausayi ,to yau zaku gane kuranku , kowa yazo ya fad'i abinda yayi ,inhar kunaso mu bud'eku ."
Jin shiru har dare yasa momy bubuga k'ofa amma shiru , ko motsin mutane bataji , number Bash da number dady bata shiga , hankalin momy ya tashi sosai ,tarasa ina suka shiga ,gashi d'akin Bash yak'i bud'uwa , tunani tafara kodai wanan aljanar tana d'akin ne ?"toshi Bash a ina ya samota , tattara zancen zucin tayi gefe ta nufi waje , driver ta hango zaune a takure kamar mai rawar sanyi."
Cikin tashin hankali momy ta k'arasa gurinshi tace ”Idi zoka nemo min malamin ruk'iya , cikin tsoro Idi ya kalli momy yace , Hajiya karfa inje garin nemo wa a kwashe ni , tsawa momy ta daka masa , hakan yasashi ficewa da gudu , tunda ya fita yaketa gudu har ya wuce anguwarsu ,amma baisan ya zoba , mutane sai kallonsa sukeyi ."
Pans kuzo muje mu taro Idi fa🤣.
Komawa momy tayi ta zauna a parlor tana jiran dawowar Idi , agogo ta duba har k'arfe shida na yamma shiru , tagumi ta zuba tace ”to shi wanan ina ya tsaya , lol niko ina gefe ina dariya Idi ya falle da gudu , mik'ewa tayi ta d'auko wayarta a bedroom , number wani malami da yake zuwa yimusu sauka farkon tare warsu a gidan , gwada number tayi , cikin rashin sa'a akace mata number bata tafiya , tashin hankali momy ta shigeshi , babu miji babu d'a , ga Idi ma shiru , rasa wazata kira tayi kawai ta zauna tadinga cin kuka gashi babu mai rarrashi ."
Bahija ce zaune itada anty da mama ,suna hira , yanzu kam jikinta yayi kyau ,washe gari da safe ta tashi da matsanancin ciwon kai tun ana ganin abin kamar ,wasa har takai ga tafara surutai da basuda kan gado , mahaifinta suka kira , "cewa yayi su kaita ,hospital , cikin gaggawa suka , kaita hospital , temakon gaggawa doctor suka fara bata , ciwo dai kamar wasa abin ya gir mama."
Bahija batacin abinci sai ruwa shima ruwan dak'yar yake tafiya mahai fiyarta ko tana ganin kamar mutuwa zatayi , ganin wata uwar rama da tayi. "
Yau kwanansu biyu a hospital d'in ,jiki babu sauk'i sai abinda ya dad'u , Allah sarki rayuwa , mutane sai zuwa gaisheta sukeyi , y'an uwa da abokan arzik'i ,duk wanda yasan Bahija to da k'yar zai ganeta , saboda tsananin ramar da tayi ."
Tun su dady da Bash na kuka , har bacci ya d'aukesu , sai sunfara bacci sai suji dariyaku , haka dai gari ya waye da asbha momy ta fice daga gidan tayi wani gida a mak'otansu , tunda take bata ta6a shiga gidan ba yaukan dole ta janyo hakan , shiga tayi da sallama , gidane madai daici sunada rufin asirinsu dai dai gwsrgwardo , da shigarta mata gidan ta shimfid'a mata tabarma ,bayan sun gaisa ne momy take tambayar matar ko tasan gidan wani malami nan kusa , akwai matsala a gidanta, matar ce tace ”barin yiwa malam magana ,momy na zaune matar ta shige d'aki ta fito tana cewa "bari malam ya shigo kiyi masa bayani , to momy tace ”tana jin jina lamarin gidan ta , bayan 5minutes wani mutumi ya fito da malun malun , ya nemi guri a can nesa da momy ,a tabarmar da aka shimfid'a masa , momy ce tafara gaishe shi danan yace ”tafad'i abinda ke faruwa , labarin abinda yafaru tabashi , malm ya jin jina wanan lamari amma baiyi magana ba ,dan haka ya d'auki Alq'uranin sa yace ”muje , momy na gaba malm na baya , gashi garin beyi haske sosai ba, haka malm ya kunna touch light , momy kam tama mance da batun fitila , haka ta bud'e get d'in suka shige , kai tsaye parlorn suka shiga , nuni momy tayi masa da hannu kaga d'akinnan , murmishi malm yayi yace ”to , momy komawa kan kujera tayi ta zauna tana maida nunfashi ."
Da shigar malam d'akin Bash yaga mutum uku a kwance , d'aya mace akan gado biyu kuma a kafet , zama yayi a kujerar da take gefe da gadon ya bud'e Alqu'ani yafara karanta suratul bak'ara , daga dady har Bash babu wanda ya motsa sai macen da tafara motsi da jikinta cikin tuhuma malam yace ”koma waye ya fito yanzu dan zan k'onashi , shiru babu mai magana , malam ne yaciga ba da karatun yana yarfa wani ruwa na adu'ar , Beauty ce ta mik'e da bak'ar riga tana dariya , tana cewa bazamu barsu ba bazamu barsu ba."
Malamin ne ya tsaya da karatun ya dubi Beauty yace ”ke wacece? cikin dariyarta da batada dad'in sauraro tace ”nima kamarku nake , ta tuntsire da dariya , malm dayake yasan ba mutum bace "ya cigaba da adu'arsa ,hak'uri tafara bashi akan yayi hak'uri , malm ko saurararta beyi ba yacigaba , zaki fad'amin gaskiya ko bazaki fad'a ba ?" Beauty ce tace ” kabarni zan yima bayani , malm bai gamsu zata fad'a ba ya watsa mata wani ruwa ,ihu tafara tana ya k'yaleta , tambayarta ya kumayi a karo na biyu ,me bayin Allahn nan sukayi miki kike cutar dasu ?".
Yau ta kama daurin auran Sumaiya , manyan mutane da dama sun halarci bikin , kowa kagani fuskarsa cike take da farinciki , Abbi ma farincinne shimfid'e a fuskar sa , haka Ammi sai albarka suke sanya mata ,gidan ango duk da dai tuwona miyata ne ,sunyi rawar gani sosai akwatuna set goma sha biyu , kuma shak'e da kaya , masha Allah amarya tayi goshi, hango Sumaiya nayi tasha bak'in lalle fuskar nan tasha make-up ga wani tsararen kitso da aka yimata , gaskiya ta had'u abinka da farare abin ba'a cewa komai , wayarta ce tafara ring ,sunan my sweetheart ne ke yawo a screen d'in wayar ,cikin sassanyar murya ta d'aga , kunsan marubuciyar taku da son jin k'wa k'waf hhh , ango ne yace ”my honey dafatan dai baki wahalar min da kanki ba , kukan shagwa6a tayi kamar yana ganinta tace ” sweetheart , bana jin cin komai yanzu ,oh my honey kinason wahalar min da kanki , wata irin dariya tayi da nima na dara hhh my fans dariyar fa ta masoya ce."
Ki fito please muje kici abinci , uhm uhm nikam bazan iya ciba ,okay to bari in aiko Shamsu ya kawo miki ,cewar Khalid salama sukayi kowa ya ajiye waya, k'awayen ta ne keta yimata tsiya wai tafiya shagwa6a Khalid zaiyi , fama ,lol niko nace ai mace babu shagwa6a to ai babu kanta 🙈 kuka tasa tana shure shure , tin tsirewa da dariya suka tafa."...✍️.
👏👏👏👏👏👏👏👏
*GASKIYA MASOYANA*
ina alfahari daku da kuma soyayyar da kuke nunamin wlh ina gani kuyi hakuri yanzu aiyuka ne sukayimin yawa , ina neman Adu'arku please kuyimin adu'a Allah ya rabani da abinda nake tare dashi lpy , kuna rai na, nagode da nuna soyayyar.
Please share👏
Vote me on wattpad
♦️😭JININ ABBANA!!😭♦️♦️.
_Labari mai d'auke da tsan tsar zalunci cin amana dakuma nishad'i_
*Story and writing*
*By*
*ZAINAB HABIB*
_(Mom Islam)_
Zainabhabibu713 @gmail.com
Wattpad momislam2020
Whtsapp group. https://chat.whatsapp.com/CehHXDP6kjk9GTiqw3BVfk
Telegram
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w
_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
EPISODE 39 & 40
____ Mama da Anty na hango a hospital , suna fitowa daga d'akin da aka kwantar da Bahija , kuka Anty takeyi sosai , juya kai mama