Showing 30001 words to 33000 words out of 37025 words
Chapter 11 - JININ ABBANA BOOK COMPLETE TXT By Zainab Habib Mom Islam.txt
biyu , kuma ya hana momy zuwa gurin bikin taci kukanta har tagaji, wanan d'akin da Harun yata6a jin dady na waya harya tsorata ,acan yake kwana yanzu baya wuni a cikin gidan gashi yanzu momy tarasa gane kan dady itadai tana ganinsa yana hidimarsa batasan me yake aikatawa ba ."
Malam ya tashi da amai da gudawa , tun ana k'irga ledar ruwa har Umma ta zubawa sarautar Allah ido , gashi duk kud'in da Asma'u ta bar mata sun k'are gurin jigilar magani , Umma tarasa wane guri zataje nemo kud'i , ga malam kwance ya kwanta a asibiti , sunfito babu kud'in magani ga yaron Asma'u na kashin hak'ori ,ya rame sosai damuwa ta taru tayuwa Umma yawa ,wani lokacin ta zauna a d'aki tayita kuka wani lokacin tai alwalah takai kukanta ga Allah."
Yau da bikin Sumaiya sati biyu kenan tayi fari tayi k'iba sosai , Khalid ne yashigo da 3 quarter yana rawa yace ”my princess tauraruwa zomuyi rawa ,d'agata yayi yana juyi yana rawa da ita ,suka hau dariya , albishirinki, sumaiya ce tace ”goro , nabiya mana makka , a zabure Zumaiya ta mik'e tace ”dan Allah fa ,suka sake kid'a suka fara rawa , hhh kowa na nuna iyawarsa , saida suka gaji sosai sanan suka baje a kan capet suna hutawa , da gudu sumaiya ta mik'e tayi bedroom d'inta , toilet ta shige rik'e da bakinta , wani amai ne ya taho mata ,Khalid ne yabiyo bayanta da sauri ya rik'eta ,meke faruwa ne ?"a wahalce tace ” amai saida tayi aman mai yawa zata zauna a toilet d'in Khalid ya wanke mata baki ya fito da ita ya kwantar da ita a gado lulu6eta yayi da blanket , ya zauna kusa da ita ya zuba tagumi kamar ba d'azu suka gama kwasar rawa ba ."
Wani jeji suka shigo mai cike da bishiyoyi iri iri bakajin k'arar komai sai na tsuntsaye , Zuby da Asma'u ne tafe sai nunfar fashi zukeyi , Asma'u da tagaji tace ”zuby nagaji mukoma zare ido Zuby tayi tace ”wlh babu inda zamu koma muzo har nan d'in kice mukoma tabb , wata tafiyar mai nisa suka kumayi ,jiyo wani irin gurnani ne zai tabbatar maka da anzo gurin hatsabibi , ya Allah ka tsare mana zuciyoyinmu, wata mahaukaciyar dariya Asma'u ta jiyo dan Zuby komai na gurin ba bak'onta bane tasaba , Asma'u ce ta k'ank'ame Zuby a haka suka k'arasa gurin , da zuwansu boka yafara yare ,Asma'u ko tana ganin kamaninsa sai da ta tsorata , kanshi gashi ne a murd'e ga wasu uban wuri daya rataya a wuyansa k'afarshi kuwa ganyene a d'aure ga layoyi , zama sukayi a gabansa Zuby tafara yimasa kirari ,washe bak'ak'en hak'waransa yayi yace ”inajinku meke tafe daku ?"dukda aljani firsus ya bani labari zanso ji daga gareku ...✍️.
Please share👏
Vote me on wattpad
♦️♦️😭JININ ABBANA!!😭♦️♦️.
_Labari mai d'auke da tsan tsar zalunci cin amana dakuma nishad'i_
*Story and writing*
*By*
*ZAINAB HABIB*
_(Mom Islam)_
Zainabhabibu713 @gmail.com
Wattpad momislam2020
Whtsapp group. https://chat.whatsapp.com/CehHXDP6kjk9GTiqw3BVfk
Telegram
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w
_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
EPISODE 49 & 50
___ Asma'u ce tace ”so nakeyi a hanasu zaman lafiya kuma , matarshi ta zamo kamar dodo inya kalleta , wata shu'umar dariya boka yayi yace ”karki damu komai zaiyi dai dai , kud'i Zuby ta mik'a masa ya mik'o mata wata laya bak'a , yace ”wanan ki hak'a rami ki sata a ciki , ki d'ibi tafasashen ruwa ki kwara a gurin , ya shek'e da dariya ,kana yace ”kowa bazaiga kamaninta ba sai mijinta , kutashi ku ficemin ."
Da baya suka fita har suka wuce gurin bokan suka kuma tafiya mai nisa ,sanan sukazo gurin motarsu , farinciki fal zuciyar Asma'u ,amma a k'asan zuciyarta tana tunanin , shirinta na gaba akan Bash ne , suna tafiya cike da nishad'i , suka tsaya a wani katafaren gurin abinci , I scream suka buk'ata tare da sauya salon yangarsu , wasu mazane suka taho da alama suma y'an yine , zama sukayi a nesa ta kujerunsu , suna aika musu da murmishi , Zuby ce ta kashe musu ido d'aya tare da cewa hi d'ayanne ya taso yana washe hak'ora ya kamo hanun Zuby ,shikuma d'ayan ya rungumo Asma'u , wata galleliyar mota ce tai parking a gefen titi ."
Wasu mata na hango guda biyu , sun fito daga motar ko wace da glass no respect a idanta , direct gurin su , Asma'u suka nufi gasu jibga jibga , wani wawan mari ta wankawa Zuby d'ayan ta cakume wuyan Asma'u , nanfa kokawa ta 6arke aka had'a harda mazan ana kaimusu naushi , da 'alamu dai matansu ne shiyasa sukayi muk'uss."
Zuby taja hanun Asma'u suka shige mota da uban gudu sukahau titi , sunyi tafiya mai nisa suka iso gidan , mai gadi najin k'arar motar ya mik'e da gudu ya bud'e get , a guje ta shige ciki , goshin Asma'u na tsiyayar jini , cikin tashin hankali Zuby ta kama hanunta suka shige ciki , doctor ta kirawo yace ”gashinan zuwa , bai jimaba ya iso kasancewar baya 6atawa Zuby lokaci a gunta yana samun kud'i sosai dan ha r ciki yana zubarwa hakan yasa Zuby batada wani doctor sai shi doctor Sameer kenan babanshi babban likita ne Allah ya yimusu arziki sai dai yanada auri saki , kuma duk matar da ya aura bata aihuwa , haryanxu Allah bai bashi ba , shiyasa ya d'au alwashin zubarwa da mata ciki subhanallh 😥."
Yana zuwa ya wankewa Asma'u ciwon yabata magani ,Zuby ta biyashi yai gaba , gani nayi Zuby ta mik'e a razane tana duduba jakarta , zuge zip d'in tayi naga tana zaro ido cikin firgici , kardai na yarda layar nan a gurin fad'a , nashiga uku , in Asma'u ta sani nasan bazata koma ba , tayi dube duben harta gaji bataga laya ba , hankalinta ya matuk'ar tashi ."
Malam ne ya shigo da tabarma a hanunshi Alhmdulilh yaji sauk'i sosai , yaron ma ya warware , Allah cikin ikonsa ya yalwata masa acikin almajiran da yake koyarwa wani ya bud'e masa shago a k'ofar gidansa , yana saida su shinkafa wake madara sugar da sauransu , cikin sati biyu Allah yakuma buk'asa shagon yanzu kam Umma hankalinta yafara kwanciya ba kamar da ba tayi k'iba sosai ta murmure , shima jaririn yana samun madara akan kari."
Tunda Emanuel yakai report , gurin jami'an tsaro suka kamashi suke gana masa azaba , sunyi neman abokan harkar tasu sun rasa , kasancewar suna had'awa da tsafi , shiko gashi a hanunsu bashida sukuni har sai ya fad'o musu gaskiyar inda abokansa suke , yayi kukan yayi rok'on ya rantse amma duk a banza ."
Zaune dady yake a d'akinsa na sirri ,ya rufe ko ina babu haske wani jan abu nake hangowa dishi dishi ko meye oho ...
Sumaiya da Khalid ne suka nufi hospital , test akayi mata da saurnsu , likita ne ya mik'awa , Khalid hannu yace ” kyakyawan albishir kakusa zama baba , matarka na d'auke da cikin 2 weeks , tsalle Khae ya doka dama shida matar tashi ba baya ba gurin rawa yana yiwa doctor godiya , d'akin da ake k'ara mata ruwa ya nufa , saura kad'an ya k'are , bud'e idanta tayi tace ” Prince K nagaji da kwanciya ,ta kashe masa ido , oh pans kuzo mud'au darasi kullum canzawa kansu suna sukeyi 🤔shafo cikinta yayi yace ”baby ka huta sosai karka wahalar da momy , Sumaiya bata gane me yake nufi ba tace ”baby kuma ¿"eh a cikinki ba ,dariya tasa ta 6oye fuskarta cikin tafin hanunta , Khalid ne ya dubeta yace ”kunya ko , zaki sani ,yanzu mekikeso kici ?" cikin shagwa6a tace ”wainar fulawa ,tuntsirewa da dariya yayi yace ”to menene hakan ?".
Misalin k'arfe biyar na yamma suka bar hospital , aka dawo gida ,abu kad'an Khalid yayi Sumaiya zata shagwa6e fuska , yanzu dai tunda Sumaiya tafara laulayi , shi kad'ai ke rawarsa tana dariya , yau befita ba kasancewar lahadi ne yana kitchen gimbiya na kan doguwar kujera tana ganin girkin , awara sukayi ko ina yayi biji biji , Khalid kuwa yakoma abin tausayi dan hanunshi zuwa fuskarsa duk k'ulin awara , gashi Asma'u tak'i sa hannu sai dai tadinga cewa haka zakayi , harda aiken mai gadi aro musu abin tata ,haka dai sukayi awarar da tsami gaye hhh , a fagen suya , Khalid ya yarfe hannu yana shirin fita ,Asma'u tasa kuka tace ”wlh inbaka soya minba zanta tsalle inta tsalle kumadai kasan doctor yace ”banda aikin wahala harsai cikin ya girma ko ?"da sauri ya k'araso ya rik'eta yana am sorry my princess zanyi jeki zauna , an sa a tirai an yayyanka , aka sa mangyad'a a wuta aka zuba ruwa a roba da gishiri da maggi , ya fara d'iba yana zubawa , wani tsalle da man yayi sai a k'afar Sumaiya da gudu ta mik'e tafara kuka tana tsalle."
Hankalinshi na gurin suya yace ”dan Allah kidena tsalle kiyi hak'uri , zama tayi tana fifita k'afar ,da Khalid yazo yaga k'afar gurin ma kad'an ne babu dai halin yin dariya ne , tasa masa kuka , yana kwashe kaskon farko ta kwashe a plet , tasa yaji , Khalid ne yace ”wlh Sumaiya bakida.... bai k'arasaba Sumaiya tafara bubuga k'afa tana cewa toni ba mai ciki bace ? dole fa kadinga lalla6a ni wlh ko indinga tsalle , shidai Khalid ya gaji sosai yana kwashe kasko na biyu ya kashe gas d'in ya kwashe a plet ya fice , tana zaune , takusa cinyeta tana jiran ya kwashe yakuma zubo mata ,da sauri ta bishi ,ina harya kulle k'ofar da key , dole ta koma kitchen tacigaba da suya."
Tanayi tana dangwala da yaji , shiko Khalid wanka yayi ya canza kaya , ya shafa mai ya sanya hula da turarensa mai d'aukar hankali ,ya fito kamar bashine mai aikinnan ba , kitchen ya nufa ,samun Sumaiya ta kuk'e tana suya ,k'unshe dariya yayi yace ”mom twins ya aiki tare da sunkuyawa ya shafo cikin ,lumshe ido tayi tace ”to inakuma zakaje ?"maida mata maganar yayi kamar inda tyi masa a shagwa6e , uhm zani gurin Ammi ne da Abbi ,in gaishe su....✍️.
Please share 👏
Vote me and follow me on wattpad
[26/02, 6:13 am] Mom Islam ce💃: ♦️♦️😭JININ ABBANA!!😭♦️♦️.
_Labari mai d'auke da tsan tsar zalunci cin amana dakuma nishad'i_
*Story and writing*
*By*
*ZAINAB HABIB*
_(Mom Islam)_
Zainabhabibu713 @gmail.com
Wattpad momislam2020
Whtsapp group. https://chat.whatsapp.com/CehHXDP6kjk9GTiqw3BVfk
Telegram
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
________________________________
*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com
https://www.youtube.com/channel/UCXPmzqpUDDjUfBUkYwadf4w
_*Ku danna mana subscribe kana da kararrawar sanarwa mu gode.*_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
EPISODE 51 & 52
____Yau satinsu Harun biyar , Basma tayi kyau ta k'ara haske ga kumato lol , tafe suke a mota itada Harun zasuje gidansu momy , da isarsu ,yayi horn mai gadi ya bud'e musu , washe baki idi yayi yace ”kaga angon dariya Harun yasa lokacin da ,yake fitowa a mota , Basma ma tafito , tana sanye cikin shadda maroon color da wani tsararen aiki wanda rabi shine a jikin rigar , gyalen a k'afad'a ta yafa , hakama Harun shima kalar shaddar ce a jikinshi , kai tsaye part d'in momy suka nufa , tana zaune a parlor tana kallo , ganin su yasata fad'a d'a murmishinta , tace ”amare barka da zuwa , tana mik'owa Basma hannu alamar tazo , zuwa kusa da ita tayi ta zauna ,cikin girmamawa suka gaisheta , harunne yace ”dady nanan kuwa ?"eh momy tace ”lokacin da take mik'ewa , yana part d'inshi , okay Harun yace ”barin lek'ashi , please Basma ki jirani in sanarwa dady na , hanyar sashen dady ya nufa ,da isarshi d'akin , yajiyo wata mahaukaciyar dariya had'e da maganganu wanda k'wa k'walwarshi bazata d'auka ba , cikin zafin rai Harun ya fara bugun k'ofar dady yana gurnani na 6acin rai ,k'ofa dai tak'i bud'ewa dady yana surutansa da alamu waya yakeyi."
Momy ce ta fito a guje ta rik'e Harun tare da cewa meke faruwa ne my son naganka haka ,babu magana Harun ya ture momy gefe idanunsa sunyi jawur alamun 6acin rai , wani duka da yakaiwa k'ofar ne yasa bud'ewa , momy na gefe ta mik'e ta share hawayenta ,ta wuce parlor taja hanun Basma suka wuce bedroom d'inta , tinkarar cikin d'akin da baka ganin komai sai duhu , babu haske a parlor , haka yadinga shiga yana gurnani kamar zaki , d'akin da yakuma jiyo magana a karo na biyu ya tinkara , hango dady yayi da bak'in kaya a jikinshi da jan k'ok'o ga wani mutum ,k'waran gwal da alamu ba yaro bane ."
Harun ne ya cakumo wuyan dady , tare da buga kansa a bago yace "wlh ko ka kasheni ko in kasheka na rantse da mahalicci na sainaga bayanka ina mahaifina yake ?" Dady ya shek'e da dariya yace ”oho kabani ajiyarsa ne ?"wanka masa mari Harun yayi tare da cewa wlh yau zan kasheka kokuma na kasara ka dan bakada amfani bkada tausayi bakada imani , meyasa zaka kashemin ubana , kabarni maraya , uwata kuma ka rabata da mijinta mezakaje ka cewa Allah, yana kuka yana jijiga dady , shiko dady tsabar ya jigata layi ya fara yana cewa tsaya zan gaya maka , yayi dai _ dai da shigowar momy d'akin idanunta sun ciko da hawaye , batace komai ba itadai tana kallonsu , Harun ne yaja dady ,yace ”kai ka turo aka kashemin mahaifina ko , wani matsanancin kuka Harun yakeyi mai cike da tausayi , dady ne yace ” YUSUF!!!!....wani mahaukacin kud'i ne ke zubowa daga bakin wanan k'waran gwal d'in , zaro ido momy da Harun sukayi tare da rufe baki da hannu ."
Innalilahi wa ina ilaihirraji'un yanzu dady rashin tausayi da imaninka harya kai ka maida mahaifina dukiya , dady ko a jikinshi , kukan kura Harun yayi yafara jibgar dady yana kuka yana kalon abinda aka kira kud'i ya zubo, da sauri momy ta fito parlor ta d'auki wayarda data ajiye akan kujera tafara lalubar number mom , cikin sa'a number tashiga , as.... wani mari taji an wanketa dashi cikin kid'ima ta juya dady tagani , d'aure da hannaye ,fitowar Harun ne yasata komawa bayansa , momy ce takuma kiran wayar mom , cikin sauri tace ”wlh kuyi sauri kuzo kuga abin mamaki ,kuyi sauri ta k'arashe zancen da kuka mai cin rai , Bash ne yashigo sanye da doguwar riga jallabiya , gurin mahaifinsa ya k'arasa daya ganshi a k'ulle, wani wawan mari Harun ya kaiwa Bash , daganan fad'a ya sauya gashi dady babu halin temako duk Harun ya d'aureshi , kuka sukaji na wata murya wacce bata gidan ba , Basma ce raku6e a gefe tanata kuka ."
Momy bataso fitowar Basma ba amma aikin gama ya gama tunda taji komai kuma taga komai , shigowar mom da Hajiya da Alhaji yasa kowa maida hankalinsa gurinsu , amma banda Harun da yaketa kaiwa Bash duka ba ji babu gani ,Alhaji ne ya k'araso a fusace ya wanke Harun da mari mom ma ta k'ara masa , kukan kura Harun yakumayi a karo na biyu ya cakumo dady idanun Harun sunyi ja kamar gaushi ya turashi , d'akinsa yana cewa , ka nuna musu wulak'ancin da kayiwa mahaifina , yana kuka yake maganar , dady da zuciyarshi a halin yanzu ta bushe babu tsoro a cikinta yace ”bazan fad'a ba , Harun na marin dady Alhaji na marin Harun cikin fushi momy ta k'araso tace ”Alhaji bakasan dalilin kiranka ba ,dazakazo kana dukansa wlh MUNTARI shine abin duka."
Hanun mom momy ta kamo suka shiga d'akin dady , itadai mom na biye da momy wani d'aki suka shiga mai komai na cikinsa ja , hango k'waran gwal mom tayi ,momy ce tayi mata nuni da hannu , momy tace ” YUSUF!!! mom taga kud'i yana zubowa daga bakin abin , cikin firgici mom ta fice da gudu , Alhaji ne yayi nasarar kamota saboda yasan ,halinda zata shiga bata iya kallon 6acin rai , cikin surutanta , tace ”wlh shine ya kashemin miji kuma bazan barshi ba , gida ya kacame da tashin hankali , ga Basma na kwance zazza6i mai zafi ya rufeta , Bash tunda ya fita da gudu bai dawo ba ,ga mom tanata surutai momy kuma na kuka ,Harun na shirin kaiwa dady naushi Alhaji na tareshi ."
Hango Bash sukayi a hanun wata budurwa , dady na ganinsu ya sunkuya da niyar guduwa yaji an cafkeshi , budurwar tace ”dama nace ”saina tona asirinku ka fad'a da bakinka waye ya kashe mahaifin wanan yaron ,Bash da yasami Halin guduwa gurin momynshi yace ”BEAUTY!!! karki k'ara danganta mahaifina da wanan bak'in lamarin , yana rufe baki yaji an shak'oshi , baiga kowa ba yasashi , zaro ido tare da rik'e wuyan yasan wanan aikin na beauty ne."
Dady dai yak'i amsa lefinsa , dan haka Alhaji ya kira police , suka wuce dashi mom da Harun da Hajiya da tunda tazo batace komai ba sai kuka da takeyi ,suka nufi mota Basma dake bacci tsabar zazza6i ta fito tana rawa sanyi ta shiga mota ,duk cikinsu fuskar su babu wal wala."
Sumaiya na kwance tana bacci, Khalid ne ya shigo da cokali da plet a hanunshi , had'awa yayi yafara ganga , dan dole Sumaiya ta tashi tana mita , Khalid na dariya yace ”oh ashedai babu dad'i ,jiya nadawo na gaji sosai inason hutawa kika isheni da kuka kikace sai na