Showing 3001 words to 6000 words out of 26460 words

Chapter 2 - ZURFIN CIKI book 1 Complete by halima Abdullahi K Mashi .pdf

ba ta laminta ba, don kuwa kowa yasan
mahaifiyar sahura gun masifa. sanna sahurace ta
gajeta. aminu sai ya watsar da mgnn auran
gabaki daya har tsawan lkc. sulaiman yanata
roqan tsohuwa ta amince, dan ya lura aminu yayi
nisa. Ba yadda tsohuwa ta iya, dole ta amince,
aka sha biki ta tare gidan aminu. mai hali dai
baya fasawa, dan sahura batasan hulda da
suwaiba da surukarta, gashi daga kawota ko
2mth bata yiba ta kama fada da yan unguwa. a
cikin 3yrs sahura aka samu ciki. lkcn sulaiman ya
samu xiyarta qasa mai tsarki shida tsohuwa dan
sauke farali. sunyi addu'a allah ya bashi xuri'a
shida aminu.suna durowa gida suka samu lbrn
cikin sahura, murna a gun sulaiman tamkar
matanshi ne keda cikin.lkcn haihuwa tahaifi da
namiji murna gun yan uwa biyu ba'a magana,
anyi shagalin suna inda yaro yaci sunnan mahai
finsu wato idris shine suke kiranshi abba. Sannan
Ahaji Sulaiman ya biyama qaninshi kugeran
makka daga nan ne aka samu ahj Babba da ahj
qarami tun abba yana jariri ahj babba da
matanshi suke dawainiya dashi Sahura ba taso
saidai ba yan da xaitai da ita. domin alj qarami
na gama shirin fita xai saba shi sai gidan sai yayi
kukan nono ake maida shi, saidai tayi ta mitar
cewa anriqe mata yaro gidan,sahura dai in an
kawoshi bata isa taxoba dan tasan tsohuwa
tafita danja.duk da gugar xana da haibaici da

sahura take antayo ma suwaiba ta katanga ko
inta je gidan, baisa ta daina dawainiya da abba
ba. cikin hakane sahura wata ran sahura ta tashi
da xaxxabi mai tsanani da amai, shine taje asibiti
ganin likita ya tabbatar mata da tana dauke da
ciki.ko da ta fadama alj qarami ba qaramin murra
yayi ba ita kuma ta batarai, yace tunda abba
yana tafiyan shi ko ina ayaye shi. Da yamma
bayan yadawo kasuwa ya shiga gaida tsohuwa
shine yake gayamata xa'a yaye abba. tace
saboda me? ku barshi yayi 2yrs. sai yace ai uwan
tanada juna biyune, shi yasa, daman sha waran
da nakesan fada maki shine xanba yaya shi
kyauta har abada.tsohuwa tace kai amma ka
kyauta. Washegari da safe shine ma yayi ma
abba wanka tana kwance ya shirya shi, sannan
yace mata ta hada kayanshi duka dan xan kaishi
gidan ahj babba gaba daya. tace kana nufin kayi
kyauta dashi gaba daya? yace ea. tace tabdi!,ba
xai yiwu ba. infishari banxane kaxa tayi mana. su
wa yace kada su dage su samu nasu dan? nima
wahala nasha na haifi dan, ba shago na bude ya
fito ba....sam bai kulata ba, ya hada kayan yaran
ya fita. ya shiga gidan ahj babba da shi. dakin
tsohuwa ya shiga, nan ya samu ahj babba suna
gaisawa, yace yauwa, dama gurinka naxo yaya.
abba ya sauka daga jikin babansa yaje jikin ahj
babba da gudu, ahj ya dauke shi ya rungume. Ahj
qarami ya keqa ya kira suwaiba,ta shigo ta xauna
sai ahj qarami ya soma jawabi da cewa. tsohuwa
ina san ki xama sheda, yaran nan na ba yaya da
suwaiba har abada.ahj babba yasake rungume
yaran a jikinshi wani saban son shi ya ratsa shi.
idanshi suka kawo qwalla, suwaiba ta sa kuka
tace mun gode da wanna abu da ka yi mana.
Allah ya bamu ikon riqeshi da amana. ahj babba
yace bani da bakin da xan maka godiya, saidai
ince allah ya qara xumunci. ahj qarami yace haba
yaya dana nakane, saidai inasan abba ya xama
xaka kai daya. tsohuwa tace allah ya maku
albarka daku da yayanku, kaima allah ya baka
haihuwa. sukace amin. Sahura kuwa mijinta na
fita da yaro, itama ta xari hijabi ta nufi gidan

iyayanta, ta shaida ma mamanta cewan aminu
yayi kyauta da danta, kuma yaba mutanan da
basa qaunan ta. nan da nan uwar tahau masifar
cewan ba xai yuyu ba, ai dole ya baki danki.
shiko uban cewa yayi ai ikon sane, dan haka
baiga laifinsa ba dan yaba dan uwansa dansa.
sannan yace ,ta tashi ta koma. uwar tace ba xata
koma ba, ya ce ta xauna. bai sake bi ta kansu ba,
ya ci gaba da harkokinsa. shiko ahj qarami cewa
yayi baxai bita ba, lokacin da ya dawo ya samu
batanan, sannan bai fadama dan uwansa ba har
aka kwana. sukuma su suwaiba basu fahinci
sahura batanan ba dan ba hurda suke ba, saida
kukaxo cin abinki ahj qarami bai futo da kwanu
ba. sannan wan yace iyalin naka bata nanne?
yace yaji tayi, niko baxan bita ba. ahj babba yace
akan wani dalili ne? ahj qarami yace ban sani ba,
na dawo gida ban ganta ba. da safe ahj babba ya
tashi gaba sukaje gidan, sahura ba kunya tace
danta takesan ya dawo mata dashi, inhar yana
san xama da ita. Ahj babba yace, indai danta ne
xai maido shi. ahj qarami yace shi kuma inhar sai
an dawo da dan to ya haqura da auranta. kuma
na cikin ta ma inta haife shi xaixo ya ansa ya
qarama wansa inya so yaga yadda xatayi. duk
juyin da akayi yaqi yarda daga qarshe ma tafiyan
shi yayi. ubanta yace da ahj babba kaima jeka
yadda suka so haka xasu yi. satinta guda taka
abincin kirki gagaranta yake yi, ita kuma uwan ta
daina samun wani abu daga gun sahurar ke kawo
mata. dan haka suka yanke shawaran ta koma,
duk da haka saida ya shareta na kwana uku
sannan ya sakar mata. haka ta haqura saidai
tasha alwashin dun runtsi sai danta ya dawo
hannunta. sannan ta kulla sabuwan gaba da ahj
babba da suwaiba kuma tace duk tsohuwa ce
takitsa abin. abba yana samun kulawa tare da
tarbiya mai kyau.sahura ta haihu ta sake samun
da namiji aka samasa bashir, daga nan haihuwa
akai akai.. Tun abba yana qarami ya koyi wasu
halaiya na ahj babba. da farko, sallar
asuba,axahar, laasar, magrib da isha. ahj babba
kan tasa abba suje masallaci da rana kuma

umman sane ke turashi. ranan jumaa ahj na
dawowa gida dan ya tafi dashi. dan haka sallah
ta xauna ma abba da xaran lkc yayi xai fara shiri
yi. sannan ya iya sadaka dan dasunje yana bashi
kudi ya rabama almajirai ko yasa a asusun
masallaci. sai xumunci aduk lkcn da ahj babba
xashi xanfara yana tafiya da shi. ya tashi da san
iyayan shi matuqa bai taba sanin basu suka haife
shi ba. duk da cewan duk lkc da ya shiga gidansu
umman bashi takan cemai bafa umman kace ta
haifeka ba, nice na haifeka. riqonka muka basu. in
yaji haka sai yace allah kiyaye. sai ya baro gidan
ita kuma taita xakinsa. inya fadama umman shi
saitai murmushi ta rungume shi. ya ce aidai kece
ummata ko? ita kuma tace nice ummanka rabuda
ita kaji. abba yanada tausayi dan haka ya
taimaka ma ummanshi aikin gida. shekara sha
biyu ya sauke kur'ani.a lkcn ne ya gama pry ya
samu xuwa js1 Abba makarantan masu kudi ya
ke yi.ita kuma sahura duk yaranta ta batasu,
musamman bashir. duk lkcn da akace yaje
makaranta inyace ya gaji, saitace ya xauna kaje
gobe. ko ahj babba ya korashi sai dai ya labe
inya tafi shi kuma ya dawo. yafi san xuwa qwallo
ko shagon game. to hakama qannansa duk sun
dau irin tarbiyyan uwarsu. cikin haka wata ran
umman abba ta tashi da matsananciyan mura,
lkcn ahj babba yaje legos don taho da kaya. ahj
qarami ne yakaita asibiti bayan gwaje gwaje, an
gano ciki wata biyu da yan kwanaki. murna gun
ahj qarami tamkar yayi tsuntsuwa yaaje ikko ya
fadama ahj babba. suna isowa ya shiga gun
tsohuwa ya sanar da ita. nan take tasa kukan
murna.ita kuwa suwaiba tamkar mafarki, sai
kunya ta isheta. lkcn da ahj qarami ya fadama
sahura, sai cewa tayi um, bana an tabuka, ni dai
gani da cikin na shida amma sai yauxu ta samu
daya. ahj qarami yace kinji matsalanki, ke ba dai
kiji wani ya samu qaruwa ki taya shi murna ba,
sai dai baqin ciki. ta ja tsaki bakin cikin me
xanyi? tunda ni ga nawan. ciki mai laulayi
suwaiba ta samu, wanda duk abin da taci sai ya
dawo. wannan lamari ya daga ma ahj babba

hankali da abba, duk aikin gidan abba ke yi, ga
makaranta, ko an hanashi sai yayi.dan haka aka
dauko harira qanwar suwaiba, wanda mijinta ya
mutu. umman abba dai bata samu kanta ba saida
cikin yayi wata biyar. sannan ta samu sauki.lkcn
sahura tanada cikin wata bakwai, lkcn haihuwa ta
haifa mace, murna gurinta kamarme, dan sai
yanxu ta samu mace. safiyar talata umma ta
tashi da naquda, hankalin ahj da abba ya tashi
matuqa. duk da tsohuwa tana ta kwantar masu
da hankali, ranan abba ko makaranta bai jeba,
duk da san makarantansa, har suka dawo sallan
axahar shuru. ahj babba yace tsohuwa bari na
samo mota akaita asibiti. tace to. yana fita ba
jimawa ta haihu. ta santalo yarta mace mai
matuqan kama da ahj babba. tsohuwa tace da
abba,mai sunan mlm bi su ahj kace sudawo ta
haihu. dama harira tasa ruwan wanka lkcn da
suka xo ta fito daga wanka.nan aka wanke
yarinya yan barka sai xuwa suke amma sahura
saida aka. Sahura saida aka kwana sannan ta
shigo. ta dauki yar ta taba baki tace wannan yar
baqinqirin haka sai idanu daqwa daqwa. wata
mata da taxo barka tace ai wannan yar sak
abba,suna kama sosai. sahura ko kunya ta ce
basa wani kama da abba. da tasamu kyan abba
da tayi kyau, umma tayi ma matan alama da
haunu tai shuru. ranan suna taci sunan tsohuwa,
wato habiba, dan haka umma ke ce mata ummi.
abba yana ji da ita, saidai in yanasan tsoka nanta
sai yace dubeta ta ba ummata wahala, sai na
xaneki kika girma kika qi mata aiki. umma taita
masu dariya. tsohuwa ma naji da ita dan guta
take wuni. tunda ga kan ummi umma bata qara
haihuwa ba. abba yana aji uku suna qoqarin xana
(j.s.c.e)ya dage sai ahj ya saka shi shagon dinki.
ahj yace abba kabar batun dinkinnan ka tsaya a
karatunka. yace ahj nidai ina so kaga inna iya su
umma sun huta dakai dinkin su gidan laminde.
umma tace ka barshi yayi ahj sana an hannu ai
tanada dadi, kaga in ya gama bokon ba bai samu
aiki ba xaya riqe kanshi da sana anshi. ahj yace
to shi ke nan Ahj yace, to shi kenan, wane shago

ka ke san shiga inkai ka? yace, na can bakin titin
nan, in da kake saya na lemo. ahj yace shi kenan.
mafarin shigar abba gurin koyan sanaa kenan.
ummi ta taso da rigima, tsiwa tare da tsokana,
wanda yasa suka daina shiri da abba sam. abba
ne ya kaita makarantan boka da islamiya, kullum
yaje daukota sai ya raba fada ko ya bada hakuri.
umma kullum addua take fili da xuciya da lokutan
sallah, allah ya shirya mata ummi. ita kuma tata
kalan quruci yan kenan inta girma xata daina.
tsohuwa takance aini me sunana kingama min
komai, domin banasan ragon da, da in kai qara
gara akawo min na bada haquri. duk lkcn da tayi
wannan kalman sai sunyi fada da abba, dan cewa
yake ai dama tsohuwan nan tuni na ane kin daure
mata gindin ta siqa tsokanan yayan mutane. ita
fa mace ce ba namiji ba, shi kenan bata da aiki
sai dambe? tsohuwa takance batta tayi. tunda
ganan abba basa shiri da tsohuwa. ita kuma fati
yar sahura kamar ummace ta haifeta dan bata da
hayani. ummi kuma kamar sahura ta haife ta.
Wata rana abba ya ke cewa, umma da ace lkc
daya kuka haihu da umman bashir, allah cewa
xanyi kunyi canjin yaya. umma ta dube shi dan
me kace haka? yace sbd masifar ummi irinna
umman bashir ne, fati kuma ba ruwanta kamar
ke.dariya kawai take yi. kwanci tashi ummi ta
gama pry, lkcn abba yana shekaranshi ta qarshe
a jamia. yana karantan (mass comm)ne dan yana
san xama dan jarida. umma tasoshi da likita
amma yace baida raayi. tace kaga kai bakada
hayaniya abba aikin jarida na masu maganane.
yayi murmushi yace umma kenan. ummi ta samu
shiga aji daya a qaramar sakandare. maimakon
hankali abin nata sai gaba yakeyi. aduk lkcn da
tai laifi abba ya daketa sai tayi wani abun dan
tabashi haushi, da sunan ta rama. ahj babba ya
bude mai shago, tare da xuba mishi kekuna.
tsohuwa tace dakai wanine mai sunan mlm, saika
tafi da takwarana ta koya. abba yace ko a
kwafan shago na na ganta ba sai na karya mata
qafa ba. ummi ta murguda baki, sai daya tafi
sannan tace allah ya kiyaye inje wannan qaxamin

shagon nashi. Tsohuwa ta ce,"tafi can kema da
baki son ci gaba, in banda abinki da zaki kwantar
dakai ki koya in an tashi auranki basai a saya
miki keken ba. in kuma shi kika aura kinga
shikenan inya samo dinkin da yawa saiki taya
shi, ta ce"Allah ya kiyaye me xanyi da yaya
Abba,yayi ta cin xalina?ni bana son shi" Umma
dake gefe tana jinsu ta ce,"ke in kin samu kamar
Abban ma ai kinji dadi,shine zai ce mai zaiyi
dake? mara hali irinki." Ummi dai tayi shiru tasan
inta cika surutu kan Abba yanxun nan umma ta
doddoketa,umma tafi son Abba fiye da ita. watan
ramadan ya tsaya,duk daukacin musulmi sun
dauki azumi ranar da akai na uku Abba ya shigo
gida karfe daya saura. daga shago yake zaiyi
wanka yaje makaranta don yanada darasi karfen
biyun rana. Gidan shiru kowa na bacci,don haka
bai shiga dakin umman shi ba don baya son ya
tasheta ya shige bandaki. Da ya gama ya fito ya
nufi daki kamar ance ya kalli madafi, ummi ce
tsugunne tana cin abinci. ya tsaya yana kallonta,
dagowan da xatayi suka hada ido, yace ke! karya
axumin kika yi? ta toshe bakinta sannan nace
dan allah yaya kayi haquri. yace fito muje. ya
kaita dakinshi yasata gwale gwale. da xashi
masallaci ya kulleta ta baya. ya ce inyaso ki
tashi kafin na dawo, xan gane. yana fita tahau
binci ken abinda xata lalata mashi. ta ciro bidiyon
da yake kallo xata doka da qasa, sai taga kwalin
wani kaset tana kallon hoton jikin kwali, na
tsiraici ne. ta xare ido kicin mamaki, tace lalle
yaya abba, daman shi dan iskane? to kuwa xan
tona mai asiri. ta turashi cikin xaninta, da taji
motsin shi yana bude qofa sai ta koma inda take.
ya shigo ya kalle ta ya ce nasan kin xauna dan
kinga bananan. ya xauna bakin katifa, sannan ya
dubeta fuska daure. ummi meyasa kika karya
axumi? tace ba komai. yace tunda aka fara axumi
kike karyawa ko? tace yaune kawai yaya abba.
yace kinsan hukuncin wanda ya kasya axumi da
gangan. Tace eh an fada mana a islamiya, amma
mlm yace sai wadanda axumi ya wajaba akan su.
ya kalle ta cike da mama ki, a xuciyanshi yana

cewa, yanxu har yarinyan nan tasan akwai
wadanda axumi ya wajaba akansu? afili kuma
yace lalle ummi kina buqatan sa ido. dama
saboda bai wajaba akanki ba shiyasa kika karya?
to daga yau xansa maki ido, kuma xan fadama
umma ta sa maki ido. hakanan duk wani abu da
akeyi lkcn axumi an daina qyale ki, xaki ringa
sallar tarawi, ke har tahajjud sai kinyi shi. sannan
bayan axumi saikin rama wannan axumin. ya
xuba mata ranqwashi a tsakiyan kanta ,tare da
cewa tashi ki fita munafuka. daga dakinshi bayi
ta shige ta qara kallon kwalin, sannan ta maida
ta soke shi, tace sai na tona maka asiri. da dare
bayan angama bude baki, abba xai tafi tarawi ya
shigo dakin umma yace ina ummi? umma tace
gatanan kan kujera tayi sharkaf, wai yau taji
axumi. abba ya shiga ciki yana kallanta. yace
umma xaki yaudara ko yar rainin wayau, tafa
karya axumi daxu da rana na ganta tana cin
shinkafa. Yace shine kika xube wai ke kin sha
wuyan axumi ko? umma ta dube ta tana mamaki,
tace abincin da kike kinba almajirai da ma qarya
ne? ya dubeta yace biyu kenan ga larya axumi ga
qarya, xaki sani. tashi muje salla ko in ballaki.
umma tace allah ya shiryi halinki. abba yayi
dariya tare da cewa, kema dai umma yaxaki
amince da batun wai tac almajirai abinci, su basa
axumi ne, umma tace tunanin haka sam bai xo
min ba. saida ya sakata sahun salla, sannan ya
nufi gun maxa. bayan ya gargadeta da cewa in an
idar ta jira shi, inyaxo batanan sai ta sani. koda
aka idar da yaxo bata nan gurin ya kaure da
dambe da wata yarinya wai da suna sallah tana
bigeta. shine daga idarwa ta cakume yarinyan da
fada. bai tsaya sauraranta ba ya cire ta kalmi ya
shiga dukanta, sannan ya tasata xuwa gida. sai
da ta shige dakin tsohuwa sanna ya koma nashi
dakin. hakanan suka ta xuwa masallaci har
axumi yakai ashirin. Ahj ya kawo masu shadda
da leshi da atamfa na sallah ita da umman su
bashir da fati. ya suya masu takalma da mayafai,
abbane xai masu dinki, ran ummi baya son dinkin
abba, domin wanda take so bashi yake mata ba.

ta ce umma dan allah nidai a bani dinkina na
kaima laminde, yaya abba baya min ne kyau.
umma tace kije ki karbo da kanki. tace ai baxai
bani ba ne, xai dakeni. umma tace ai nafi san ya
dake kin, lamindan finshi dinki mai kyau tayi ne?
ummi tace nidai gara ita. tsohuwa tace ai banga
lkcn da mai sunan mlm xai faranta ma takwara
ba, kullun burinshi ya quntata mata. umma tace
tsohuwa ummi fa ba a mata gwaninta, inace dinki
in yayi mata har aro ake xuwa yi? ta dube ta
tace keda shine inya jiki kyayi biyu babu, yaqi
maki dinkin luma ya hana kayan bare kiba
laminde inga ta tsiya. qarfe dayan dare ya tura
dakin tsohuwa tana xaune a kan sallaya tana
addua, abba yayi murmushi. tsohuwannan kina
birgeni dama kina ibadan dare? ya kalla kan
gadonta, ummi taya dai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login