Showing 21001 words to 24000 words out of 26357 words
yayi mana amfani duk matan ,ajinmu da suka san ciwon kansu to Meye dalilin da zance na tsane ka aa halayyar ka ra,ayin kane kuma kaga zaka,iya da,ace malam bashi da kamun kai ai gara a ce yana da tsarewa .
Hmm Affanan na gode to wani hali nake da shi wanda matan ajinku suka koya ki gayamun zan gyara ko ta dalilin ki dan Allah ki sanar dani ko yaya ne koda shine ɗabi,a na zancire shi daga raina in Sha Allahu.
Yawan tsarewar ka shine muka koya babu wanda ya,isa a cikin malamai ko ɗalibai wani ya kawo mana zancen banza ko tawani fanni koda kuwa acikin malamai ne zamu taka mishi burki saboda karatu muka zo kuma shine makasa a gaba to kadai ji .
Amma ai ku mata da fara,a ,a kasan ku ke yanzu irin mai halina shi kikafi so mara fara,a wanda baya dariya kullum cikin ɗaure fuska gashi da ra,ayi shine kike muradi"ni banceba nima irin ra,ayin nake da shi .
Kice ra,ayin mu yazo ɗaya kenan zamuyi zama na amana tunda kowa yasan halin ɗan uwanshi
Murmushi yayi kawai yayi shiru
"Gashi ka duba sai gobe sai in karɓa in ka duba "bari in duba biyu sauran kuma in nayi zan kiraki in gaya Miki in yayi to in baiyi ba shikenan karɓa yayi ya duba duk abu ne mai kyau amma dole ya bata wahala ko dan yasamu hanyar da zasu dinga gaisawa.
Ya dade yana nazari kafin ya dago
Ita kuwa tana ta danna wayar ta tana murmushi tanajin daɗi har aka kirata a waya ta ɗauka tana waya.
"Mommy yaushe zaki dawo nifa kadaice ya kamata kudawo nayi missing naki a kwai wani labari da zan baki jibin inazuba ido ki gaishe mun da Inna Amina kice ta baki abun daɗi ki kawomun nagode .
Tunda ta fara wayar ya zuba mata ido har ta gama wayar .
Ince wani abu Affanan
Shiru tayi sai cewa yayi amma ke auta ne a gidan ku,ko saboda shagwabar ki tayi yawa zanje gidan ku,in cewa mommy zane ki zata dinga yi kina yimun rashin kunya .
Dariya tayi amma mommy bazata yadda ba wallahi saboda tasan wacece ni kuma tasan mezanyi kawai sharri phone stone .
Dariya yayi
Shima dariya yayi yace gashi duk basuyi ba ki kawo wani a kan Chemistry kuma dan Allah ki kawo abu mai kyau tunda kinfi gane ,abun da ya dace hakan za,ayi amma a kwai ɗaya zan duba zan gaya Miki bani number ki,cikin hikima ya karba yayi godiya sosai kuwa har ta fice yau yafi kowa farin ciki sosai duk wanda yasa shine supervisor ta ya taimaka mishi sosai kamar yasan halin da yake ciki kuwa shine ya tabbatar da hakan cikin natsuwa yayi aikin shi yau kam babu wani tunanin da yayi.
Wallahi abun da nake ji a kan Affanan shine naji a lokacin da nafara son Salma in dai kuwa haka ne wallahi da kuwa ya dace sosai dan ita ce irin kalar matar da nake so amma ba zai taba yadda yayi ganganci irin yadda ya sakewa Salma ba.
Ko yaya ne
Affanan
Lokacin da ta fito su kausar suna jiranta gunsu ta nufa suka tafa"ai daman nagaya muku zan sha wahala sosai kuma mu,uku ne fa yan group ɗin gashi dani suka dogara amma yace baiyi ba kubar malam zan rama karku da mu albishir mommy jibi zata dawo ku tayani girki dan Allah jibi a gidan mu zamu kwana nida kaina zan shirya musu abinci.
"Karki damu zamu zo mutaya ku in sha Allahu yanzu kam muwuce in sauke ku sai in fadawa gidan ku ,a barku ko ya kuka gani duk kansu shiga mota sukayi gidan su kausar suka fara zuwa sai gidan su Maryam a gajiye ta shiga gida mai gadi ya bude mata suka sha hira malam Dauda ya,iya bada labari shi yasa mommy da Abban ta suke zuwa su zauna har da Affanan suta hira ranan Lahadi ko,ina yake shiga a gidan wani zubin a falon mahaifin Affanan yake ƙaryawa ga tsafta ga kuma iya magana da bada shawarar da ta dace suna alfahari da shi shine ke karawa su Affanan karatun qur,ani har mommy da Abban babu abun da basayi tundaga kan sira Tauhidi fikihu ta,azeef huruf ko wanne yisukeyi babu wani girman kai mazan unguwar da basuda taurin kai suma zuwa suke yi .
Salma
Cikin Salma bai wuce wata biyu da sati biyu ba amma babu cikin da ta tsana irin wannan bata shiryawa haihuwa kwana kusa ba wai tasha wahala sosai a kan cikin nan tun safe ta shirya ta nufi asibiti doctor fa,iza ta samu suka gaisa kawarta tane da sukayi karatu a waje Ingila tun suna makaranta suke mutunci sai dai kowa da abun da ya karanta ta ɓangare da dama .
Fa,iza ra,ayin su yazo kusan iri daya duba ga irin gidan da suka fito kowa tana alfahari da ilimin ta sosai da kuma abun da ya dogara da shi .
Doctor bakwa so a mutu ba kwaso a rayu
Salma Kabir Yusuf yau kece a nan kice ina da babbar ba kuwa ya dalibai kuwa ya fama da koyarwa nikuwa ba zan,iya ba "nima kuwa bazan iya aikin kiba ko kaɗan nagode..
Nazo gunki Fa,iza Usman Tonga ne a kan wani al,amari ina son zubar da cikin jiki na ne wallahi ban shirya haihuwa yanzu ba zeenat ma bana iya daukar nauyin ta agun jidda take ki taimake ni fa,iza kinji kawata
Hmmm Salma kenan ko Meye dalilin ki wanifa yana neman haihuwar nan bai samu ba ke kuma kunsamu wani ko auren baiyi ba duk hanyar da ya bi amma ke kin samu har kike cewa bake,so to Meye laifin mijin ki ko dai wani abun yayi Miki ne kike son hukunta shi ta ɓangaren nan nifa har yanzu shiru ban haihuba kuma babu ma,alamar hakan .
Kece kika so hakan
"Me yasa kika bawa jidda zeenat duk wani kulawar ta yana gunta yar aiki fa munguwa ce kuma wallahi ki kula zata kaikine ta baro ki basu da amana ko kaɗan .
Banda Jidda in Sha Allah
Nifa ko yar aiki banida ita komai nine nakeyiwa kaina kuma har in fito aiki wallahi wataran har abincin da mijina zaici nakeyi in gama komai .
Kekikaga zaki, iya amma nikam gaskiya .
Bari na dubo Miki wani magani da zakiyi amfani da shi tunda baiyi kwari ba zai zube karki da mu jirani ina zuwa babu dadewa ta dawo dauke da maganin ta mika mata gashi in kinje gida ki sha "a'a bani ruwa in sha kawai tun yanzu sai in wuce gida ruwan ta miƙa mata tace ta shiga toilet ta cusa dayan haka kuwa a kayi .
Sallama sukayi ta wuce daki ta nufa ta kwanta ta fara bacci ko zeenat bata tambaya ba ta kwanta karfe ɗaya ciwon ciki ya tasar da ita tana ta birgima gashi tayi alƙawari a kanta ba zata je bangaren Ammar ba koda zata mutu ciwo maranta yake tayi cen tafara jin saukar wani abu dubawa tayi jinine ya fara sauka .
Har ƙarfe goma na dare bata fito ba zeenat ne ta nufi dakin "mommy zanci abinci ki tashi ki zuba mun "ubanki yau nine nake zuba Miki abincin ina jidda take .
Momy ba ta nan taje siyo kati tun dazu ,kije ki zuba tashi "tsayi na bazai kaiba ta daura a sama me yafitar da ita wajen karfe goma kije gun Affin ki ki gaya mishi kinji .
Yayi bacci fa
Ki tasheshi zai tashi ko kibari ta dawo ta zuba Miki
Dakin Affin ta tayi tace yazo ya zuba mata abinci yace to ko musu baiyi ba ya zuba mata abinci ta zauna taci abincin ya bata ruwa yace ta kwanta a dakin sa tace to daɗi take ji sosai da farin ciki .
Lokacin da Jidda ta dawo bata ganta ba dakin Salma ta nufa ta tambaye ta tace tana gun Affin ta sai da zuciyar ta ya tsinke nan kuwa zeenat baccin ta take yi cikin kwanciyar hankali amma tana razana sai ta dinga kiran sunan jidda .
Shikuwa ya dauka shaƙuwa ce irin tasu wani kalma da ta dinga faɗa .
*Anty Jidda ina brush din na duba wanda kike mun amfani da shi ban gani ba ki dauko kiyi mun dashi yafi daɗi*
Yadinga nanata wa har gari ya fara yin haske sallah ya tafi ya dawo ya kwanta yayi mata addu,a shima yayi bacci amma ina baccin idon shi a rufe amma baya koda jin halamar bacci ya dinga tunanin ko dai brush ɗinta ne da zafi ƙarfe takwas ya tashi ya siyo brush sabbi guda hudu .
"Jidda ga wannan a zubar da wancen brush din tace in kinayi mata aiki da shi yanayin zafi gara wai wani yafi daɗi to kincenza mata kinji
Take cikin jidda ya ɗura ruwa har wani gumi takeyi jikin ta sai rawa ya keyi .
Lafiya kuwa Jidda me ya faru naga sai rawa jikin ki ya keyi.
Malam Sabo
Asabe ne ta shiga gun malam Sabo ko sallama babu ganin ta yayi a kan shi ranta duk a ɓace "Asabe lafiyar ki kuwa naga a lamar da muwa a ranki sannan ai ba girkin ki bane balle kice zan san da zuwan ki me ya kawo ki ne ki sanar da ni
Ikon Allah
Shikenan kenan sai ranan girki na zan ganka wannan dukar da ka gindaya babu wanda zaibi bzan ƙara zuwa dakin ka ba daga yau kuma wallahi kama janye ranan da zan yi maka girki dan babu shi da ga yau zanje in taho da yarona in yaso ka hada mu ka kore mu ga wanda zaka kora daga gidan ka amma kake koron yaro da munafiki Gara ɓarawa haka da mazinaci kuwa gara dai ɓarawon."mekuma ya kawo zancen nan in dai yaro ne ki dawo da shi amma batun kice mu rabu kam batama taso ba .
Sai da kabari yaro ya lalace gidan karuwai ya ke bi shine mai aiken su ,siyo musu sigari kafin ina Khalisat da Abida har da zuwaira da auren ka take cin amanan ka take holewar ta da maza amma sune basa laifi agun ka wallahi na bar musu kai suje su hada har da kwana na
Ficewa tayi daga ɗakin da ido ya bita
Asabe ubanwa yace ki shiga gun malam tunda ba girkin ki bane kwartuwa kawai da bata ramin kanta " banza Zuwaira tunda halin kine bun maza har da na sauran mutane ba dole kice haka ba a sauran matan wallahi duk abun da kukayi ina da video shi wallahi a sirin kune zai tounu a gun mutane susan ko ku waye .
A'a asabe karfa kice zakiyi wa umma ta rashin kunya wallahi dan zanyi maganin ki wallahi "ai kuwa abida ba zakiyi albarka ba tunda rashin kunya ne aikin ki sai duniya tasan me kukeyi wallahi .
Shigewar ta ɗaki tayi ta barsu mayafi ta dauka ta fice daga gidan gidan Usman ta wuce tayi sa,a kuwa yana nan daman ita yake jira abun hawa suka hau sai gidan Hajiya Lawisa shiga cikin gidan sukayi Yusuf yana kwance a wani ɗaki bayan sun gaisa ne tare da yi mata bayani komai ta kaisu dakin da yake
Daman kece uwarshi munan bama koran yaro in har yazo dole a barshi yayi duk abun da ya ke so muma ba musan waye zai kula mana da namu da muka baro a gidan wasu ba Yusuf kuwa yana da kyau ga hankali babu ruwanshi in har dai zaici abinci ya ƙoshi ba shida matsala kuma bai taɓa daukar kuɗi na ba ko kadan wallahi Allah dai yayi mishi albarka yarane fa sai a hankali in bakwa so ku bani ni ina son kayana .
Nagode baiwar Allah Allah ya saka har yayi jiki kuwa yayi haske kayan shi Allah ya tsare ya kuma kiyaye na gaba Allah ya rufa asiri idan da ranka zaka sha kallo a kalli naka, kaima
Daukar Yusuf sukayi gida suka wuce da shi suna shiga yara suka dinga ga ɓarawo Yusuf ya dawo zuwaira ne ta fito kuce muyi hankali in ba haka ba bera ya dawo yanzu zamu fara boye boyen kuɗin mu Allah ya rufa asiri .
A ɗakin Asabe yake ganin jikin nashi babu ƙarfi Usman ya kira masu gyara suka gyara in da ya ɗan baci har sabon kujeru ya canza mata ya kuma bata hakuri yace ta bari in ya gama ginin da yake yi zaizo ya ɗauketa su koma gidan da yake gina mata ta ƙara hakuri sallama yayi musu ya bata kuɗi yana kuka ya fita in ya tuna malam Sabo ne mahaifin shi sai takaici ya kamashi sosai irin zagin sa da akeyi a kan mungun halin mahaifin shi .
Wani ne yayi wa Khalisat duka kuma ya kawo ta har ƙofar gida ya ajiye ta da gudu ya ra suka shiga gun kaltume suka sanar mata a guje ta fito ganin halin da take ciki ne yasa ta sure ta sai ga malam Sabo
Ajiye ta tashi dan ubanki ki taka da kafarki shegiya kawai.
AZURFA
STORY AND WRITING BY AMINA MA'AJI MAMAN KHAIRAT
Ina jama,a albishir dan Allah kuce mun goro ku zauna kufara bibiyan littafin Azurfa wanda ya kunshi abubuwa masu tarin yawa .
In kin San ba comments zakiyi ba dan Allah karma ki siyi littafin nan ki zauna ko na Allah ya,isa a kawo Miki labarin Azurfa ya faru da gaske in labarin yayi dai dai da rayuwar wasu ina neman afuwan ku .
Kai tsaye zaki tura kudin karanta littafin Azurfa a wannan asusun 8068748984 Amina ma'aji opay sai shedar biya ta wannan nunber 08068748984 kafin in gama Free page 300 in nagama 500 mutane uku zasu iya biyan kuɗi su biya 700 sai na jiku .
Marubuciyar
Aminatu
Halacci ne
Zaɓi biyu
Yancin mata
Halin maza
Gidan marayu
Wata mahangar
Damai rai ake rikichin duniya
Hangen nesa
Ɗan Adam butulu.
Azurfa.
Albishir gareku yan group ɗin Azurfa an yi muku ragi zaki biya dari uku gaba da yan ku in kuna da ra,ayin ƙaran ta Azurfa wallahi bazaku taɓa dana sanin karanta littafin Azurfa ba sai najiku a nan na kawo karshen free page sai najiku a paid group.
Ƙarshen free page
LAMBA NA GOMA SHA BIYU
________Tashi Khalisat mu shiga gida kaltume in kin ƙara riƙe yarinyan nan zan baki mamaki bake ganin ta kamar ma ,abuge take ne,wannan da yazo ya ajiye ki kamar kayan wanki dan ubanki wato kwarton ki ko shine ya ajiye ki ?
Baba taimako na fa yayi ina tafiya jiri ne ya ɗebe ni banci abinci ba shine nayi mishi kwatancen gidan mu ya kawo ni kaji amma babu komai "wallahi duk lokacin da kuka ɗebo masifa ya ƙare muku kuda iyayen ku yan iska kawai ki wuce kisha magani kaltume zo ki karɓa mata magani in kuma ya kama na zuwa asibiti kuje da kuɗin ku amma banda nawa na gaya muku kubace mun daga nan banzaye masu jawomun magana.
tun safe zuwaira ta gama duk wani aikin da zatayi yau ne a ke kawo mata sabbin kujeru gidan ta tun safe ta fita a na ta aiki gida yayi kyau ya sha gyara da taimakon Alhaji Jafar ko mai ya bun ƙasa unguwa ce ta masu kuɗi wanda babu ruwan kowa da kowa kowa ta kanshi yake yi Abida da Adnan suka zo duba gida sun yaba da irin wannan tsarin gidan akwai ɗakuna da yawa a cikin gidan sai yamma suka tafi a babban hotel suka yada zango zuwaira ita ma da Alhaji Jafar suma hotel din suka nufa tare da siyan komai duk wanda zasu buƙata dan zuwaira tace a malam Sabo biki a keyi kuma sai dare zata koma suke more wa ya hanata kula kowa duk abun da take so zai,yi mata .
"Hajiya ta wallahi babu wanda na tsana fiye da mijin ki yanzu ki ƙaurace mishi kawai bana son ya taɓaki nima kuma Kinga bawai sanin shi nayi ba amma daga jin sunan shi ,yana cutar da kene kawai taya kamar ki mutum zai,ajiye ki ace yana bin wata kuma kinsan nida A'isha bamu dace ba ga siranta ga dai kawai tana amsa sunan ta ne a matsayin Matana kana kwanciya da mace ƙashin ta yana sukan ka ki yadda muyi aure kawai in daukeki mubar garin gaba daya in ba auran ki nayi ba gaskiya banida nutsuwa ko kadan .
Kwantar da hankalin ka ina so komai ya kammala wanda koda mun rabu ina da in da zan zauna kafin in gama idda dan nasan iyayena bazasu barni in zauna dasu ba karka da mu.
Marmarin ki yau nakeyi kije ki watsa ruwa kawai watsa ruwa tayi da tawul ajikin ta suka kwanta wajen aikata abin da bai dace ba ko kadan Allah ka tsare mana zuri,a soyayya suke gudanar wa mai cike da rashin imani a hotel din Abida take Khalisat da Bashir malam Sabo da wata mace a babba wanda ta amsa sunan ta mace yar gaye wanda yake da Hajiya Balaraba me zai yi da su Asabe kuwa dakunan da suke ciki duk makwabtan juna ne malam Sabo shine a daki mai lamba na biyar Zuwaira na shida Abida na goma Khalisat na sha ɗaya kowa holewar shi yake yi .
Abida
Gaskiya Adnan so nake ka cenza mun waya in ba haka ba in nemi wanda zai cenza mun haba nafi sati biyu ina abu daya daɗi na da kai ƙanƙamo in ba haka ba murabu amma kanacewa wai aure zamuyi a hakan ,kake Sona dame ma zaka riƙeni .
Kedai bari kawai akwai kuɗin da nake so in Sha Allah komai zaizo da sauki da yardar Allah ki kwanta ki huta kayan ki nima baccin zanyi yana