Showing 45001 words to 48000 words out of 78516 words

Chapter 16 - FEERYAL Part 1 Complete Hausa Novels by Rasheeda S Director.doc

kizo, ko nazo nayi miki."
kafad'a ta make
"A'a ni zanyi Ammie Miemie tana min dari ta ce wai har yanzu ana min wanka."
"To in banda Miemie ai itace gaba da ke, in ita ta iya ke da sauran ki."
"Ni dai Ammie na iya nima."
"To je jiyi yanzu anjima da daddare da kaina zan miki."
ta juya da sassarfa tayi ta fice a kichin d'in..




Hajiya ce kwance a kan makeken gadon ta tana sharara bacci sai gwarti take saukewa.
daga cikin bacci taji ana kiran sunan ta, ana jajjan kafafunta.
A firgice ta mike tana fad'in
"Wayyooo ni Hanne nayi mugun ji, waye waye anan, Bishira wane ne?."
ta lalub'o makunni wuta dake d'aure a kan bedside ta kunna.
d'akin ya bada haske ba mai yawa ba.
can kuma hasken ya soma karuwa da kansa, yayi wani irin bau ya haske d'akin gaba d'aya lokaci guda.
a take kuma d'akin yasoma amsakuwar magana had'e da tafi tamkar ana gad'a cikin d'akin.
ga wasu irin maganganu barkatai wannan nayi wancan nayi fad'i a ke

"Hajiyaaaa taso muyi gad'a, taso ke ce da shiga fili yanzuuu."
Hajiya da fitsari ke kokarin kwace mata sabar azabebben tsoro tashiga fad'in
"To to laaaha'ilaaaha'illallahu, wasayyahu wasayyahu wasayyahuuu, li'eelafiiiikuraishin,
dan girman Allah kuyihakuri wlh lalurar ido gare ni, ga kwab'ewar gwuiwa, ta ina zan fara,
kuyi min rai."

"Bafa zamu kyale ki ba ke ce da shiga fili taso ki fad'o mu cab'e."
Hajiya ta kwalala uban ihu
"Wayyo Allah jama'a ku kawo min d'auki yaukam nayi gamo,
dan Allah dan ma'aiki Rasulullahi nagama ku da Allah kui hakuri ku kyale ni,
ta ina zan fad'o bana ganin ku, tun zamanin yaranta rabon da nayi gad'a,
wlh babu kafar yin gad'a kuyi hakuri kuje gurin masu kafa."
"Dole ki taso Hajiyaaa ko mu d'aga ki, kuyi sama da ke."

Ba sai ga Hajiya ta mike da kafafunta ba, dama tun sati biyu aka ce ta gwada takawa ta ki ta ce wai da saura tukun guiwar bata gam???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a had'ewa ba.
"Ku taro ta zata gudu."
tuni Hajiya ta saki fitsari, jiki na kakkarwa ta nufi kofa fitsari na zuba,
kafin ta isa kofar ta bud'e tazo daf zata fice kofar yakuma kullewa garamm.
Hajiya tayi dakuwan 'yan bori a kasa, daram da d'uwawu.
ta rufe idanunta gam tana fad'in.

"Yasin kafa dubu, li'eelafi kafa bakwai, lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya,
yasin me manjagara yakwasheku ya zubdaku can kuyi nesa ku tsaya a can, wasayyahuuu wasayyahuuu ku tsaya a can laaaa'ilaaaha'illahu,
aniya bi aniya aniya bi aniya, fatiha da salatin annabi."

Ji kake kuuu cikin Hajiya na bada sauti, tsoro iya tsoro firgici iya firgici a tare da Hajiya.
sai ihu da kwalala take kamar makogoron ta zai fita.

A tare Hajiya Bishira da Kulu suka fito daga d'akunan su, suna rige-rigen shi ga d'akin Hajiya.
a bakin kofa suka ganta tayi zaman dirshem tana kwarara ihu.
duk sukayi kanta suna had'a baki wajen fad'in
"Lafiya Hajiya me yafaru, ciwon kafar ce ta motsa? subhanalillahi!."

Jin moryoyin Hajiya Bishira da kulu yasa Hajiya bud'e idanunta.
ta kankame kafafunsu kad'an yarage ta zubar da su kasa.
Hajiya Bishira ta kara hasken d'akin ta hanyar kunna makunnin koyayen wutan da sukayi wa tsakiyar p.o.p d'akin kawanya,
tamkar kwalliya ta sama.
d'akin yabada haske sosai tamkar tsakiyar rana.

Hajiya tashiga binsu da kallo da alama dai yanzu ne ta dawo cikin hayyacin ta.
Hajiya ki sake mu kar ki yardamu a kanki."
cewar Bishira tana janye kafafun ta daga rukon da tayi musu.
cikin sauke numfashi'n tsoro irin wanda mutum ya kub'uta daga azaba Hajiya ta ce

"Nayi gamo gamo nayi da bakaken aljanu, ku kaini bayan gida ciki na ya rud'e."
"Hajiya wa ya kawo ki nan to ke da ba tafiya kike ba?."
cewar Kulu tana rike hab'a.
"Ban san ya akayi nazo nan ba ina ga su suka kawo ni, ke da'alla kamani ku kaini masai ko sai nayi anan nabar muku aiki."

Suka tallafe ta ta mike Hajiya ta d'aga kafa tana d'ingisawa.
"Hajiya kin warke ashe."
Kulu ta fad'a tana bin kafarta da kallo sai kuma ta waro ido
"Me zan gani Hajiya fitsari kamar kikayi a zaune."
"Har uwar fitsari ma zanyi a nan in ya kama,
da'alla ku kaini bayi na matsu."
Hajiya Bishira ta bi gurin da kallo tambas fitsari ne tun daga bakin gado har zuwa inda suka same ta zaune.

Suna kaita bayi ta sunkuya gudawa daya murd'e ta, zasu fita su bata guri, ta ce babu wan da ya isa ya fita su jirata sai ta gama.

Suna fito da ita takuma cewa su koma tana jin wani.
sai da ta shiga bayi sau biyar a kai a kai.

Tana zaune a bakin gado tana sauke numfashi, su Hajiya Bishira da suka gama tsaftace cikin d'akin da sarkake shi,
suka dawo inda take suna yi mata sannu.

Kulu ta dube ta tana fad'in
"Sannu Hajiya dare d'aya har kin zabge, wai ya akayi mu bamuga bakaken aljanun ba sai ke, ta ina suka shigo ne, ko dai mafarki kika yi,
anya ba mayu ke bibiyar ki ba kuwa?."

"Uhum ke dai bari Kulu ko ta sama ko ta kasa sai Allah, ina bacci narika jin ana kira na, da na amsa kiran da sun tafi da ni, kin san ba'a amsa kiran dare kana amsawa to ka tafi ke nan,
yazama dole a sawa gidan nan kafi, tun ba yau ba nake fad'awa Abubakar ya sa kafi a gidan nan sabo da miyagu yaki ji, to ba ga irin ta ba da babu wani mugun da zai iya shigowa gidan nan, kota sama ko ta kasa ko a b'oye ko a bayyane,
badun nayi ta addu'a ina ja musu yasin ina sauke wa ba da sun tafi da ni."

D'ip Hajiya tayi jin motsi karkashin gado ta kankame su Kulu ta na fad'in
"Yasin kafa dubu li'eelafi kafa bakwai lakadija'akum kafa d'ari ba d'aya fatiha da salatin annabi wasayyahuuuu."
Hajiyq Bishira ta ce
"Hajiya bafa komai kinga ni kyanwarki ce gata can fa, magen ki ce a kasan gado taga haske ta fito."
"Kin tabbata mage ce."
Hajiya ta fad'a tana zazzare ido.
"Itace ba gata nan ba ta fito, watakila ma ita ce ta razane ki d'azu."
"Um-um ba ita ba ce magana naji bilhakki, kyanwa tana maga ne."
"Hajiya in zaki kwanta kirika addu'a, babu abin da zai same ki insha'allahu."
"Ai ni yau naga karfin addu'a baki ji yanzu ma nayi ba, ai addu'a tana da amfani yana kora miyagu."
"Ai Hajiya wannan da kikayi yanzu ba addu'a ba ce, ki karanta shi a karance ba ki fad'a irin yadda kika fad'i yanzu ba,
ayatul'kursiyu da suratul iklas da falaki da nasi, a duk sanda zaki kwanta ki karantasu sun'ishe ki komai da komai,
zasu karake daga sharrin komai."

Hajiya ta mara baki tana fad'in
"Ahaf wannan addu'ar da kike gani tun muna yawo da jajayen sawu muke ganin amfanin sa, duk shi mukeyi da kawayen mu, muyi fad'a da uban kowa mu kwana lafiya, ai ko munga amfanin sa."
Hajiya Bishira ta girgiza kai tana fad'in
"Allah shi kyauta."

Sun so tafiya d'akunan su Hajiya ta ce sai dai fa su zauna su waye gari anan tun da gari yakusa waye wa.

Washegari Hajiya ta d'agawa Daddy hankali a waya wai sai dai yadawo yanimo kafi a sa a gidan, miyagu nason ganin bayan su.
ya ce mata to yakusa dawowa.


Shirye-shiryen bikin Farida nadad'a matsowa.
uwar amarya Mommy ba zama.
anata kai kawo yadda biki zai gudana baza aji kunyar kawaye ba.

Mommy ce zaune a parlour tana waya da Hajiya'n Dubai wata kanwar su Daddy ce, wacce take da zama a can kasar Dubai.
takan zo Nigeria jifa-jifa dan mijinta yana nan Nigeria ita kuma tana can Dubai da 'ya'yan ta,
zaman ta yafi yawa a can.
Mommy dake rike da d'aya wayarta tana dudduba wasu arnan kayan d'aki da Hajiya'n Dubai ta turo mata,
ta gyara rukon wayar dake kare a kunnen ta tana cewa.
"Gaskiya Hajiya'n Dubai wad'annan set ukun duk sun min, duka za'a bada kud'in su a sako a jirgi a kawo."
daga cikin wayar Hajiya'n Dubai ta ce
"Wai dama Hajiya Halima ba wucewa da su can UK d'in za'ayi ba, Nigeria za'a kawo su?."
"Eh Nigeria za'a kawo su a zuba mata su a gidan ta dake nan, idan sun shigo kasar yazamana da suna da masaukin su mai kyau, a can UK kuma ai shi angon ma yagama shirya gidan sa da ke can yazuba komai babu abinda za'a tafi dashi daga nan,
idan kunje abinda kuka ga babu sai kuyi odan sa acan d'in kawai."
"Ah yayi hajiyar mu, ai harka ta jin kunya baiyi ba,ai ni sam bana son harkar karanta,
me za'ayi da jin kunya kana cikin kawaye karika kunyata, idan fa kikaga gidan da za'a zuba kayan nan ba wani na arziki bane, ba nagani a fad'a bane ,
kawai a basu gida, kada mushiga kunyar kawaye, ace kamar mu aga gidan 'yar mu bai taka kara ya karya ba,
d'iya ga Alhaji Abubakar Fiya guda ace gidan ta zubin na talakawa, haba ina bazamuji wannan kunyar ba, kawaye suzo daga nesa suna yi mana kallon kasa-kasa, kallon raini,
kai ina da wuri ma zan shigo Nigeria naje na duba gidan da kaina,
idan beyi ba gaskiya za'a basu gidan da za'a zuba kayan nan,
dan wlh ban yarda da harka ta jin kunya ba."

Mommy ta sheke da dariya tana fad'in
"Hajiyar Dubai tamu, ai duk in da za'ayi bazan bari aji kunya ba, ko kin mance wane ne mijin Farida ne, Faruoq-Al'Hussain ne fa, kin san naira kuka take a family'n Al'Hussain,
da kanta Farida ta zab'i gidan da take so a cikin gidajen da mahaifinsa, Al-Hussain ya ce ya zab'i wanda za'a d'auko masa amaryarsa a saka ta ciki kafin bayan biki da kwana biyu su bar kasar."
"Yauwa yanzu naji zance ai ni na ma mance da ko d'an gidan wa d'iyar tawa zata aura, ah gaskiya mun baiwa jin kunya baya, Faruoq-Al'Hussain kai ka dace da d'iya ta."
suka sheke da dariya.

A b'angaren amarya Farida ma fa ba zama, duk da ba a kasar nan zasu zauna da mijin nata ba,
a can UK in da yake aiki zasuyi zaman shekaru goma kafin su dawo Nigeria,
sabo da aikin sa da yake yi a can shekaru goma zaiyi ya gama ya dawo gida Nigeria.
ana ta shiga da fita.

Sai ana biki saura sati Daddy ya dawo.
aiko Hajiya ta dira a kansa ko huta gajiya baiyi ba, ta ce ya d'auki Feeryal ya mai da ita tun da ya dawon.
sai da ya yi ta lallab'a ta ya ce tayi hakuri a gama biki tukun zai mai da ita.
da kyar ta yadda.

Tuni gidan Alhaji Abubakar Fiya ya d'auki manya manyan baki na kusa da ma na kasashen ketare.
ciki kuwa harda Hajiya'n Dubai da iyalenta,
da kuma kayan d'akin da Mommy tasa akayi odan sa daga Dubai.

Tun ana saura kwana uku biki aka fara gudanar da shagulgulan biki,
a manya manyan Hall.

Amarya Farida ta amsa sunanta amarya dan kuwa dubbannin d'arurruwan mutane ne suka shaida d'aurin auren, Farida Abubakar Shitu Fiya da angonta Faruoq-Al'Hussain.

Bayan d'aura aure jama'a suka soma taruwa a Hall na musamman dake a cikin gidan ta can baya,
wan da aka tanade shi sabo da tarurruka, na cikin gida idan ya taso.
nan aka tanada domin gudanar da walima bayan d'aurin aure.

Aunty ce ke saukowa daga saman bene ta cab'a kwalli had'i da gwala-gwalai, tayi matukar kyau ta dawo yarinya d'anyiwa sharaf tammar ita ce amaryar,
sai baza kamshi take.
Aunty Hindu d'iyar baffan su Daddy ta saka gud'a tana fad'in
"Kaga Amarya a gidan Alhaji Abubakar Fiya, wlh babu wan da zai ganki ya ce shekarun ki goma da yin aure,
tamkar kece amaryar ai dole ki rika rikita yayan namu, tsaruwa iya tsaruwa."
dariya ta bisu da shi ganin yadda duk parlour'n suka rud'e da zu-zu-ta-ta.
Aunty Hindu ta d'aga wayarta tana cewa
"Tsaya dan Allah na d'auke ki na turawa Yaya nasan tukuicina na daban ne yau."
"A'a huta abin ki ai gani a zahiri yafi gani a hoto, yanzun nan ma gurin sa na dosa."

Duk suka sheke da dariya har suna tafawa.
"Da gaskiyar ki wlh je ki gwada masa ya gani a zahiri wannan irin wanka, ba shigar bane sukayi miki kyau ke ce kikayi wa shigar kyau."
ita dai dariya tayi musu tayi waje...........!






Mommyn Twins ce


??/\??/\ *FEERYAL* ??/\??/\


*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*


( _Book 1_)


*~Free page~*



*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*

*____________________________________*

*???[???VAINUWA ???VRITER'SA??]Fq??*
*???VSSOCIATION??B惙?_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*???a???_

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*____________________________________*



Bismillahirrahmanurrahim





??T???14





Side d'in Daddy ta nufa ta kofar baya, dan tasan ta ainahin kofar kam cike yake tam da mutane.
ai ko hakan take har cikin babban parlour'n sa ba'i ne maza ciki a ciki.

D'akin kwanan sa direct ta wuce, tana shiga ta kirasa a waya.
ganin mai kiran nasa yasashi mike acikin jama'a ya nufi bedroom d'in sa, domin amsa kiran.
ya tura kofar yana kokarin kuma maida kiran dan ya yanke,
sai ganin ta ya yi tsaye cikin d'akin.
ido ya bud'e da kyau ya kura mata su, itako murmushi take sakar masa.
a hankali ya tako ya iso in da take.
hannu ta mika ta sakalo wuyan sa, tana cigaba da aika masa murmushi.
cikin sanyin muryar ta mai kara masa kaunar ta.
ta ce
"Daddy tun d'azu nake son ganin ka mutane sun min fin karfi."
ta karasa maganar da kashe masa ido.
wani numfashi ya sauke, sai kawai ya rungume ta ya na fad'in
"Godiya ya tabbata ga Ubangijin daya mallakamin wannan kyakkyawar tsuffar."
ya d'ago ya manna mata kiss a goshi.
d'an zame jikin ta tayi tana fad'in
"Daddy ka fara tsufa fa."
"Ina da ke ai ita ma tsufar bata isa ta dumfaro ni ba, sai dai ta tsaya a iya shekaru."
dariya ta yi ta ce
"Yau fa ka aurar da 'ya tsufa ya dad'a bayyana ga furfuran ka sun karu."
ta karashe maganar da muryar dariya.
kumatun ta yaja ya ce
"To kar ki bari tsufar tai mana tasiri, ki san yadda zakiyi ki yake sa tun kafin a fara kiran mijin ki da tsoho, shi ke nan ke ma kin tsufa."
dariya duk sukayi wa junan su.

Ya matsa can jikin bedside drower ya danna ma dannin bud'e sa, gilashin jiki ya zuge, yad'auko d'aya daga cikin makullan motocin da suke ciki.
ya zo ya mika mata.
ta karb'a tana bin key'n da ido sannan ta ce
"Na mene ne wannan?."
ya ce "Naki ne tukuicin wannan kwalliyar."
wani lallausar murmushi ta sake ta rungume shi tana fad'in
"Godiya marar adadi, naji dad'i dad'in da bazai fad'u ba."
murmushi ya bita dashi, yana matukar jin dad'i ya yi mata kyauta yaga tana nuna yabawa da jin dad'in kyautar da ya yi mata.
yana daga cikin abin da yake dad'a kara girman fadarta a cikin birnin zuciyarsa.

Bata jin kanta ita wata ce dan mahaifinta yana da dukiya, ko min kankancin kyauta takan nuna jin dad'in ta mara misaltuwa.
akasin sauran matansa da iyayensu ba koman komai ba sai fad'in ran tsiya.


Da sauri Miemie ta shige side d'in Aunty, ta haura sama da sauri tashige d'akin Feeryal.
tana zaune sunata wasa da kawayen ta, wan da ita take ganin su.
Miemie ta ce
"Feeryal taso muje ayi mana kwalliya ga mai kwalli tana kan yi wa su Ameerah, a side d'in Hajiya,
muje gurin walima ke bazaki je bane?."
"Ni bazan je ba Ammie na ta ce nazauna nayi wasa na a nan kije kawai abinki."
"Dan Allah taso muje gasu Umaima'n Dubai ma sun zo zo muje ki gansu."
ta janyo hannunta suka fita.
tun kafin su karasa sauka daga stairs hankalin 'yan cikin parlour'n ya dawo kansu.
wad'an da dama sunsan Feeryal d'in tun tana jaririya,
suna ta mamakin girman ta da yanayin tsarin zubin halittarta.
wad'an da kuma basu santa ba suna binta da kallon rashin sani, kallon itama daga cikin ba'in da suka zo daga kasashen turai suke mata.

Har sun zo shiga parlour'n Hajiya,
Feeryal tayi baya da sauri a matukar tsorace.
Miemie ta ce
"Hajiya bazata miki komai ba zo muje, kar a gamawa Ameerah a kama yi ma wani."
hannu Feeryal ta d'aga baki na rawa ta ce
"Ga mage can ni dai bazan je ba."
"Baya komai fa ki zo mu shiga."
"A'a ni bazan shiga ba!."
tayi maganar tana ja da baya a mugun tsorace, tamkar zata shid'e.

"Ke Miemie me kike yi a nan ana can anayi wa su Ameerah kwalliya ke kina nan, gashi har an watse an tafi gurin walima, kiyi maza kije a yi miki."
cewar Hajiya data fito zata gurin walimar tana gyara zaman mayafin ta.
ido ta gwalalo kan Feeryal dake ja da baya da baya.
"Me zan gani haka me ya kawo wannan aljanar nan?
ke Miemie kifita idona na rufe, ban rabaki da wancan yarinyar mai kamata faran mayu ba,
kin d'auko ta zaki kaita cikin jikoki na ta lashe su da maita ko ta shige jikinsu,
kar ki sake ki shiga min b'angare mayyar banza mayyar hofi ko na had'a ki da karnuka su yayyaga min namarki anan."

Ai da gudu Feeryal ta juya tayi waje.


Uwar amarya Mommy ta fito da ka kawayen ta zasu gurin walima, ta cab'a kwalliya cikin wani arnen lashi mai tsadar gaske tasha d'inkin manyan mata,
matan masu nera.
Umma Karima ita ma da nata kawayen kusan shiga iri d'aya sukayi da Mommy sai dai kalar leshin ta daban ne amma mai tsadar ce ita ma.

Motar Hajiya Luba ne ya kunno kansa cikin gidan.
bayan ta nunawa security pas d'in gayyatar ta,
suka bud'e mata get ta shigo.
Mommy suka tsaya suna zaman jiranta su karaso dan ta gane motar ta.
a babban parking lot d'in gidan in da motoci ke cike tam nagidan dana jama'ar da suka sami halarta bikin ke tare.
direban ta ya dai-dai parking.
Hajiya Luba suka fito ita da wata budurwar yarinya.
suka karasa in da su Mommy ke tsaye.
suka rungumi juna da Mommy,
Hajiya Luba ta saki Mommy tana fad'in
"Kaga uwar gida a gidan Alhaji Abubakar Fiya, Allah dai yasa bamu makara a walimar ba."
"Kun dai kusan makara dan har an fara, na ce gajiyar jiya ce ta hanaki isowa da wuri, to ya gajiyar jiyan."
"Wlh ke kam dai ingaya miki bawai gajiya bace ta zaunar da ni, d'iyarki ce gata nan Kuraiba ta b'ata min lokaci, kin san shirin 'yammata sai a hankali, a fenta nan a fenta can,
ke Kuraiba ga Mommyn ku nan ki gaida surukan ki."

Budurwar da aka kira da Kuraiba ta ce
Ina yini."
ta fad'a a takaice.
Mommy tayi murmushi tana amsawa da
"Lafiya lau Kuraiba ya school."
ta ce "Alhmdulillah."
"Kuraiba fa an girma nakai 1y rabon da na ganta,
har tafi Farida a tsaye."
cewar Mommy, tana dubanta da murmushi.
Hajiya Luba ta ce
"Ni da nayi zaton ma lokaci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login